← Book details Aindo Tantagariyar Yar Aiki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 45

Sashe 33

Aindo Tantagariyar Yar Aiki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

B'ANGARENTA ta nufa tana murmushi tayi wanka,ta sa doguwar riga wace take iya gwiwa,wani irin sha'awa take ji , wajen yanzu wata daya kenan tunda ta saba da sex yanzu take jin matukar sha'awa saide abun bakin ciki sam Bashir baya gushe mata sha'awar ta,baya tambayar ta tana gamsuwa ko kuwa,kawai shi in ya gamsu shikenan,a yanzu haka ma duk da tanajin yunwa,ga raunin dake jikin ta anma bata jinsa tafi jin sha'awar mijin ta.

Zuwa tayi ta zuba abincin taci ta k'oshi, sanan ta wanke bakin ta ta bare bonbon mai kamshi tasa a bakin ta.

Wajen sa ta nufa ta zauna kusa dashi tare da shafa jikin sa tana masa wani salo mai nuni da tana bukatar sa.

"a'a lfy dai kuwa keeee."

"Plz Bashir sau daya dai ka taimaka ka biya min bukata ta,wallahi ina cik'in bukata,kuma kai daga kayi kake tashi."

"Me kike nufi da hakan,kinga malama bana son rainin hankali,me kika d'auke ni,kije ki shirya muje nace miki bana ciki da rainin sense din ki ,in mun dawo na baki duk ma abinda kike so ."

Ba yanda ta iya haka ta hakura ta tashi ta shirya ta fito.

Katon hijabi tasa,dan tasan jarabar kishin sa wani private asibiti suka nufa,dama ya san doctor din abokin sa ne.

Suna zuwa Office dinsa sukaje direct ,bayan sun gaisa Doctor ya gaisa da A'INDO,nan suka dan taba yar fira,sanan daga bisani Bashir yayi ma Doctor signe da su dan tashi zasuyi magana ne .

Ganin Yanayin Bashir Wanda bata yarda dashi ba sai wani zargi ya tsargu a ran A'INDO ,Dan haka suna fita ta tashi itama ta bisu.wani Office na kusa da wanan suka shiga.
Ita kuma sai ta labe daga k'ofa
Suna zama Doctor din yace"haba Bashir me yasa kake son a juya mahaifar ,ai ka bari koda da daya ku samu da ita ko."

"Bashir yace"Abokina nifa ba haihuwar ce bana so ba a'a daga ita din ne dai bana son haihuwar,soboda bazan haihu da wace batada cikak'en asali ba,kuma wace batada cikak'en dangi ba,in ma akoi su yan kauye ne,kawai ka cire mata cik'in sai a juge mahaifar,inason yara anma ba daga gareta ba,zan auri wata wace take yar wani kusa wada kowa ya sani akasan asalin ta a birni ba a kauye ba,,yar masu kudi kamar ni."

"anma Bashir idan kayi haka baka kyauta ba,yanzu sai ka zabi juya mahaifar baiwar Allah,haba Bashir ai rashin imanin yayi yawa,ga cire ciki ga kuma juya mahaifa.

Gaba-daya wanan abu a kunnuwan A'indo,tabas yau ta shaida cewar Bashir baya sonta tabas yau tagane cewar Bashir ba masoyi bane makiyi ne,tabas yau tasan cewar Bashir shine asalin mugu ba Alhassan ba.
Share hawayen ta tayi tabar asibitin.

Keke napep ta tara ta fada masa unguwar da zai kaita,direct ya kaita gidan ta,ta shiga ta fido kudi ta fito ta basa .

Zama tayi falo ta hada Kai da gwiwa tana kuka kamar ranta zai fita,Bashir ba irin dubawar da basuyi ba basu ganta ba,sai mai gadi suka tambaya suka kwatanta masa mai kaya kala kaza, yace musu ta fito ta tari adaidaita.

Ran Bashir idan yayi dubu to ya baci dan haka bai ma tsaya sauraran doctor ba ya shiga mota ya fice daga asibitin,gidan sa ya nufa,tun a waje yake ihun kiranta,falo ya iske ta ta takure waje daya tana zabga kuka,.

Yana zuwa ya ganta baiyi wata-wata ba ya zuba mata naushi,Wanda ya sata kara sautin kukan ta,yace"dan ubanki Raina ni kikayi da zamuje wuri ki gudo ki barni.

"Allah ya isa tsakani na da kai Bashir ,kuma bazan zubar da cikin nan ba mugu."

"Ke ni kike ma wanan banzar maganar?

"An maka Bashir kayi abinda zakayi."

A'indo ta fada cik'in hargagowa da bakin ciki.

Belt din wondon sa ya zare nan ya fara lafta mata ,ba k'ak'autawa,"zaki bari a cire ko kuwa.?

"Wallahi saide ka kashe ni bazan yarda ba."

"Good good Aisha to bara kiji wallahi ko ki yarda ki tashi muje a zubar da cikin nan ko kuma na yanke igiyoyi uku dake tsakani na dake."

Duk da bala'in da take ji a marar ta Saida ta bud'e baki tace"na k'wanmace ka sake ni zanfi jin dadi,."

Zuciya na dibar sa,ransa a bace ba ko tsayawa tunanin yaje ya d'auko biro da takarda,yazo ya tsaya kusa da ita yace"damar ki ta k'arshe ko ki tashi muje a zubar ko na baki takardar sakin ki."

"Na fada ma ba inda zani kuma wallahi bazan zubar da cikin nan ba."

_Rubutu yayi kamar haka ni Bashir na saki Hassana matata saki uku,saboda na kama ta tana zina da wani namijin Wanda ba ni ba,kuma tayi cikin shege Wanda ba nawa ba._

Yana gamawa ya jefa mata takardar yace"ki tatara inaki inaki kafin na dawo ki barmin gida."

A kwance take da k'yar ta bud'e takardar ta karanta abinda ta gani yayi bala'in girgiza ta,waro idanu tayi a matukar razane tace"Bashir ni kayi ma shairin zina,kuma ka rasa abinda zakayi dogoro dashi sai zina."

Ko sauraran ta baiyi ba ya jata kiiiii sai waje ya yar daidai shigowar Husseina gidan,yayyin da jini ya balle ma A'indo anan take.....

Kuyi hakuri bana Jin dadin jiki na har yanzu kawai Ina dai muku ne hakanan da Babu gwanda kadan...
[04/11 à 19:38] MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE: https://mobile.facebook.com/Anatarewritersassocian/
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*A'INDO*
_(Tantagariyar Yar Aiki_)
✨✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨
✨✨✨✨
✨✨✨
✨✨


*NA*
*MAIMOUNA MATAR ABDOULAYE AM*💋

*🤝🏻ANA TARE WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*
_(We are the best Writers Among All writers_)📚

*DAGA ALKALAMIN MARUBUCIYAR*

👇
*YA MACE KOWACE DA IRIN NI'IMAR TA*,
*LABARIN MAIMOUNATOU*,
*KAICONA*,
*HASSADA GA MAI RABO*,
*YAN MATAN ZAMANI*,
*INA MATSALAR TAKE MAZAN KO MATAN*,
*MAKIRCI*,
*LATIFA*,
*CANJIN RUHI*,
*WACECE NI KAMRINA*,
*SO NE SILAR FARUWAN HAKAN*,
_and Now_👇
*LATIFA SABON SALO*,
*A'INDO (Tantagariyar Yar Aiki)*

_DEDICATED TO SADJIDA & UMMY ONTOP_

*Page -67-68*

ta sume,waro idanu Husseina tayi a razane idrissa da bai ida fita daga gidan ba ta madubi yaga abinda Bashir yayi ma A'indo ,da gudu ya fito daga motar ya nufo su husseina hankali a tashe ya shiga falon ya iske Bashir sai famar huci yake ba shiri yaji idrissa yakai ma Bashir duka a baki,waro idanu Bashir yayi yace"Kai dan uwarka ni zaka doka,
"an dokeka dan iska Wanda baisan darajar mace ba,dama dan ka halaka ta ne yasa ka aureta,dama tunda naji zuciya ta bata kwanta da kai ba nasan kanada wata boyayar fuska a tare dakai."

Dambe ne ya kaure a tsakanin su,inda idrissa ya samu Sa'a ya kayar da Bashir yanata jibga, Husseina ce ta kwala ihun kiran Idrissa tace"idrissa yanzu ba lokacin fada bane dan Allah kazo mu kaita asibiti kaga bata hayacin ta,ga jini da take zubarwa."

Saida idrissa yayi ma Bashir jina jina sanan ya sauka daga kansa ,da gudu suka talabo A'indo suka sata a motar su sukayi asibitin sa dashi da gudu, koda suka isa aka amshe ta ,akayi urgence da ita,nan aka hau kanta dan ganin an tsayar da jinin,anma ina saida ciki ya zube gaba-daya,da k'yar suka samu suka shawo kan matsalar.
Anma ciki kam ya zube,saida akayi Karin jini,da ruwa, gaba-daya ta rame ta fita hayacin ta.

Alhamdulillah Alhassan jiki yayi sauki inda a yau ne kuma aka Salamo sa,duka yan aikin sa da manyan mutane,hata shugaban kasar saida yazo ganin sa,anma banda Mina,a yau aka Salamo su,kuma a yau suka taso,dan takanas shugaban kasa ya bada jirgi aka taho dasu.

Masha Allah ,idan kaga Alhassan kamar ba majinyaci ba,yayi kyau yayi freshe,kawai ramar da yayi ce zaka tabatar da cewa yayi jinya.

A'INDO Saida tayi kwana biyu Husseina ke kulla da ita,anan Suma idrissa ya salamo ta,direct gidan Hajiya suka nufo wanda yayi daidai da shigowar motocin da sukaje tarbon su Hajiya da Alhassan.

Idrissa ne ke jan motar bayan motocin su Alhassan sun gama shiga shima sai ya danno da kan motar sa.,idrissa na murmushin jin dadi suka fito harda A'INDO wace duk ta rame da Husseina, Hajiya ma fitowa sukayi ita da Alhassan,kusan a tatare duk suka fito.

Duk yanda A'indo takai ga ramewa bai hana Al'Hassan ganeta ba ,sai yaji duk ba dadi ganin ta a haka,dan daga gani yasan batada lfy,saurin kawar da fuskar sa yayi sakamokon tunawa da yayi yanzu fa ita matar wani ce,juyawa yayi tare da fakar Idanun mutane yayi saurin goge yar kwalar da ta zubo masa, idrissa ne yaje ya rungume Alhassan yace"waw brother kunyi mana surprise,ya jikin."

"Alhamdulillah."
Alhassan yace tare da sakin Idrissa,ya kalli Hajiya yace"Mom zanje b'angare na na huta."

"To Hajiya" tace

shiko yace hakan ne dan Sam baya son yana ganin A'INDO,dan idan yana ganin ta wani sonta ke kara fizgar shi.

Hajiya ce ta kura ma A'INDO idanu,tare da jansu ita da Husseina,sukayi b'angaren su idrissa na biye dasu.
Halissa ce ke gidan wace har yanzu take zaune miji yaki sakin ta kuma yaki zuwa,dan Khalissa ita tana gidan idrissa yanzu haka ma.can ta koma da zama,saboda kumyar cik'in da tayi,idan ta zauna kusa da Hajiya kara mata damuwa take,yayyin da har yanzu ta kasa fadin waye ya mata cikin.

Bayan sun shiga sun zauna falo, Rabi'u daudu wanda ya dawo daga hutu,ya kawo musu juis da abin ciye ciye, yanata murna,sanan ya tashi domin komawa kitchen.

Hajiya ce tayi gyaran murya tace"Aisha meye ya faru Kika koma haka,Ina mijin naki?

Kecewa da kuka A'indo tayi,nan ta fara ba Hajiya Labarin abinda ya faru,tun da aka kaita tana amarya da yanda Bashir yaso juya Mata mahaifa,har dukan da yayi mata da kuma sakin da yayi mata ,tare da shairin zina .

Innalillahi wa'ina illaihi Raju'un kawai suke nanatawa,dukansu kowane saida ya zubar da kwala,Hajiya tace "Allah nagode ma Allah ka bani ikon cinye wanan jarabawar da take fadawa akan yara na,shairin zina ai ba karamin abu bane,idrissa yace"Mom wallahi sai naja dan iskan nan shari'a."

"a'a karkayi haka,ka barshi da Allah,shi yayi ma kansa,kuma kanshi ya cuta bamu ba,Allah yasa hakan shi yafi Alherie,Aisha kije wancan d'akin ku dinga zama keda Halissa tunda yanzu kamar mai jego kike sai an kulla dake.

Nan tace husseina ta kama ta takaita gatanan zuwa bara tasa a aza mata ruwan zafi.
Chapter 33 · 0% Book details