← Book details Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 69

Sashe 45

Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dai dai sanda ya sake dawowa dakin bayan ya gama shirin barcinsa yaga iya abincin data ci din,sauri yadan qara zuwa inda take kwancen,sai yaja da baya,ya zuba ruwan dumin daya tafasa ya barshi yadan sha iska cikin cup din daya dauko,ya sanyata ta sake zama tana sharar qwalla.

Kallo daya yayi mata ya dauke kanshi yana tuna zahra,lokacin da qwalla ke fita daga idanunta kamar haka,tana cewa ya yafe mata mutuwa zatayi,bai taba kawo mata mutuwar ba a sannan sai gashi ta tafin,wannan tunanin yaji ya motsa zuciyarsa,wannan tunanin yasa yaji baiso yabar dakin,hakanan ya di ga jin idan yabar dakin kamar wani mummunan abu zai biyo baya,saboda haka ya koma dakinsa ya dauko duk abinda yasan zaya iya buqata ciki harda sytem dinsa da wayoyinsa ya dawo dakin,a lokacin tayi rub da ciki cikin bargo,bata juye juye kamar daxu,saidai lokaci zuwa lokaci takan motsa,da alamu ta samu relief ne daga ciwon.

Saman kujerar dakin yayi zamanshi bayan ya maida dakin dim light,saiya bude system dinsa ya soma rage aiki,aikin yadda zai gudanar da office dinsa,da kuma bataliyar rundunar sojin dake qarqashin jagorancinsa,ya soma tsara komai bisa hikima,saidai baya daukar wasu mintuna masu tsaho bai daga kai ya dubeta ba.

A hankali ya zare gilashin idanunsa da yake amfani dashi idan zai dade saman screen na waya ko system,ya ajeshi gefe yana miqa,ya sake duban inda take kwance sau babu adadi,har yanzu dai ba alamar bacci ya dauketa,saiya tattare komai waje daya,ya taka a hankali har ya isa saman katifar,ya zauna sosai,saita rintse idanunta tana jin yadda ya zauna gefan nata kamar tayi kusanci da yawa,gabanta ya dinga faduwa,sanda ya dora hannunsa saman goshinta da wuyanta bayan ya yaye bargon data rufa numfashinta ya sake yi mata wahalar shaqa,hakan yasa yadan firgita,saiya dagota daga kwanciyar da tayin,ba tre da tunanin komai ba ya zira dukkanin hannunsa cikin rigarta ta baya,ya kama maballin bra dinta yana qoqarin balle mata wai ko zata samu damar shaqar numfashin sosai,kamar yadda yaga suna yiwa juna sometimes a gida ko a battlefield idan tsautsayi ya ritsa da dayansu numfashi ya fara masa wuyar shaqa,suna cire masa duk damarar dake jikinsa don a rage masa wahala.

Ji tayi kamar zuqa daya ya rage mata na iska a duniya sanda taji dumin hannunsa a bayanta,kawai saita tafi luu gaba daya zuwa jikinsa tana jin wuta na dauke mata,bai damu ba,hakan ma saiya rage masa aiki,ya balleta gaba daya ya saka hannu ya zareta ya wurgata gefe,sai kawai ya gyara mata kwanciya saman cikinsa ta rub da ciki yadda ya fuskanci tafi jin dadin kwanciyar,bata da wani zabi da ya wuce tayi likimo,babu qarfin zame kanta daga gareshi,sannan tsoro da tsananin mamakin jinta kwance tsakiyar qirjin mutumin da bata taba kawowa kanta hakan ba yasa batajin akwai wata kalma guda daya da zata iya fita daga bakinta.

Wani dumi ne ya dinga ratsata,duka sanyin da takeji yayi nasa waje,daddadan turaren aliyyu daya zama tambarinsa ya baibaye dukka kafar hancinta,lallausan gashin qirjinsa ya dinga gogar fatar fuskarta,ta dinga jan numfashinta da nauyi tana saukewa,ba tare da saninta ba sai hakan ya zamana kamar wani communication ne tsakanin jikinta da nashi,sai ya zamana kamar tana pushing jikinta da nashi.

"Subhanallah" ya fada cikin zuciyarsa yana qaryata kansa,take ya dinga jin tsigar jikinsa na zubawa,saiya dunqule kowane hannu nasa ya damqe tafin hannunsa sosai,sai a sannan ya lura ya kuma gane gangancin daya aikata,wanda shi sam bai kawo hakan ba,ya karkata tunaninsa da son ganin ta samu relief na ciwon da takeji.

Ga mamakinta kuma saita dinga jin komai yana daidaita,numfashinta ya fara zama dai dai,hakanan ciwon shima yana raguwa da kadan da kadan,sai kuma idanunta suka fara nauyi kamar an dora mata dutse,da alamu qaqqarfan bacci ne yakeson sureta,wanda ciki qanqanin lokaci ba tare data ankara ba yayi awon gaba da ita.31

_RANO NET! RANO NET! RANO NET!_

_WHO NO LIKE BETA AWUUF THINGS?_

_IDAN KAJI GANGAMI DA LABARI....! INA MASU ZUBIN ADASHEN DA BA RANAR DAUKA NA DATA?_

_TO KU MARMATSO KUJI, KU KUMA SHARE HAWAYEN KU, MUNZO MUKU DA SABBIN TSARE TSARE NA DATA, WADDA KOWA ZAI IYA SAYA DAI DAI KARFIN SA. A FARASHI MAI RAHUSA_

_RANO NET! RANO NET! RANO NET!__
_(Afford data at chikini price)_
_MALLAKI DATA A KUDI KALILAN DA RANO NET_

_TSAYA KUJI, A RANO NET ZAKA IYA ZAMA RESELLER KO WHOLESALER KAI MA, EH ZAKA/KI IYA ZAMA MA SAYAR DA DATA A FARASHIN SARI MUKE BAYARWA, KAI/KI KAFA KASUWANCIN KU KUMA. DA KUDI KALILAN._

_MUNA KUMA SAYARWA AKAN ‘DAI DAYA, KOWANE NETWORK MUNA SAYARDA DATA PLAN DINSA AKAN KUDI KALILAN, MASU FARASHIN SARA KUWA MA KU KUDIN BAI KAI HAKA BAMA_

_AIRTEL_
_9MOBILE/ETISALAT_
_MTN_
_GLO_

_DUK MUNA SAYARDA TSARIN DATA DINSU. KAMAR MISALI MTN MUNA SAYARDA 1GB.24MB AKAN FARASHIN NERA 300 KUMA YANA KAIWA WATA DAYA, GWARGWADON YADDA KAKE AMFANI DA DATA, 2GB 600, 3GB 900!!_

_DUKA WADANNAN TSARIN DATA DAMA NA SAURAN LAYIKA MUNA SAYRWA AKAN FARASHI MAI RAHUSA, WANDA KOWA ZAI IYA YIN TSARIN DAI DAI ALJIHUN SA_

_Ranonet.com.ng_
_GA SITE DINMU NAN DAKE YANAR GIZO, KAI TSAYE ZAKI/KA IYA SIYAN NAKA TA NAN. _

_KO A TUNTUBE MU TA NAMBAR TARHON MU: +234 803 081 1300/+234 808 540 5215_

_KYAU, INGANCI, RAHUSA, ADADE ANA YAWO A YANAR GIZO SAI RANO NET._

_RANO NET..!!!!_
___________________________________

Yadda yaji numfashinta na sauka a hankali cikin nutsuwa ya tabbatar masa da tayi bacci,hannunsa yasa zai sauketa saita motsa,hakan yasa ya fasa ya maida hannunsa ya ajiye,tsahon minti biyar ya sake daga hannun nasa zai sauketa,hakanan wannan karon a karan kansa yaji ya kasa,saiya sake maida hannun nasa ya ajiye yana maida numfashi gami da runtse ido,wani irin yanayi yakeji cikin jikinsa,irin wanda tunda yake bai taba jinsa ba,wani nauyin jiki da kasala yakeji,minti daya biyu saiya kalli fuskarta,duk da baya iya ganinta sosai saboda fuskar na kife a saman wuyansa ne,gaba daya jikinta dake manne da nashi ya soma takurashi gami da rikita masa lissafi.

Yayi tsammanin zai jure amma saiya kasa,don haka tilas tasa ya zameta daga jikin nasa cikin dabara,ya koma gefe yan furzar da iska daga bakinsa,ya kuma kulle idanunsa,sannu a hankali jikinsa ya soma nauyi shima,bacci ya qara maaa rauni da kasala,saiga bacci ya fisgeshi ba tare daya sani ba.

Dukkansu babu wanda ya sake farkawa, saishi ne da akayi kiran sallah firgigit ya tashi,sam ya mance a inda yake sai daya nutsuwarsa ta dawo jikinsa,saiya miqe a hankali bayan ya gama addu'ar tashi daga bacci ya miqe a nutse ya nufi bandaki.

Alwala ya daura,ya dauki dadduma a nan dakin,sannan ya dubeta yana qarasa inda take,yasa hannunsa saman pillow din da take kwance ya bubbuga,ta bude idonta dake cike da bacci sai cikin nasa,tayi saurin mayarwa ta rufe,shi kuma ganin haka ya sanyashin yin gaba yana cewa
"Lokacin sallah yayi" yana qarasa ficewa daga dakin.

A nutse ta sauka daga gadon zuwa bandaki tana tuna abinda ya wakana daren jiyan,dukka jikinta babu abinda yake sai fidda qamshin turarensa duk motsin da zatayi,duk sai taji wani irin kunya da nauyinsa sun saukar mata wanda bata taba ji ba sanda ta tsaya gaba madubi ta tuna shi ya cire mata bra,ita kadai a bandakin amma sai ta dinga ji kamar yana kallonta,tasa hannu ta cukuikuye rigarta ta nufi gaban sink ta daura alwala sannan ta fito.

Tana fitowa daga bandakin sanda ta miqa hannunta ta baya tana rufe qofar toilet din shi kuma yana shigowa,kai tsaye idanunsa suka sauka a kanta,rigar jikinta ta kwanta sosai a fatarta,ta yadda duk wanda ya kalleta yasan babu brazier a jikinta,hakan ya baiwa albarkatun qirjinta damar tsayawa sosai kowanne a muhallinsa.

Kamar wanda aka sanyawa shocking haka yaji,ya dauke kansa da wani irin sauri yana qarasa shigowa ciki ya kuma nufi kan gado kai tsaye,yayin da ita kuma ta qame a tsaye cukuikuye da gaban rigarta,gabanta na wani irin faduwa saboda lura da tayi da inda yake kalla din.

Saman katifar ya haura,ya dage filo ya dauki wayarsa,da alama ita ya manta ya dawo dauka,saidai yana miqewa yaci tuntube da breezier dinta,saiya janye qafarsa a hankali ya sauko ya fice.

Da sauri ta qarasa ta sakawa qofar key tana sakin numfashi,wai wannan wane irin abun kunya ne haka,sai data kusan makara sannan ta samu tayi sallar bayan ta tattare katifar.

Har wajen sha daya saura na safe tana dakin bata fita,duk da tayi wanka,amma nauyin haduwa dashi yasa ta kasa fita,uwa uba kuma mararta daketa qulle mata,addu'a take Allah yasa kada period din yazo sai ta koma gida.

A hankali ta bude qofar sanda taji anyi knocking,saita labe daga bayan qofar ta yadda bazai iya hangota sosai ba,haka itama.

Muryarsa kawai taji da mayen qamshin turarensa yana cewa
"U know you r sick....ki fito ki samu wani abu kici"
"Okey" ta amsa masa tana sakin qofar,ta koma cikin dakin tana laluben me zata yafa,ta ciji yatsa tayi Alla wadarai da wadanda suka hada mata kaya,kaf kayan babu hijabi ko daya,sai sannan ta tuna yace mata ta rubuta list na abinda take buqata amma batayi hakan ba,saboda batason abinda zai ja ta dade bata koma gida ba,kodon jarabawarta data tabbatar duk abinda akw ciki ba zasu wuce two weeks basu fara ba,inda kuma ta rubuta din wala'alla ta hada harda shi,amma yanzun idan sun dawo dole ta rubuta abinda ba'a rasa ba,dole qanwar naqi ta dauki mayafi ta yafa.

Saman dining ta sameshi da waya a hannunsa yana dannawa,yana jin takunta ya dago kai,ga mamakinsa ba inda idanunsa ya sauka sai a qirjinta,yayi maza ya dauke kai yana jan tsaki can qasan ransa,mugun haushin kansa ya kamashi,meya kaishi ma daga kai koda fuskarta zai kalla bare wani sashe na jikinta,inda Allah ya taimakeshi bata kula da hakan ba harta qarasa,taja kujera ta zauna,ta gaidashi ya amsa yana ci gaba da danne danne a wayarsa,bata ma sani ba shi ko yayi breakfast din ko beyi ba,ta hada ruwan zafi ta fara kurba a hankali,tana jinta duk a takure saboda zamanshi a wajen.
Chapter 45 · 0% Book details