Sashe 53
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baice mata uffan ba harta diba abincin zata wuce yace
"Zo nan" dan hade rai tayi kafin ta juyo ta maida fuskarta dai dai,saita qaraso,ya dubeta
"Zauna nan kici....daga yau duk sanda kika sake rufe kanki a daki....zan balle qofar na shiga,kuma abinda xai biyo baya bazai miki dadi ba,don banga abinda xaisa ki ringa kulle kanki ba anan" narke fuska tayi,yunwa takeji sosai,kuma bata jin xata iya cin abinci a gabansa,kamar ya karanceta sama taka taji yace
"Eheeennn....idan xaki ci abinci kici,kaman bake muke bawa abincin ba a baki muna share miki majina a hanci" da sauri ta daga kai ta dubeshi,sai suka hada idanu,ta sake kautarwa da sauri saboda yadda ta kafeta da idanunsa dake mata kaifi da yawa,kai ya gyada mata alamun tabbatarwa
"Yesss.....ba zaki iya tunawa ba,saboda a sannan kinyi qanqanta da yawa.....kukan kitso...kukan wanka duk kin iya,da kika girma kuma sai kika zama mai tsiwa da taurin kai....right?" Ya qarashe da tambayarta,sosai maganar ta mata nauyi ta kuma bata kunya,zata iya tuna wani abun,amma wani abun ba zata iya tunawa ba,hakanan taji tana son sake jin wani abu daga bakinsa,mutum ce dakeson labarin quruciyarta,tana son a dinga gaya mata abubuwan da tayi zamanin quruciya wanda ita batasan ta yisu ba,ya karanci hakan akan fuskarta,amma bai sake cewa komai ba,saidai ta sanya cokali ta soma diban abincin a hankali tana taunawa,yayin daya lafe jikin kujera kamar mai kallo a tv,saidai ita yake satar kallo time to time.
Da magariba yayi waya aka sama masa ticket na jirgin da zai tashi daga abuja zuwa kano qarfe biyu na rana,bai shaidawa zahran ba ita kanta sai washegari daya dawo daga sallar asuba,haka nan wannan karon sai taji bata wani daukin tafiyar sosai,haka ta sake abinda yake da buqatar a shirya din,zuwa sanda ya gaya mata xasu fita ta kammala komai,ta yafa mayafinta,ta janyo akwatinta tayo falon.
A tsaye ta sameshi tsakiyar falon yana amsa waya,ya baiwa qofar da zata fito din baya,tun kafin ta qaraso ta gama qare masa kallo,sanye yake da wani trouser da shirt,sai high top takalminsa daya dace da kayan jikinsa,tun bata ga fuskarsa ba amma ta tabbatar da cewa shigar ta amsheshi,ta qara masa kwarjini.
Ta gefansa ta raba zata wuceshi,sai taji an kama hannunta dake riqe da majanyin akwatin matafiyar da take ja,waiwayowa tayi sai suka hada idanu,ya mata alama data saki,don haka ta zame hannunta daga cikin nashi a hankali,ya taka ya biyo bayanta yana ci gaba da yin wayarsa.
Dukkansu a baya suka xauna,driver ne ya jasu,wanda idan ya kaisu airport zai dawo da motar ne gida.
Ko a cikin jirgi ma babu magana tsakaninsu,saidai lokaci zuwa lokaci kowa ya kama dan uwanshi yana satar kallonsa,daga bisani ne haidar ya tanka
"Idan na sake kamaki kina satar kallona saina tsole idanun nan naki" gefe tayi da kanta,ciki ciki tace
"Da wanne idon mutum yasan ina kallonshi" baice komai ba amma taji kamar sautin fitar murmushinsa.
Suna sauka a aminu kano airport driver ya daukesu sai gida,ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a gida,tafiyar kusan minti arba'in ita ta kawosu gida,wanda tun daga harabar gidan tasan tabbas taro ake,saboda jama'a da kuma rumfunan da aka kafa,indai lissafinta yayi dai dai yaune sunan yasira kenan,harga Alla ta fidda rai data ji bai sake tada zancan ba,shi yasa ta daina lissafin ma.
Zumudi fal ranta ta saka hannu xata bude murfin motar,sai taji an dafe hannun nata,ta waiwayo da sauri idanunshi na akanta,hakanan tana iya jiyo hucin numfashinsa sosai saman fuskarta saboda yadda yake dab da ita,da wata irin kwantacciyar murya taji yace
"Ki nutsu da kyau,kada ki manta ke din wacece,banason yawo jiki a bude da sunan kina cikin gida....ki kiyayemin mutuncin igiyata" gaba daya ita zancan nauyi ma yayi mata,saita maida kanta daya side din,daga nesa tana hango su salma suna kai kawo,da alama hidima ta dauki zafi
"Soja baya son kawo qorafi ko kawo uzuri,just be obedient to my commands" cikin ranta take mitar ance masa a bariki ake dazai soma lissafa mata wasu qa'idoji,bata gama wannan ba taji ya zame wayarta daga hannunta,yayi wasu danne danne ciki sannan ya miqa mata
"This is my number,just call me idan kina da wata matsala ko buqata,bance ki tambaya kowa komai ba,ummi ko hajja,nayi cancel duka,zaki iya tafiya" da sauri ta buda murfin motar ta fito,wanda fitowar tata yaja idanun mutane da yawa,donma aliyyun zamanshi yayi cikin mota,ya kuma nada umarnin a sake fita dashi daga gidan,batasan inda xaije badai,tadai san koda can baison hayaniya kwata kwata,indai ana wani taro a gidan bai zama,sanda bai kuma wani zama saurayi ba wuni yake cikin dakinsu ya kebe kanshi shi kadai,mama tayita faman fadan me yasa baya son shiga dangi ko ya fito su gaisa,tun tana mita da qorafi harta gaji ta qyale,tunda ta fuskanci halinsa ne hakan,
Nan da nan labarin dawowar tata ya zagaye gidan,aka fara cecekuce da zancan dawowarta,ta fara gaisawa da 'yan uwa data samu harabar gidan,suna amsawa gami da tayata murnar qarin girman da aliyyun ya samu,ta sake fuska sosai tana amsa musu cikin walwala da nuna jin dadi,da yawa suka dinga binta da kallo wanda batasan na meye ba,da haka harta isa sassan abba babba,inda canne yafi cikowar yan suna da yawa,tunda anan mahaifiyar yasiran take wato mommy.
Ihun murna 'yan uwan nata suka saka sanda sukayi arba,kowa yayo kanta,suka cika kunnuwanta da magana,kowa da abinda zaice,salma ce daga can tace
"Allah matar ya haidar ba haka muka taho muka barki ba,anya ya haidar bai cika aiki ba kuwa?" Ta qarashe fada qasa qasa,wani wawan dundu zahra takai mata,akayi sa'a kuwa ta sameta,fa gantsare saboda zafi,sauran suka sheqe da dariya,dai dai sanda mommy ta shigo
"Waiku kam bakusan kun girma ba don Allah,yanzu kalli yadda sahal yake kallonku,kin dirke masa uwa.....daga dawowarki kin biye musu,tashi ki qarasa gaisawa da jama'a ki qyale wadan nan shirmammun,kuna nan a waje ana nemanku kunata baqi"tana kaiwa nan ta fice ta barsu.
Tare suka fito da ita,ta soma lalubar mama don su gaisa,a kitchen na tsintota sunata rabon abinci da taimakon masu aikin gidan,wai yau sai ta tsinci kanta tana kunyar maman,tana kunyar hada idanu da ita,tana shirin tsugunnawa har qasa ta gaidata tace
"A'ah,tashi inna wuro kada ki bata kayanki,bakiga yadda kitchen din yake a kacame ba" saita lalubi kujera ta zauna akai saboda ji take kamar zata fadi ta gaida maman tayi mata barka
"Ki shiga wajen hajja,can ne naga da sauqin mutane" da to ta amsa mata,suka fito tare da hafsa.
Hafsan ce ta dubeta sanda suka fito ta qyalqyale da dariya
"Anya zahraty wannan kunyar nidai ban taba gani kina yiwa mama irinta ba kamar yanzu,lallai yayana ya cika aiki....to ku shirya wallahi kuda hajja,tana nan satin nan gaba daya kullum saita muku dan biki" harara ta watsawa hafsan,bata iya bata amsa ba suka qarasa sassan umminta.
Kusan a tsaitsaye suka gaisa saboda jama'a itama dake cike a sassan nata,sai kawai ta wuce sashen mutuniyar tata hajja.
A dakinta ta sameta ita kadai tana tsaye inna gaje na wanke mata bandaki,da alama wani ya shigar mata ne,haka take,duk sanda wani ya shigar mata bandaki indai baqo ne to sai an wanke mata,har mamakin tsafta irin na tsohuwar zahra keyi,wani lokaci kuma ta tsokaneta
"Waike da kika kusa gangarawa tsaftar nan duk ta meye?" Wanda idan wani ne ya gayawa hajjan haka sai inda qarfin zahran yake,takance
"Kaga tafiya lahira a kanka,hajjanmu ba yanzu ba".
Wani kallo hajjan tabi zahran dashi kafin ta yamutsa fuska sanda take gaidata
"Munafukai....sai yau kuka ga damar tahowa?,aida kun sani kun dawwama a can" ta fada da biyu,sabida ta bigi cikin zahran taji me zata ce,hade rai zahra tayi tadan ja baya
"Zaki fara daga dawowata,ni inacan kamar nayi me saboda kewarki,amma irin marabar da zakimin kenan?"
"Na miki da arziqi ma 'yar nan,ina daya ja'irin?" Baki ta turo ta haye gadon hajjan,wanda tayi kewarsa sosai
"Ki kirashi ki tambayeshi mana" ta fada tana kwanciyarta
"Toooo...da saura kenan" hajjan ta fada a ranta,don tayi tsammanin zata kareshi ne
"Muje zuwa mahaukaci yahau kura" ta kuma fada a ranta
"Duk na isheku riga da wando" ta fada tana shigewa bandaki.
Wunin ranar cikin walwala tayi abinta gaba daya cikin dangi,har zuwa dare sanda aka qare sunan,baqi suka tattafi saura 'yan gidan da yaran gidan aurarru wadanda sukayi aure,suma a cikinsu wasu sun tafi,tawagar su zahra kuwa suna tattare a sassan hajjan sunata kwasar hira,kamar ba za'a rabu ba,don yasiran a nan sassan hajjan take zaune tunda tazo haihuwa.
Tana idar da sallar isha'i zahran ta koma wajen ummin nata,suka sake gaisawa sosai sannan suka taba hira,wanda ta lura kusan fiye da rabin hirar tata kan aurenta da aliyyu ne a fakaice,tana mata jirwaye mai kamar wanka a kansa,ta rasa wanne irin qauna ce a tsakaninsu
"Nasan zakiyi mamaki me yasa na damu da zancan aliyyu a kanki ko inna wuro?....nafi kowa sanin aliyyu mijine na kerewa sa'a,irin mijin da ake cewa mijin marainiya,mijin dana jima ina miki addu'ar samu,kici gaba da gyara mu'amalarku inna wuro,zaki fuskanci abinda nake gaya miki,mazan aure irin haidar a wannan zamanin wahala sukeyi,cikin dari guda daya ne tak,Allah ne ya amshi addu'ar dana jima ina muku ya kawo sanadi da kika zama matarsa" wannan shine magana kusan ta qarshe da sukayi da maman nata,wanda da ita ta dawo zuwa sassan hajja,wanda zuwa yanzu an sake yoyewa,inna gaje ta gyara falon fes,sai fidda qamshi yakeyi.
Dakinta ta shige,saita tadda yasira ta baje abinta ita da jaririnta,sai suwaiba da itama zata kwana,sai wata 'yar uwarsu badi'a,itama ba aure ne da ita ba.
Tunda can dama ba wani shiri suke sosai da suwaiba ba,don haka da badi'a suka gaisa kawai,ta diba kayan wankanta ta shige bandakin tayi wanka,sannan ta fito ta dauki kayan da zata saka ta wuce dakin hajja donta shirya,saboda ta fuskanci kamar suwaiba ta sanyawa duk wani motsinta ido,batason ta fusata harta buda baki ta gaya mata magana,shi yasa tabar musu dakin da niyyar kwana dakin hajja.
"Zo nan" dan hade rai tayi kafin ta juyo ta maida fuskarta dai dai,saita qaraso,ya dubeta
"Zauna nan kici....daga yau duk sanda kika sake rufe kanki a daki....zan balle qofar na shiga,kuma abinda xai biyo baya bazai miki dadi ba,don banga abinda xaisa ki ringa kulle kanki ba anan" narke fuska tayi,yunwa takeji sosai,kuma bata jin xata iya cin abinci a gabansa,kamar ya karanceta sama taka taji yace
"Eheeennn....idan xaki ci abinci kici,kaman bake muke bawa abincin ba a baki muna share miki majina a hanci" da sauri ta daga kai ta dubeshi,sai suka hada idanu,ta sake kautarwa da sauri saboda yadda ta kafeta da idanunsa dake mata kaifi da yawa,kai ya gyada mata alamun tabbatarwa
"Yesss.....ba zaki iya tunawa ba,saboda a sannan kinyi qanqanta da yawa.....kukan kitso...kukan wanka duk kin iya,da kika girma kuma sai kika zama mai tsiwa da taurin kai....right?" Ya qarashe da tambayarta,sosai maganar ta mata nauyi ta kuma bata kunya,zata iya tuna wani abun,amma wani abun ba zata iya tunawa ba,hakanan taji tana son sake jin wani abu daga bakinsa,mutum ce dakeson labarin quruciyarta,tana son a dinga gaya mata abubuwan da tayi zamanin quruciya wanda ita batasan ta yisu ba,ya karanci hakan akan fuskarta,amma bai sake cewa komai ba,saidai ta sanya cokali ta soma diban abincin a hankali tana taunawa,yayin daya lafe jikin kujera kamar mai kallo a tv,saidai ita yake satar kallo time to time.
Da magariba yayi waya aka sama masa ticket na jirgin da zai tashi daga abuja zuwa kano qarfe biyu na rana,bai shaidawa zahran ba ita kanta sai washegari daya dawo daga sallar asuba,haka nan wannan karon sai taji bata wani daukin tafiyar sosai,haka ta sake abinda yake da buqatar a shirya din,zuwa sanda ya gaya mata xasu fita ta kammala komai,ta yafa mayafinta,ta janyo akwatinta tayo falon.
A tsaye ta sameshi tsakiyar falon yana amsa waya,ya baiwa qofar da zata fito din baya,tun kafin ta qaraso ta gama qare masa kallo,sanye yake da wani trouser da shirt,sai high top takalminsa daya dace da kayan jikinsa,tun bata ga fuskarsa ba amma ta tabbatar da cewa shigar ta amsheshi,ta qara masa kwarjini.
Ta gefansa ta raba zata wuceshi,sai taji an kama hannunta dake riqe da majanyin akwatin matafiyar da take ja,waiwayowa tayi sai suka hada idanu,ya mata alama data saki,don haka ta zame hannunta daga cikin nashi a hankali,ya taka ya biyo bayanta yana ci gaba da yin wayarsa.
Dukkansu a baya suka xauna,driver ne ya jasu,wanda idan ya kaisu airport zai dawo da motar ne gida.
Ko a cikin jirgi ma babu magana tsakaninsu,saidai lokaci zuwa lokaci kowa ya kama dan uwanshi yana satar kallonsa,daga bisani ne haidar ya tanka
"Idan na sake kamaki kina satar kallona saina tsole idanun nan naki" gefe tayi da kanta,ciki ciki tace
"Da wanne idon mutum yasan ina kallonshi" baice komai ba amma taji kamar sautin fitar murmushinsa.
Suna sauka a aminu kano airport driver ya daukesu sai gida,ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a gida,tafiyar kusan minti arba'in ita ta kawosu gida,wanda tun daga harabar gidan tasan tabbas taro ake,saboda jama'a da kuma rumfunan da aka kafa,indai lissafinta yayi dai dai yaune sunan yasira kenan,harga Alla ta fidda rai data ji bai sake tada zancan ba,shi yasa ta daina lissafin ma.
Zumudi fal ranta ta saka hannu xata bude murfin motar,sai taji an dafe hannun nata,ta waiwayo da sauri idanunshi na akanta,hakanan tana iya jiyo hucin numfashinsa sosai saman fuskarta saboda yadda yake dab da ita,da wata irin kwantacciyar murya taji yace
"Ki nutsu da kyau,kada ki manta ke din wacece,banason yawo jiki a bude da sunan kina cikin gida....ki kiyayemin mutuncin igiyata" gaba daya ita zancan nauyi ma yayi mata,saita maida kanta daya side din,daga nesa tana hango su salma suna kai kawo,da alama hidima ta dauki zafi
"Soja baya son kawo qorafi ko kawo uzuri,just be obedient to my commands" cikin ranta take mitar ance masa a bariki ake dazai soma lissafa mata wasu qa'idoji,bata gama wannan ba taji ya zame wayarta daga hannunta,yayi wasu danne danne ciki sannan ya miqa mata
"This is my number,just call me idan kina da wata matsala ko buqata,bance ki tambaya kowa komai ba,ummi ko hajja,nayi cancel duka,zaki iya tafiya" da sauri ta buda murfin motar ta fito,wanda fitowar tata yaja idanun mutane da yawa,donma aliyyun zamanshi yayi cikin mota,ya kuma nada umarnin a sake fita dashi daga gidan,batasan inda xaije badai,tadai san koda can baison hayaniya kwata kwata,indai ana wani taro a gidan bai zama,sanda bai kuma wani zama saurayi ba wuni yake cikin dakinsu ya kebe kanshi shi kadai,mama tayita faman fadan me yasa baya son shiga dangi ko ya fito su gaisa,tun tana mita da qorafi harta gaji ta qyale,tunda ta fuskanci halinsa ne hakan,
Nan da nan labarin dawowar tata ya zagaye gidan,aka fara cecekuce da zancan dawowarta,ta fara gaisawa da 'yan uwa data samu harabar gidan,suna amsawa gami da tayata murnar qarin girman da aliyyun ya samu,ta sake fuska sosai tana amsa musu cikin walwala da nuna jin dadi,da yawa suka dinga binta da kallo wanda batasan na meye ba,da haka harta isa sassan abba babba,inda canne yafi cikowar yan suna da yawa,tunda anan mahaifiyar yasiran take wato mommy.
Ihun murna 'yan uwan nata suka saka sanda sukayi arba,kowa yayo kanta,suka cika kunnuwanta da magana,kowa da abinda zaice,salma ce daga can tace
"Allah matar ya haidar ba haka muka taho muka barki ba,anya ya haidar bai cika aiki ba kuwa?" Ta qarashe fada qasa qasa,wani wawan dundu zahra takai mata,akayi sa'a kuwa ta sameta,fa gantsare saboda zafi,sauran suka sheqe da dariya,dai dai sanda mommy ta shigo
"Waiku kam bakusan kun girma ba don Allah,yanzu kalli yadda sahal yake kallonku,kin dirke masa uwa.....daga dawowarki kin biye musu,tashi ki qarasa gaisawa da jama'a ki qyale wadan nan shirmammun,kuna nan a waje ana nemanku kunata baqi"tana kaiwa nan ta fice ta barsu.
Tare suka fito da ita,ta soma lalubar mama don su gaisa,a kitchen na tsintota sunata rabon abinci da taimakon masu aikin gidan,wai yau sai ta tsinci kanta tana kunyar maman,tana kunyar hada idanu da ita,tana shirin tsugunnawa har qasa ta gaidata tace
"A'ah,tashi inna wuro kada ki bata kayanki,bakiga yadda kitchen din yake a kacame ba" saita lalubi kujera ta zauna akai saboda ji take kamar zata fadi ta gaida maman tayi mata barka
"Ki shiga wajen hajja,can ne naga da sauqin mutane" da to ta amsa mata,suka fito tare da hafsa.
Hafsan ce ta dubeta sanda suka fito ta qyalqyale da dariya
"Anya zahraty wannan kunyar nidai ban taba gani kina yiwa mama irinta ba kamar yanzu,lallai yayana ya cika aiki....to ku shirya wallahi kuda hajja,tana nan satin nan gaba daya kullum saita muku dan biki" harara ta watsawa hafsan,bata iya bata amsa ba suka qarasa sassan umminta.
Kusan a tsaitsaye suka gaisa saboda jama'a itama dake cike a sassan nata,sai kawai ta wuce sashen mutuniyar tata hajja.
A dakinta ta sameta ita kadai tana tsaye inna gaje na wanke mata bandaki,da alama wani ya shigar mata ne,haka take,duk sanda wani ya shigar mata bandaki indai baqo ne to sai an wanke mata,har mamakin tsafta irin na tsohuwar zahra keyi,wani lokaci kuma ta tsokaneta
"Waike da kika kusa gangarawa tsaftar nan duk ta meye?" Wanda idan wani ne ya gayawa hajjan haka sai inda qarfin zahran yake,takance
"Kaga tafiya lahira a kanka,hajjanmu ba yanzu ba".
Wani kallo hajjan tabi zahran dashi kafin ta yamutsa fuska sanda take gaidata
"Munafukai....sai yau kuka ga damar tahowa?,aida kun sani kun dawwama a can" ta fada da biyu,sabida ta bigi cikin zahran taji me zata ce,hade rai zahra tayi tadan ja baya
"Zaki fara daga dawowata,ni inacan kamar nayi me saboda kewarki,amma irin marabar da zakimin kenan?"
"Na miki da arziqi ma 'yar nan,ina daya ja'irin?" Baki ta turo ta haye gadon hajjan,wanda tayi kewarsa sosai
"Ki kirashi ki tambayeshi mana" ta fada tana kwanciyarta
"Toooo...da saura kenan" hajjan ta fada a ranta,don tayi tsammanin zata kareshi ne
"Muje zuwa mahaukaci yahau kura" ta kuma fada a ranta
"Duk na isheku riga da wando" ta fada tana shigewa bandaki.
Wunin ranar cikin walwala tayi abinta gaba daya cikin dangi,har zuwa dare sanda aka qare sunan,baqi suka tattafi saura 'yan gidan da yaran gidan aurarru wadanda sukayi aure,suma a cikinsu wasu sun tafi,tawagar su zahra kuwa suna tattare a sassan hajjan sunata kwasar hira,kamar ba za'a rabu ba,don yasiran a nan sassan hajjan take zaune tunda tazo haihuwa.
Tana idar da sallar isha'i zahran ta koma wajen ummin nata,suka sake gaisawa sosai sannan suka taba hira,wanda ta lura kusan fiye da rabin hirar tata kan aurenta da aliyyu ne a fakaice,tana mata jirwaye mai kamar wanka a kansa,ta rasa wanne irin qauna ce a tsakaninsu
"Nasan zakiyi mamaki me yasa na damu da zancan aliyyu a kanki ko inna wuro?....nafi kowa sanin aliyyu mijine na kerewa sa'a,irin mijin da ake cewa mijin marainiya,mijin dana jima ina miki addu'ar samu,kici gaba da gyara mu'amalarku inna wuro,zaki fuskanci abinda nake gaya miki,mazan aure irin haidar a wannan zamanin wahala sukeyi,cikin dari guda daya ne tak,Allah ne ya amshi addu'ar dana jima ina muku ya kawo sanadi da kika zama matarsa" wannan shine magana kusan ta qarshe da sukayi da maman nata,wanda da ita ta dawo zuwa sassan hajja,wanda zuwa yanzu an sake yoyewa,inna gaje ta gyara falon fes,sai fidda qamshi yakeyi.
Dakinta ta shige,saita tadda yasira ta baje abinta ita da jaririnta,sai suwaiba da itama zata kwana,sai wata 'yar uwarsu badi'a,itama ba aure ne da ita ba.
Tunda can dama ba wani shiri suke sosai da suwaiba ba,don haka da badi'a suka gaisa kawai,ta diba kayan wankanta ta shige bandakin tayi wanka,sannan ta fito ta dauki kayan da zata saka ta wuce dakin hajja donta shirya,saboda ta fuskanci kamar suwaiba ta sanyawa duk wani motsinta ido,batason ta fusata harta buda baki ta gaya mata magana,shi yasa tabar musu dakin da niyyar kwana dakin hajja.