Sashe 44
Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai tsaye ɗakinsa ya wuce, kanshi ya soma mashi zafi gashi zuciyar sa yana mashi wani irin barazana. Sam baya so ya yarda cewa yana san ta ne, amma ya kasa daina tunaninsa.
Saida ya ganta ya lura ba Miemie yake tunawa ba illa ita. Tirkashi! Yanzu ya zaiyi? Haka yake tunanin yadda zaiyi over coming problem ɗinsa.
Ya yanke shawarar yaje ya sameta saboda zuciyarsa yana mashi barazana bugawa idan bai samu abinda yake so ba.
Bayan Isha ya tafi gidan gona, a bakin gate Mai gadi ya faɗa mashi cewa ta tafi gidansu. Dayake ya taba kai Miemie gidan sanda take raye so bai wahala ba.
Ya aika ayi mashi iso da ita, shikuma yana zaune cikin motarsa yana addu’a saboda gabansa yanata faɗi na rashin dalili. Ita kuma tana kwance akan gado ta gama rubuta wani proposal haka.
Whatsapp ta shiga tana ɗan karance karance littafin hausa mai suna “A Dalilin Mene” wanda UmmieeJafar ta rubuta. Maigadi yayi sallama wai ana nemanta a bakin kofa.
Koda ta tambaya wanene yace gaskiya cikin dare ne kuma baiga fuskarshi ba,saidai ya ce ai mashi iso da Abla. Dayake ta riga tayi shirin kwanciya, saita daura dogon riga da kuma Hijab wanda ya wuce gwiwanta da kadan.
Sallama tayi data isa wajen motarsa, ya fito yana jingine. Saida ya amsa ta gane Khattab. Nan taji gabanta ya faɗi saboda idan abinda take tunani yake so yayi zata tsayar dashi tun kafin komai yayi nisa.
Na farko dai ita ba Miemie bace, saboda haka babu gurbin dazata maye mashi. Bayan sunyi gaisuwa sai sukayi shuru na kusan minti biyar , kana ganinsu kasan akwai tension tsakanin su.
Kawai nazarinta yakey, tabbas wannan ba Miemie bace, koh ɗabi’un su ya bambanta sosai. Miemie bazata taɓa ganinsa tayi shiru ba, saidai kuma Miemie tana sanshi, wannan babu wani abu datake ji mashi a ranta.
Haka suka gama tsayuwa ya kasa cewa komai sai kawai yayi mata sallama ya tafi. Itama sallama tayi ta wuce cikin ɗaki.
Abla irin matan nanne masu kwarjini da ba kasafai zaka iya gaya masu aininhin abinda ke ranka ba. Ita ma taji dadi bai kawo mata wani shirmeba.
Bawai tanada wani tsayayye bane amma bata tunanin zata iya soyayya dashi, ita tana ganin cin amana ne wajen mai rasuwa Miemie.Babu abinda bata sani na Khattab daga abincinsa, kayansa, colors da sauran abinda ya dace wani ya sani akan ka. Miemie idan ta dawo daga taɗi takan bata labarin shi sosai.
So wannan amanar yasa bazata iya betraying trust ɗinta ba even in death. Kawai Khattab ya dauki na damu ya nema wata chan daban.
Shikuma yanzu duk bayan kwana biyu sai yaje dubata, sometimes ya kanyi siyayya ya kai mata. Bai taɓa faɗa mata dalilinsa na zuwa ba, asalima basa hira daga gaisuwa sai bayan wajen 20mins haka ko 30 sai ya tafi shikenan kuma sai gobe ko jibi. Infact ko number dinta bashida shi itama haka batada nasa.
Duk sanda ya zo ya tafi abu ɗaya take faɗi a ranta, ‘Iska na wahalar da me kayan kara”
Shikuma yasan cewa every disappointment is a blessing in disguise, baisan abinda zai faru nan gaba but he is optimistic about everything. Yasan cewa Allah baya baka abinda bazaka iya handling ba.
Komai rabo ne da kuma lokaci, idan babu rabonka a cikin abu duk yanda kaso bazaka samu ba, dama zabin Allah yake nema a koda yaushe.
#NiDaDiyata
_Yarinya Mai DIMPLΣS_©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 38 ✨✨✨
Abu Hurairah (May Allah be pleased with him) reported: The Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "There are two statements that are light for the tongue to remember, heavy in the Scales and are dear to the Merciful: 'Subhan-Allahi wa bihamdihi, Subhan-Allahil-Azim [Glory be to Allah and His is the praise, (and) Allah, the Greatest is free from imperfection]'."[Al-Bukhari and Muslim].
********
Wani Laraba haka wajen sha biyun rana, ina zaune cikin Office dina saiga Sadeeq ya shigo. Bayan munyi sallama sai yayi min korafin yunwa.
Nan take gabana ya faɗi saboda gidana ba inda za’a kai bako bane, Aminu shima ya shigo wai a dole sai sunje gidana cin abinci. Babu noke noke da banyi ba amma sukayi burus dani.
Haka na tashi ina Hasbunallahu wa ni’imal wakeel inatayi har muka kai gidana. A parking lot mukaga Motar Huzaifa, nan jikina yayi la’asar. Yanzu Huzaifa bashida timetable na zuwa gidana, baisan safe balle rana. Koda yaushe zuwa yakeyi.
Su kuma su Huzaifa da Yasmeenah sun zama besty 5 and 6. Suna jin daɗin company ɗin junarsu. Babu tashin hankali da batayi dani akan abin kuma na nuna mata bacin raina amma tayi kunnen uwar shegu.
Suna zaune a falo suna kallon sabon India mai suna ‘Dilwale’ wanda Kajol da Sharukhan sukayi acting. An kai wajen wani waka haka sai Yasmeenah tayi rewinding ɗinsa daga farko. Toh dama laptop din Huzaifa suke kallo dashi.
Nan ta soma babbaka rawa, su crip walking takeyi saita haɗa da azonto daga nan sai tayi ending dinshi da dab.
Su kuma su Naufal ana cikin tafiya akaji karar waka, nan take raina ya ɓaci. Gashi kuma nazo da baki. Yau tabbas sai na ji kunya. Dama duk wanda baiji bari yaji hoho!
Fatana ɗaya kada na risketa tana zabga rawa tunda karamin aikinta ne. Aikuwa kaddara ta riga fata saboda babbaka rawa take yi abinta. Sororo muka tsaya bakin kofa muna kallonta.
Huzaifa yana daga kwance ya hakince a 3 seater kai zaka ranste shine mijinta. Amshi yake mata “Go Meenah! Go Meenah!! Go go go Meenah !!!” ita kuma sai dancewa take yi. Dariya ya bushe dashi sannan ya naushi iska tareda tafa hannayensa sai yace “Tirrrrrr yarinyar nan bakida dama wallahi”
Itama dariya tayi saita juya ta ganni tsaye bakin kofa da baki. Da gudu tazo inda nake ta sumbace bakina babu kunyar mutanen dake wajen.
“Mine ka bani mamaki bansan yanzu zaka dawo ba”
“Nida gidana saina tambaya izininki kafin na shigo?”
“No bahaka bane im not expecting you, at least ko waya da kayi min amma bawai kawai ka fado min ba without a warning” ban kulata ba saboda ina dab da marin ta, karyan iskanci takeyi nazo na iske ta tana rawa gaban wannan gwaskar shine zata wayanace.
Sai kuma ta juya ta gaida su Aminu kana tayi introducing Huzaifa as Big bro dinta.
Shikuma Huzaifa ya mika masu hannu suka gaisa, nidai ban mika masa ba saboda na tsane shi. Da baki muka gaisa saiya tafi, har yakai bakin kofa saiya juyo yace, “Lil sis gobe da safe zanzo na karɓa laptop dina saboda munada board meeting”
“okay Yaya Huzzy dont worry yau ba zanyi barci ba zan kwana ina kallo har saina gama”Daga gira yayi daga nan sai ya tafi. Ni yanda yake behaving ban taba zaton yana anything for a living ba saboda baya zuwa aiki at all, kullum yana gidana. Wata rana har Saturday and Sunday.
Shigowa falon muka yi gashi kacha kacha babu gyara, su ledan Oasis ne birjik dasu gwangwani na maltina da pepsi wanda aka sha aka rage. Ga kuma burbushin cake daga kan kujera har kasan carpet.
Da sauri taje ta fara tattara wa, gashi rigar ta doguwa ce amma ya matseta tsam. Duk wani haushi da kunya ya kamani kawai bance komai ba. Itace ta fara magana, “Please kuyi hakuri dama inaso na gama kallo ne tukun kafin nayi shara”
“Karki damu amarya lantarkin gida, ai bakya lefi koda kin kashe dan masu gida” Aminu yace yana kallon fuskar Naufal. Ni kuma haɗa rai nayi saboda nasan iskanci yake min.
Wucewa tayi ta dauko ragowar cake dasu shawarma ta kawo mana, nidai banci ba saboda yadda na tsane Huzaifa bana iya cin abinda ya kawo. Su dai su Sadeeq sunci.
Ta kwashe tarkacen da zata iya tsincewa saita ce, “Kuyi hakuri banyi abinci ba, yanzu sharp sharp zan maku taliya”
“Au bama ki daura ba kenan?” Aminu yace yana dariya.
“Wallahi kuwa, nifa house chores is not my calling, i really hate it... Kawai saboda ina san Mine ne yasa nakeyi”
“Toh fah!” Aminu yace
“Mazaaa kaji ance saboda ana sanka ne ake yi a haka” Sadeeq yace.
Ni kawai ban kula suba banda chanza channel zuwa Aljazeera na soma kallon labarai.
Wucewa tayi kitchen domin ta daura sanwa, wanke wanke ne shake a wajen. Gashi batazo da Dish washer ɗinta saboda kitchen dinta is too small. Wasu daga cikin sun fara yauki saboda tun na jiya dana shekaranjiya ne.
Haka ta matsar da wanda zata iya saita dauraye tukunya ɗaya. Saita daura ruwa akan gas, manja ta saka bata ko soya ba saita saka tomato paste. Bata saka albasa ba saboda bata so hannunta yayi wari sai kuma ta zambada barkono.
Dauko kifi tayi daga fridge mai kankara, dayake akwai sanyi dayawa, da kyar ta wanke. Ko scales din bata cire ba, haka kashin dake ciki ba duka suka samu daman fita ba.
Cikin ruwan dake tafasa ta tsumbula saita saka spaghetti ɗaya ma gardawa uku. Maggi kuwa ta saka kusan goma ma taliya leda daya.
Babu kamshin dake tashi bazaka zata ana girki cikin gidan ba, ko su Naufal mamaki sukeyi har yanzu bata daura ba saiga abinci a cooler ta fito dashi.
Ta ajiye masu akan dinning table saita koma ta cigaba da kallonta. Ta hada masu Ginger drink mai dan karan zafi, Aminu yana sakawa a baki saida ya fito dashi. Hawaye ya soma gangaro masa saboda zafin dayaji.
Sun buɗe cikin cooler sai sukaga taliya kitub ya chabe, gashi mai isheshi ba. Kawai addu’a sukayi kada yayi rashin daɗi. Sun zuba ma kansu amma bazai ishesu ba saidai managing.
Naufal ya fara kaiwa baki, zare ido yayi saiya toshe bakinsa da hannunsa. Da sauri ya dauki zuwa yakai baki tunda bazai iya shan ginger dinba. Tauna yakeyi amma abincin yaki wucewa, saida ya sake korawa da ruwa tukun.
Saida ya ganta ya lura ba Miemie yake tunawa ba illa ita. Tirkashi! Yanzu ya zaiyi? Haka yake tunanin yadda zaiyi over coming problem ɗinsa.
Ya yanke shawarar yaje ya sameta saboda zuciyarsa yana mashi barazana bugawa idan bai samu abinda yake so ba.
Bayan Isha ya tafi gidan gona, a bakin gate Mai gadi ya faɗa mashi cewa ta tafi gidansu. Dayake ya taba kai Miemie gidan sanda take raye so bai wahala ba.
Ya aika ayi mashi iso da ita, shikuma yana zaune cikin motarsa yana addu’a saboda gabansa yanata faɗi na rashin dalili. Ita kuma tana kwance akan gado ta gama rubuta wani proposal haka.
Whatsapp ta shiga tana ɗan karance karance littafin hausa mai suna “A Dalilin Mene” wanda UmmieeJafar ta rubuta. Maigadi yayi sallama wai ana nemanta a bakin kofa.
Koda ta tambaya wanene yace gaskiya cikin dare ne kuma baiga fuskarshi ba,saidai ya ce ai mashi iso da Abla. Dayake ta riga tayi shirin kwanciya, saita daura dogon riga da kuma Hijab wanda ya wuce gwiwanta da kadan.
Sallama tayi data isa wajen motarsa, ya fito yana jingine. Saida ya amsa ta gane Khattab. Nan taji gabanta ya faɗi saboda idan abinda take tunani yake so yayi zata tsayar dashi tun kafin komai yayi nisa.
Na farko dai ita ba Miemie bace, saboda haka babu gurbin dazata maye mashi. Bayan sunyi gaisuwa sai sukayi shuru na kusan minti biyar , kana ganinsu kasan akwai tension tsakanin su.
Kawai nazarinta yakey, tabbas wannan ba Miemie bace, koh ɗabi’un su ya bambanta sosai. Miemie bazata taɓa ganinsa tayi shiru ba, saidai kuma Miemie tana sanshi, wannan babu wani abu datake ji mashi a ranta.
Haka suka gama tsayuwa ya kasa cewa komai sai kawai yayi mata sallama ya tafi. Itama sallama tayi ta wuce cikin ɗaki.
Abla irin matan nanne masu kwarjini da ba kasafai zaka iya gaya masu aininhin abinda ke ranka ba. Ita ma taji dadi bai kawo mata wani shirmeba.
Bawai tanada wani tsayayye bane amma bata tunanin zata iya soyayya dashi, ita tana ganin cin amana ne wajen mai rasuwa Miemie.Babu abinda bata sani na Khattab daga abincinsa, kayansa, colors da sauran abinda ya dace wani ya sani akan ka. Miemie idan ta dawo daga taɗi takan bata labarin shi sosai.
So wannan amanar yasa bazata iya betraying trust ɗinta ba even in death. Kawai Khattab ya dauki na damu ya nema wata chan daban.
Shikuma yanzu duk bayan kwana biyu sai yaje dubata, sometimes ya kanyi siyayya ya kai mata. Bai taɓa faɗa mata dalilinsa na zuwa ba, asalima basa hira daga gaisuwa sai bayan wajen 20mins haka ko 30 sai ya tafi shikenan kuma sai gobe ko jibi. Infact ko number dinta bashida shi itama haka batada nasa.
Duk sanda ya zo ya tafi abu ɗaya take faɗi a ranta, ‘Iska na wahalar da me kayan kara”
Shikuma yasan cewa every disappointment is a blessing in disguise, baisan abinda zai faru nan gaba but he is optimistic about everything. Yasan cewa Allah baya baka abinda bazaka iya handling ba.
Komai rabo ne da kuma lokaci, idan babu rabonka a cikin abu duk yanda kaso bazaka samu ba, dama zabin Allah yake nema a koda yaushe.
#NiDaDiyata
_Yarinya Mai DIMPLΣS_©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 38 ✨✨✨
Abu Hurairah (May Allah be pleased with him) reported: The Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "There are two statements that are light for the tongue to remember, heavy in the Scales and are dear to the Merciful: 'Subhan-Allahi wa bihamdihi, Subhan-Allahil-Azim [Glory be to Allah and His is the praise, (and) Allah, the Greatest is free from imperfection]'."[Al-Bukhari and Muslim].
********
Wani Laraba haka wajen sha biyun rana, ina zaune cikin Office dina saiga Sadeeq ya shigo. Bayan munyi sallama sai yayi min korafin yunwa.
Nan take gabana ya faɗi saboda gidana ba inda za’a kai bako bane, Aminu shima ya shigo wai a dole sai sunje gidana cin abinci. Babu noke noke da banyi ba amma sukayi burus dani.
Haka na tashi ina Hasbunallahu wa ni’imal wakeel inatayi har muka kai gidana. A parking lot mukaga Motar Huzaifa, nan jikina yayi la’asar. Yanzu Huzaifa bashida timetable na zuwa gidana, baisan safe balle rana. Koda yaushe zuwa yakeyi.
Su kuma su Huzaifa da Yasmeenah sun zama besty 5 and 6. Suna jin daɗin company ɗin junarsu. Babu tashin hankali da batayi dani akan abin kuma na nuna mata bacin raina amma tayi kunnen uwar shegu.
Suna zaune a falo suna kallon sabon India mai suna ‘Dilwale’ wanda Kajol da Sharukhan sukayi acting. An kai wajen wani waka haka sai Yasmeenah tayi rewinding ɗinsa daga farko. Toh dama laptop din Huzaifa suke kallo dashi.
Nan ta soma babbaka rawa, su crip walking takeyi saita haɗa da azonto daga nan sai tayi ending dinshi da dab.
Su kuma su Naufal ana cikin tafiya akaji karar waka, nan take raina ya ɓaci. Gashi kuma nazo da baki. Yau tabbas sai na ji kunya. Dama duk wanda baiji bari yaji hoho!
Fatana ɗaya kada na risketa tana zabga rawa tunda karamin aikinta ne. Aikuwa kaddara ta riga fata saboda babbaka rawa take yi abinta. Sororo muka tsaya bakin kofa muna kallonta.
Huzaifa yana daga kwance ya hakince a 3 seater kai zaka ranste shine mijinta. Amshi yake mata “Go Meenah! Go Meenah!! Go go go Meenah !!!” ita kuma sai dancewa take yi. Dariya ya bushe dashi sannan ya naushi iska tareda tafa hannayensa sai yace “Tirrrrrr yarinyar nan bakida dama wallahi”
Itama dariya tayi saita juya ta ganni tsaye bakin kofa da baki. Da gudu tazo inda nake ta sumbace bakina babu kunyar mutanen dake wajen.
“Mine ka bani mamaki bansan yanzu zaka dawo ba”
“Nida gidana saina tambaya izininki kafin na shigo?”
“No bahaka bane im not expecting you, at least ko waya da kayi min amma bawai kawai ka fado min ba without a warning” ban kulata ba saboda ina dab da marin ta, karyan iskanci takeyi nazo na iske ta tana rawa gaban wannan gwaskar shine zata wayanace.
Sai kuma ta juya ta gaida su Aminu kana tayi introducing Huzaifa as Big bro dinta.
Shikuma Huzaifa ya mika masu hannu suka gaisa, nidai ban mika masa ba saboda na tsane shi. Da baki muka gaisa saiya tafi, har yakai bakin kofa saiya juyo yace, “Lil sis gobe da safe zanzo na karɓa laptop dina saboda munada board meeting”
“okay Yaya Huzzy dont worry yau ba zanyi barci ba zan kwana ina kallo har saina gama”Daga gira yayi daga nan sai ya tafi. Ni yanda yake behaving ban taba zaton yana anything for a living ba saboda baya zuwa aiki at all, kullum yana gidana. Wata rana har Saturday and Sunday.
Shigowa falon muka yi gashi kacha kacha babu gyara, su ledan Oasis ne birjik dasu gwangwani na maltina da pepsi wanda aka sha aka rage. Ga kuma burbushin cake daga kan kujera har kasan carpet.
Da sauri taje ta fara tattara wa, gashi rigar ta doguwa ce amma ya matseta tsam. Duk wani haushi da kunya ya kamani kawai bance komai ba. Itace ta fara magana, “Please kuyi hakuri dama inaso na gama kallo ne tukun kafin nayi shara”
“Karki damu amarya lantarkin gida, ai bakya lefi koda kin kashe dan masu gida” Aminu yace yana kallon fuskar Naufal. Ni kuma haɗa rai nayi saboda nasan iskanci yake min.
Wucewa tayi ta dauko ragowar cake dasu shawarma ta kawo mana, nidai banci ba saboda yadda na tsane Huzaifa bana iya cin abinda ya kawo. Su dai su Sadeeq sunci.
Ta kwashe tarkacen da zata iya tsincewa saita ce, “Kuyi hakuri banyi abinci ba, yanzu sharp sharp zan maku taliya”
“Au bama ki daura ba kenan?” Aminu yace yana dariya.
“Wallahi kuwa, nifa house chores is not my calling, i really hate it... Kawai saboda ina san Mine ne yasa nakeyi”
“Toh fah!” Aminu yace
“Mazaaa kaji ance saboda ana sanka ne ake yi a haka” Sadeeq yace.
Ni kawai ban kula suba banda chanza channel zuwa Aljazeera na soma kallon labarai.
Wucewa tayi kitchen domin ta daura sanwa, wanke wanke ne shake a wajen. Gashi batazo da Dish washer ɗinta saboda kitchen dinta is too small. Wasu daga cikin sun fara yauki saboda tun na jiya dana shekaranjiya ne.
Haka ta matsar da wanda zata iya saita dauraye tukunya ɗaya. Saita daura ruwa akan gas, manja ta saka bata ko soya ba saita saka tomato paste. Bata saka albasa ba saboda bata so hannunta yayi wari sai kuma ta zambada barkono.
Dauko kifi tayi daga fridge mai kankara, dayake akwai sanyi dayawa, da kyar ta wanke. Ko scales din bata cire ba, haka kashin dake ciki ba duka suka samu daman fita ba.
Cikin ruwan dake tafasa ta tsumbula saita saka spaghetti ɗaya ma gardawa uku. Maggi kuwa ta saka kusan goma ma taliya leda daya.
Babu kamshin dake tashi bazaka zata ana girki cikin gidan ba, ko su Naufal mamaki sukeyi har yanzu bata daura ba saiga abinci a cooler ta fito dashi.
Ta ajiye masu akan dinning table saita koma ta cigaba da kallonta. Ta hada masu Ginger drink mai dan karan zafi, Aminu yana sakawa a baki saida ya fito dashi. Hawaye ya soma gangaro masa saboda zafin dayaji.
Sun buɗe cikin cooler sai sukaga taliya kitub ya chabe, gashi mai isheshi ba. Kawai addu’a sukayi kada yayi rashin daɗi. Sun zuba ma kansu amma bazai ishesu ba saidai managing.
Naufal ya fara kaiwa baki, zare ido yayi saiya toshe bakinsa da hannunsa. Da sauri ya dauki zuwa yakai baki tunda bazai iya shan ginger dinba. Tauna yakeyi amma abincin yaki wucewa, saida ya sake korawa da ruwa tukun.