Sashe 61
Alqibla Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kowanne a parlour din son barka yake gami da sanya masa albarka,tare da yaba wannan namijin qoqarin sa yayi
"naso ace na qara da abban tsakiya da abba yusuf,to amma kudin hannuna sun qare,ba zasu isa ayi komai na mutum biyu ba,amma in sha Allah sune a lissafina na gaba" nunawa sukayi babu komai,su da dan uwan nasu duka abu dayane,sannan suna da yaqinin da yardar Allah shi mai kai kowa ne cikin dangi idan da halin yiwuwar hakan.
Sun dan jima anan suna tattaunawa cike da farinciki,kafin daga bisani suyiwa hajja sallama kowa ya nufi wajen neman kudinsa,sai falon ya rage daga hajjan sai haidar din,sai kuma zahra dake kitcehn tana dora abincin rana kawai don idan ta zauna ta huta gaba daya,inna gaje ciwon qafa ya hanata zuwa aiki tun shekaran jiya.
Kira hajjan ta qwalawa zahra tace ta fito da abincin haidar,ta zata kai masa za'ayi,batayi tunanin yana falon ba don haka ta fito gaba gadi haka abunta,wata straight gown ce a jikinta,wadda tayi mata das a jikinta.
Da kallo ya bita bayan ta gaidashi ta aje masa abincin ta koma,suna hada ido da hajja ya hade rai tsam sannan yace
"Yanzun haka take yawo anan?"
"To uban mutane,sai akayi yaya?ni bama wannan ba,tafiyar nan da zahra'u ya dace ayita,don baka je dakin Allah haka ziqau ba,kabar kyautar da yayi maka a gida ba" kallonta yayi ya soma zuba abincin yau da kanshi ba tare daya nema wani ya zuba masa ba
"Yanzu dai babu kudi hannuna,saidai nan gaba idan Allah yayi" hade ranta tayi sosai
"Eh na sani ai ubana.....ni zan biya mata da kaina,saboda haka a sama mata komai da komai,idanma za'a dage tafiyar sai lokacin data samu to a dage din" baice mata komai ba,dama kuma tasan halinta ba zaya tanka ba,don haka taci gaba da sabgarta kawai,tana ta kiran 'yan uwa daya kamata su sani tana gaya musu batun biya mata umarar,abun mamaki kuma don iya qarfa qarfa irin na hajja sai take hadawa da zahra kan harda ita za'a tafin,shidai yana zaune yana cin abinci yana kuma kallon ikon Allah,zahra kuwa na kitchen bata ma san wainar da ake toyawa ba.
Sai da ya gama cin abincinsa sannan ya miqe ya fice,dole zaiyi maganin hajja,zai kawo qarshen wannan mulkin mallakar nata,zata ga nasa qarfin ikon akan aurensa,don haka tun a motarsa driver na jansa ya kira anty alawiyya.
Bayan sun gama gaisawa tayi masa godiya da addu'ar qaruwar aziqi kan umarar da ya biyawa iyayensu saiyayi mata maganar da ita ta sanya ya kiratan
"Kaya nakeso a hadamin,irin wanda ake hadawa amare a akwati" dariya ce taso kubce mata amma ta danne,don kada tayi dariyar ta jama kanta jagwal,duk da cewa ita ke gaba dashi
"Ohkey.....lefe kenan....kaman na nawa?,kuma akwati nawa?"
"Akwati bakwai is okey,nayi hidima da kudaden hannuna....amma banison kaya low quality please,designers kumadd high quality"
"In sha Allah babu matsala"
"Please su zama ready kafin na dawo"
"To shikenan....babu damuwa" saiya yanke wayar ya aje gefa,ya maida idanunsa kan titunan da suke wucewa.40
Wayar ya sake jawowa,wata number ya sake laluba,wanda suke masa aikin ginin filin da ya siya a nan,yadan jima da siyan filin,tun farkon fara aikinsa ya hada albashinsa ya siya,hakanan da kadan da kadan ake aikin gininsa,yadda zaifi masa sauqi bazai wahala ko ya kashe kudi masu yawa ba lokaci guda,zuwa yanzu ginin yayi nisa qwarai,don abinda ya rage ma sauran abubuwan da ba'a rasa bane,da farko yayi niyyar ma ya kammala gidan ya saida,amma da yayi tunani sai yaga,bashi da mazauni kenan duk sanda yazo ganin gida saidai a cikin gidansu,auren da aka daura masa da zahra yasa ya fasa saidashin kwata kwata,saboda koba zahra ba dama dole zaiyi aure,idan kuma yayi auren zai dawwama zuwa gidansu ya zauna?,dole yana buqatar muhalli.
Da kamfanin yayi magana,ya shaida musu abinda yake da buqata cikin gidan,suka gaya masa kudinsa da zaya bayar,yayi musu alqawarin turawa zuwa qarshen wata,a sannan suna can basu dawo ba kenan a yadda ya lissafa,yana saka ran kuma kafin su dawo din an kammala komai,saiya aje wayarsa yana ci gaba da lissafe lissafensa cikin ransa,zuciyarsa fes,yana jin wata nutsuwa da sukuni suna ratsashi.
******** **** ********
Bai sakewa hajja zancan tafiyar zahran ba,kamar yadda bai amshi kudinta ba,tayi tunanin waskewa yakeson yi,saita matsa da mita da qorafi,sai ranar daya sameta zaune ya miqa mata komai da komai na tafiyar zahran da aka kammala bayan an dage tasu tafiyar da sati daya.
Kwalla ce ta qwacewa hajjan,abinda bai taba zaton gani daga idanunta ba,duka shida zahra dake zaune a gefanta suka zuba mata ido,jikinsu duka yayi sanyi
"Allah yayi maka albarka,ubangiji yaci gaba da gin riqo da hannayenka,Allah ya kula maka da rayuwarka,yadda kake taimakon al'ummar annabi kake kula da iyayenka da 'yan uwanka....Allah yayi maka kyakkyawan sakamako,haidar....kaida zahra Allah shine shaida....kaf cikin jikokina babu wadanda suka shiga raina kamar yaku,hakan ya sanya nan duniya tun kuna da qanana bani da burin daya wuce Allah ya hada kanku kuso juna ku zama miji da mata,sai wani al'amari me daure kai ya soma gudana a tsakaninku,amma hikima ta ubangiji da baya maida addu'ar bawansa,sai gashi ya kawo hadin aurenku ta fuskar dani kaina ban tsammata ba.....haidar....ga zahra nan,a yau zan baka amanarta...ka riqe amanar zahra,kai da ita duka nasan halayenku...hakan ya sanya nake da yaqinin dukkanku kun dace da junanku,zaku gasgata abinda nake fada din,zahra,haidar yayanki ne kuma mijinki,ki bishi ki masa biyayya,ki masa biyayya kamar yadda musulunci ya tanada,Allah ya albarkaci rayuwarku" cikin sanyin jiki dukkansu suka amsa da amin,saita miqawa zahra passport din hannunta
"Zaki tafi umara tare damu,mijinki ya biya miki" kamar a mafarki taji fitar furucin daga bakin hajjan,saita daskare a zaune tana jujjuya passport din,yau itace zata qasa me tsarki ta qarqashin ya haidar din?,mutumin da take masa kallon mara qaunarta,wanda bayason yaga suna farinciki da walwala?,mutumin da take kiranshi da mara ALKIBLA?,mai baudadden hali,wanda sam ALKIBLARSU bata zo daya ba,ashe ta sanadinsa zata je taga ma'aiki?sai qwalla ta cika mata idanu,ta sake matsawa kusa dasu muryarta na rawa saboda farinciki
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi,ya qara budi,ubangiji ya biya da jannatulfirdaus" idanunsa ya lumshe yana jin dadin muryarta hade da dadin addu'ar data yi masa ya amsa da
"Amin".
"Wannan kadanne daga alkhairinsa,alkhairin nasa kuma da zaya shiga rayuwarki matuqar kika ci gaba da bin maganar magabatanki,matuqar kika ci gaba da daukar zancansu da muhimmanci,na taba gaya miki,haidar ba irin sauran maza bane gama gari,tun a shekarun quruciya na gama karantar halayyarsa tsaf,tun kafin na haifeki nake sha'awa inama ina da diya da idan ya girma zan bashi ita?,yana da boyayyun nagartattun halaye da dabi'u,yana da sauqin kai da sanyin hali,yana da tausayin mace.....amma dukka ba kowa ke iya karanta da gane hakan ba,saboda matuqar zaka mu'amalanceshi daga nesa,to tabbas zaka masa fassarar mai ra'ayin riqau,mai kakkausan hali,mara tausayi ne,mai zafi da saurin fushi,eh aliyyu yana da ra'ayin riqau akan gaskiya,yana da kafiya kan abinda yasan shine dai dai,yana da fushi idan yasan an sabawa dai dai ko doka,yana da rashin tausayi akan azzalumin mutum mara imani,amma matuqar baka da irin wadan nan siffofin,zakaji dadin zama da haidar fiye da kowane dan adam.....zan baki tips na zama da haidar din,a matsayinki na diyata,ni kuma uwa a gareshi da tasan halayyarsa,ba don ki mallakeshi ba,sai don ki masa biyayya ku samu zaman lafiya da qauna me dorewa" wadan nan sune lafuzzan umminta a sanda take shaida mata batun tafiya da ita bayab ta miqa mata passport dinta ta sanya masa albarka,zama ummin tayi ta dinga zayyana mata abubuwa masu matuqar amfani a rayuwarsu,har zahran ta dinga mamaki da kunyar hakan,saidai ta lura ummin ko a jikinta,saboda ta sani tana gyara rayuwar diyarta ne,tana kuma inganta rayuwar haidar dinta,aikine da takejin ya wajaba a kanta a matsayinta na uwa
*_AMINU KANO INTERNATIONAL AIRPORT KANO_*
Da motoci hudu duka aka dunguma aka tafi rakiyarsu filin jirgin saman don wucewa qasa me tsarki,suna ajesu sukayi bankwana dasu aka maida motar gida,dama daya ta abba yusuf ce,daya ta abban tsakiya,zasu wuce kuma kasuwa ne abinsu,sauran biyunne na haidar,mustapha yaja daya,ya shamsu da suke tare da ya sadiq sukaja daya suka koma gida da sauran yaran gidan da aka taho dasu.
Gaba daya wani irin nauyi takeji,surukutar abba babba da mama takeji tana mamayarta,ko hira ake bata iya magana cikinsu,dama shi haidar din ba wani gwanin magana bane,sau tari wayarsa tana hannunsa ne yana faman danne danne,wanda baya wuce duba labarai,ko duba saqonni da suka shafi aikinsu.
Yana ankare da yadda ta kasa sakewa din,nutsuwar data sakeyi ta bashi mamaki,kusan tun tale tale yasan zahra cikin yaran gidan,tayi shuhura wajen aikata laifi da samun kariya daga wajen hajja da a wancan lokacin yake ganin daure mata qarqashi kawai takeyi,abinda ya janyo rashin jituwarsu kenan,yaci alwashin shi bazai bari ta buwayi kowa ba,duk da girma ya sake canzata qwarai,amma a yau din ta sake canzawa,wata kamala ta musamman ke kwaranya tun daga fuskarta zuwa jikinta.
Qafarshi daya dora daya kan daya ya sauke bayan ya gama karantarta,ya duba agogon hannunsa,akwai sauran lokaci kafin a nemi passingers din,don haka ya miqa a nutse yana daukar hularsa dake ajjiye gefe ya soma takowa inda suke.
Ita ta fara ganinsa,a sace take kallonsa,tunda suke da shi ba zata iya tuna sau nawa ta taba ganinsa da qananun kaya ba,yau sai gashi sanye da wata dakakkiyar shadda gezner gray colour,sabuwar dal,sai maiqo take da daukar idanu,wani irin annurin kyau yake fitarwa na musamman,gaba daya kamanninsa sun canza kamar ba Aliyyu haidar sojan nan ba,batasan yaganta,batasan tunda ta fara kallonshin ya ganta ba sai da yazo dab da ita,ba tare da su abba suna gani ba yadan ranqwafa ta gefan kunnenta kamar xai dauki wani abu
"Idan kinaso kawai kice kinaso,kada ki wani damu da jan ajin nan naki" saiya miqe ya barta daskare cikin tsananin jin kunya da nauyi,yayin daya bar mata sauran turarensa tana shaqa wanda ke qara sanyata cikin wani yanayi nason kasancewa dab dashi
"Waini babu inda zan samu ruwa ne,ishirwa fa nake ji tunda muka fito daga gida" hajja ta fada,sai haidar din yace
"Akwai.....muje a duba mata" yayi maganar yana duban zahra,a hankali ta miqe,tayi gaba yabi bayanta.
"naso ace na qara da abban tsakiya da abba yusuf,to amma kudin hannuna sun qare,ba zasu isa ayi komai na mutum biyu ba,amma in sha Allah sune a lissafina na gaba" nunawa sukayi babu komai,su da dan uwan nasu duka abu dayane,sannan suna da yaqinin da yardar Allah shi mai kai kowa ne cikin dangi idan da halin yiwuwar hakan.
Sun dan jima anan suna tattaunawa cike da farinciki,kafin daga bisani suyiwa hajja sallama kowa ya nufi wajen neman kudinsa,sai falon ya rage daga hajjan sai haidar din,sai kuma zahra dake kitcehn tana dora abincin rana kawai don idan ta zauna ta huta gaba daya,inna gaje ciwon qafa ya hanata zuwa aiki tun shekaran jiya.
Kira hajjan ta qwalawa zahra tace ta fito da abincin haidar,ta zata kai masa za'ayi,batayi tunanin yana falon ba don haka ta fito gaba gadi haka abunta,wata straight gown ce a jikinta,wadda tayi mata das a jikinta.
Da kallo ya bita bayan ta gaidashi ta aje masa abincin ta koma,suna hada ido da hajja ya hade rai tsam sannan yace
"Yanzun haka take yawo anan?"
"To uban mutane,sai akayi yaya?ni bama wannan ba,tafiyar nan da zahra'u ya dace ayita,don baka je dakin Allah haka ziqau ba,kabar kyautar da yayi maka a gida ba" kallonta yayi ya soma zuba abincin yau da kanshi ba tare daya nema wani ya zuba masa ba
"Yanzu dai babu kudi hannuna,saidai nan gaba idan Allah yayi" hade ranta tayi sosai
"Eh na sani ai ubana.....ni zan biya mata da kaina,saboda haka a sama mata komai da komai,idanma za'a dage tafiyar sai lokacin data samu to a dage din" baice mata komai ba,dama kuma tasan halinta ba zaya tanka ba,don haka taci gaba da sabgarta kawai,tana ta kiran 'yan uwa daya kamata su sani tana gaya musu batun biya mata umarar,abun mamaki kuma don iya qarfa qarfa irin na hajja sai take hadawa da zahra kan harda ita za'a tafin,shidai yana zaune yana cin abinci yana kuma kallon ikon Allah,zahra kuwa na kitchen bata ma san wainar da ake toyawa ba.
Sai da ya gama cin abincinsa sannan ya miqe ya fice,dole zaiyi maganin hajja,zai kawo qarshen wannan mulkin mallakar nata,zata ga nasa qarfin ikon akan aurensa,don haka tun a motarsa driver na jansa ya kira anty alawiyya.
Bayan sun gama gaisawa tayi masa godiya da addu'ar qaruwar aziqi kan umarar da ya biyawa iyayensu saiyayi mata maganar da ita ta sanya ya kiratan
"Kaya nakeso a hadamin,irin wanda ake hadawa amare a akwati" dariya ce taso kubce mata amma ta danne,don kada tayi dariyar ta jama kanta jagwal,duk da cewa ita ke gaba dashi
"Ohkey.....lefe kenan....kaman na nawa?,kuma akwati nawa?"
"Akwati bakwai is okey,nayi hidima da kudaden hannuna....amma banison kaya low quality please,designers kumadd high quality"
"In sha Allah babu matsala"
"Please su zama ready kafin na dawo"
"To shikenan....babu damuwa" saiya yanke wayar ya aje gefa,ya maida idanunsa kan titunan da suke wucewa.40
Wayar ya sake jawowa,wata number ya sake laluba,wanda suke masa aikin ginin filin da ya siya a nan,yadan jima da siyan filin,tun farkon fara aikinsa ya hada albashinsa ya siya,hakanan da kadan da kadan ake aikin gininsa,yadda zaifi masa sauqi bazai wahala ko ya kashe kudi masu yawa ba lokaci guda,zuwa yanzu ginin yayi nisa qwarai,don abinda ya rage ma sauran abubuwan da ba'a rasa bane,da farko yayi niyyar ma ya kammala gidan ya saida,amma da yayi tunani sai yaga,bashi da mazauni kenan duk sanda yazo ganin gida saidai a cikin gidansu,auren da aka daura masa da zahra yasa ya fasa saidashin kwata kwata,saboda koba zahra ba dama dole zaiyi aure,idan kuma yayi auren zai dawwama zuwa gidansu ya zauna?,dole yana buqatar muhalli.
Da kamfanin yayi magana,ya shaida musu abinda yake da buqata cikin gidan,suka gaya masa kudinsa da zaya bayar,yayi musu alqawarin turawa zuwa qarshen wata,a sannan suna can basu dawo ba kenan a yadda ya lissafa,yana saka ran kuma kafin su dawo din an kammala komai,saiya aje wayarsa yana ci gaba da lissafe lissafensa cikin ransa,zuciyarsa fes,yana jin wata nutsuwa da sukuni suna ratsashi.
******** **** ********
Bai sakewa hajja zancan tafiyar zahran ba,kamar yadda bai amshi kudinta ba,tayi tunanin waskewa yakeson yi,saita matsa da mita da qorafi,sai ranar daya sameta zaune ya miqa mata komai da komai na tafiyar zahran da aka kammala bayan an dage tasu tafiyar da sati daya.
Kwalla ce ta qwacewa hajjan,abinda bai taba zaton gani daga idanunta ba,duka shida zahra dake zaune a gefanta suka zuba mata ido,jikinsu duka yayi sanyi
"Allah yayi maka albarka,ubangiji yaci gaba da gin riqo da hannayenka,Allah ya kula maka da rayuwarka,yadda kake taimakon al'ummar annabi kake kula da iyayenka da 'yan uwanka....Allah yayi maka kyakkyawan sakamako,haidar....kaida zahra Allah shine shaida....kaf cikin jikokina babu wadanda suka shiga raina kamar yaku,hakan ya sanya nan duniya tun kuna da qanana bani da burin daya wuce Allah ya hada kanku kuso juna ku zama miji da mata,sai wani al'amari me daure kai ya soma gudana a tsakaninku,amma hikima ta ubangiji da baya maida addu'ar bawansa,sai gashi ya kawo hadin aurenku ta fuskar dani kaina ban tsammata ba.....haidar....ga zahra nan,a yau zan baka amanarta...ka riqe amanar zahra,kai da ita duka nasan halayenku...hakan ya sanya nake da yaqinin dukkanku kun dace da junanku,zaku gasgata abinda nake fada din,zahra,haidar yayanki ne kuma mijinki,ki bishi ki masa biyayya,ki masa biyayya kamar yadda musulunci ya tanada,Allah ya albarkaci rayuwarku" cikin sanyin jiki dukkansu suka amsa da amin,saita miqawa zahra passport din hannunta
"Zaki tafi umara tare damu,mijinki ya biya miki" kamar a mafarki taji fitar furucin daga bakin hajjan,saita daskare a zaune tana jujjuya passport din,yau itace zata qasa me tsarki ta qarqashin ya haidar din?,mutumin da take masa kallon mara qaunarta,wanda bayason yaga suna farinciki da walwala?,mutumin da take kiranshi da mara ALKIBLA?,mai baudadden hali,wanda sam ALKIBLARSU bata zo daya ba,ashe ta sanadinsa zata je taga ma'aiki?sai qwalla ta cika mata idanu,ta sake matsawa kusa dasu muryarta na rawa saboda farinciki
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi,ya qara budi,ubangiji ya biya da jannatulfirdaus" idanunsa ya lumshe yana jin dadin muryarta hade da dadin addu'ar data yi masa ya amsa da
"Amin".
"Wannan kadanne daga alkhairinsa,alkhairin nasa kuma da zaya shiga rayuwarki matuqar kika ci gaba da bin maganar magabatanki,matuqar kika ci gaba da daukar zancansu da muhimmanci,na taba gaya miki,haidar ba irin sauran maza bane gama gari,tun a shekarun quruciya na gama karantar halayyarsa tsaf,tun kafin na haifeki nake sha'awa inama ina da diya da idan ya girma zan bashi ita?,yana da boyayyun nagartattun halaye da dabi'u,yana da sauqin kai da sanyin hali,yana da tausayin mace.....amma dukka ba kowa ke iya karanta da gane hakan ba,saboda matuqar zaka mu'amalanceshi daga nesa,to tabbas zaka masa fassarar mai ra'ayin riqau,mai kakkausan hali,mara tausayi ne,mai zafi da saurin fushi,eh aliyyu yana da ra'ayin riqau akan gaskiya,yana da kafiya kan abinda yasan shine dai dai,yana da fushi idan yasan an sabawa dai dai ko doka,yana da rashin tausayi akan azzalumin mutum mara imani,amma matuqar baka da irin wadan nan siffofin,zakaji dadin zama da haidar fiye da kowane dan adam.....zan baki tips na zama da haidar din,a matsayinki na diyata,ni kuma uwa a gareshi da tasan halayyarsa,ba don ki mallakeshi ba,sai don ki masa biyayya ku samu zaman lafiya da qauna me dorewa" wadan nan sune lafuzzan umminta a sanda take shaida mata batun tafiya da ita bayab ta miqa mata passport dinta ta sanya masa albarka,zama ummin tayi ta dinga zayyana mata abubuwa masu matuqar amfani a rayuwarsu,har zahran ta dinga mamaki da kunyar hakan,saidai ta lura ummin ko a jikinta,saboda ta sani tana gyara rayuwar diyarta ne,tana kuma inganta rayuwar haidar dinta,aikine da takejin ya wajaba a kanta a matsayinta na uwa
*_AMINU KANO INTERNATIONAL AIRPORT KANO_*
Da motoci hudu duka aka dunguma aka tafi rakiyarsu filin jirgin saman don wucewa qasa me tsarki,suna ajesu sukayi bankwana dasu aka maida motar gida,dama daya ta abba yusuf ce,daya ta abban tsakiya,zasu wuce kuma kasuwa ne abinsu,sauran biyunne na haidar,mustapha yaja daya,ya shamsu da suke tare da ya sadiq sukaja daya suka koma gida da sauran yaran gidan da aka taho dasu.
Gaba daya wani irin nauyi takeji,surukutar abba babba da mama takeji tana mamayarta,ko hira ake bata iya magana cikinsu,dama shi haidar din ba wani gwanin magana bane,sau tari wayarsa tana hannunsa ne yana faman danne danne,wanda baya wuce duba labarai,ko duba saqonni da suka shafi aikinsu.
Yana ankare da yadda ta kasa sakewa din,nutsuwar data sakeyi ta bashi mamaki,kusan tun tale tale yasan zahra cikin yaran gidan,tayi shuhura wajen aikata laifi da samun kariya daga wajen hajja da a wancan lokacin yake ganin daure mata qarqashi kawai takeyi,abinda ya janyo rashin jituwarsu kenan,yaci alwashin shi bazai bari ta buwayi kowa ba,duk da girma ya sake canzata qwarai,amma a yau din ta sake canzawa,wata kamala ta musamman ke kwaranya tun daga fuskarta zuwa jikinta.
Qafarshi daya dora daya kan daya ya sauke bayan ya gama karantarta,ya duba agogon hannunsa,akwai sauran lokaci kafin a nemi passingers din,don haka ya miqa a nutse yana daukar hularsa dake ajjiye gefe ya soma takowa inda suke.
Ita ta fara ganinsa,a sace take kallonsa,tunda suke da shi ba zata iya tuna sau nawa ta taba ganinsa da qananun kaya ba,yau sai gashi sanye da wata dakakkiyar shadda gezner gray colour,sabuwar dal,sai maiqo take da daukar idanu,wani irin annurin kyau yake fitarwa na musamman,gaba daya kamanninsa sun canza kamar ba Aliyyu haidar sojan nan ba,batasan yaganta,batasan tunda ta fara kallonshin ya ganta ba sai da yazo dab da ita,ba tare da su abba suna gani ba yadan ranqwafa ta gefan kunnenta kamar xai dauki wani abu
"Idan kinaso kawai kice kinaso,kada ki wani damu da jan ajin nan naki" saiya miqe ya barta daskare cikin tsananin jin kunya da nauyi,yayin daya bar mata sauran turarensa tana shaqa wanda ke qara sanyata cikin wani yanayi nason kasancewa dab dashi
"Waini babu inda zan samu ruwa ne,ishirwa fa nake ji tunda muka fito daga gida" hajja ta fada,sai haidar din yace
"Akwai.....muje a duba mata" yayi maganar yana duban zahra,a hankali ta miqe,tayi gaba yabi bayanta.