Sashe 39
Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ta soma magana, “Shikenan an tafi da ita, na shiga uku na lalace” tana kuka sosai wannan karon kamar ranta zai fita daga jikinta.
Lokacin yayi daidai da fitowan wani doctor, da sauri suka tashi kowa yana so yaji me ake ciki. Shikuma Dr din baice komai ba zai ratsa su ya wuce.
Khattab ne finkico shi yana masa masifa “Meye haka Doctor kana ganin mu tsaye zaka wani ratsa mu ka wuce”
“Mallam sakeni mana” Doctor yace
“Basan sake ba ɗin, dan rainin wayo” ya amsa
Naufal ne ya shiga tsakanin su, shima yaji haushin abinda Dr din yayi kuma yaji daɗin yadda Khattab ya saisaita shi. Kawai baya jin daɗin jikinsa ne da sai yayi ma Doctor ɗin dukan tsiya.
Doctor ɗin ya soma tafiya abinsa tareda nuna Khattab da yatsa yana hararar shi, Mommy tayi magana daga zaune.
“Doctor Haba mana ya zaka wuce mu baka ce mana komai ba”
“Kiyi hakuri Mama, jini zani store in dauko” saiya tafi.
Yaje ya dauko zai shiga ciki sai Naufal ya tambayeshi “Doctor please ta farfardo kuwa?”
“Kuyi hakuri shi muke kokarin yi” nan take Khattab ya fashe da kuka, wai ace kusan awanta uku a ciki amma an kasa tada ta. Shima baya maso ya kawo wani mugun tunani waiko bazata farka ba.
Daddyn shine ya shigo tareda Grand Kadi da sauran jama’a. “Meye haka kake yi kamar mara tawakkali? Maimakon kayi mata addu’a” Daddyn shi ya faɗa.
Mikewa yayi ya tafi kurya inda yake kukanshi babu mai kwaɓansa.
9:30 pm......
Locacin wasu Doctors su huɗu suka fito duk suna zufa, ga kuma leberori suma suna fitowa da Miemie akan gadon da ake turawa.
Da sauri yan uwan Miemie sukayi wajen ta, kana ganinta saita baka tausayi matuka. Duk bandage a jikinta manya manya, daga fuskanta, cikinta haɗe da bayanta, kafar dama da kuma hannun damanta.
Ga wani an zagaye goshinta dashi, sannan an saka mata Oxygen domin shakar numfashi. Da sauri suka rinka bin gadon dakin da aka ware masu.
Daga nan wani Doctor mai suna Abdullahi ya soma magana, “Bincike ya nuna cewa ba bigewa tayi ba, an buga mata kanta da sledgehammer ne. Kafin wutan ya soma ci”
Salati kowa ya somayi, masu matse kwalla kuma kamar su Fadeela da Anty suka soma. Kowa Mamaki yakeyi wai da gangan akaso kashe Miemie. Dr ne ya cigaba magana.
“Munyi kokari munga munyi stabilizing ɗinta amma gaskiyar magana shine sai anyi addu’a saboda har yanzu jini yana fitowa daga cikin kanta kadan kadan”
“Kuma hayaki yayi yawa a cikin lungs ɗinta, yanzu dai idonta biyu kuma tana jinku. Amma bansan ko zata iya magana ba ko buɗe idonta”
Daga nan sai Naufal ya tambaya asalin meya faru, Fadeela ta labarta masu komai daga zuwan su Yasmeenah har batan Pha’eexah da kuma konewan Miemie.
Kuka takeyi sosai saboda tana tunanin yau zata rasa mutane biyu da sukeda mahimmanci a rayuwarta. Duk juriyar da Khattab yake kokarin Nunawa saida wani hawaye na takaici ya gangaro daga idanunsa.
Shiko Naufal abin duniya yayi masa chunkoso, ‘yarsa ta ɓace ga kuma k’anwarsa rai yana hannun Allah. Zuciyar shi sai zafi yakeyi yana tafasa, shiko kuka ya samu yayi ko zaiji sanyi amma ya kasa.
Idanunsa a kafe sai zallan ɓacin rai dake bayyana, tausayin kowa yake a wajen musamman wanda abin yafi shafa kamar Khattab, Anty da kuma Fadeela.
Doctor yace su Abba su biyoshi office zai masu magana, duk sun watse sai Khattab yaje inda Miemie ke kwance.
Rike mata hannu yayi yana rero kuka, ko ajikinsa baya jin kunyarsu Anty ko Deela. Baice komai ba haka ya kafa ma fuskanta da baka ganin komai daga bandage da Oxygen.
Saida yayi ma’ishi sai ya fara magana still hawaye yana malalo mashi daga idanu. Abinda yasa yaketa kuka baifi yadda yau da rana Miemie ke masa maganar mutuwa.
“Yaya Khattab idan na mutu ya zakayi?” “Miemie meye haka?” “Please just answer me” “Bazaki mutu ba sai munyi aure kin haifan min yara masu kalan ‘yan gidan ku” dariya tayi kafin tace “You never know......”
Kuka ya sakeyi sosai daya tuna abinda ya wakana tsakanin shida Miemie da azahar dazu. Cikin kuka yace, “Please Haskena ki tashi karki mutu. Nasan anso a kasheki ne amma ina so ki basu kunya by staying alive”
“Kuma i promise you duk wanda yayi ɗanyen aikin nan za’a kamashi duk inda yake.....” saiya cigaba da kuka.
Rike mata hannu yayi yana matsawa a hankali, itama ta rike masa hannu amma idanun ta a rufe. Suna cikin haka sai su Naufal da Abba suka dawo.
Yanda suka ga Khattab jaɓe jaɓe da hawaye gwanin ban tausayi, ita Anty tana tausayin shi saboda yama fita damuwa.
“Meye haka kake kuka? Wayace maka mutuwa zatayi?” Naufal ya faɗa a takaice. Mikewa Khattab yayi yana jan manjina saiya bar ɗakin gaba daya.
Motarsa ya koma kai tsaye, sai a lokacin ya lura baima kulle ba. Kifa kai yayi akan steering yana sheshek’ar kuka.
Itakuma Deela zuwa tayi tana shafa mata goshinta wanda akwai bandage akai, hawaye itama takeyi saita soma magana da dishenshen muryanta.
“Please Miemie ki tashi kinji, kinga an tafi da little one. Im sure zaki san wanda yayi wannan abun....” kuka ta barke dashi mai kara, su Mommy da Anty sunata matse kwalla saboda tausayin Deela.
Tabbas zata shiga wani yanayi idan ta rasa Miemie kuma bayan ta rasa ‘yarta. Ciwon Miemie yanzu ya hanata kukan rashin yarta.
Naufal ne ya janyo Kujera ya zauna dab da ita, bubbuga mata baya yayi ya kwantar da ita akan kafaɗarsa.
“Kiyi hakuri kinji, in sha Allah komai zai daidaita”
“Allah yasa” ta amsa.
Suna haka kowa yana addu’a a ranshi. Abba ne yace masu Fadeela su tafi da Anty. Akwai nurses da aka ware zasu rinka dubata kafin gari ya waye.
Kuka Deela ta barke dashi wai baza’a bar Miemie ta kwana ita kadai da bare ba. Hakuri aka rinka bata amma taki shiru. Naufal ne yace zaije ya dauko Abla ta kwana da ita.
Anan ta rage kukanta sai tace yaje ya dawo zata zauna da ita tukun kafin yazo ya mayar da ita gida idan an dauko Abla ɗin. Kowa ya tafi tareda mata addu’a.
Naufal ya tafi ya dauko Abla, yana parking lot dasu Anty da Abba za’a tafi sai suka ga Khattab cikin motarsa yana kuka. Tadashi aka yi ya tafi gida sai yace ba yanzu ba tukun.
Abba ne yace ya shiga ciki ya zauna kafin Naufal yaje ya dawo saiya tafi. Shiga yayi ciki jiki babu kwari duk ya gaji. Ga wani matsananci ciwon kai da kuka da haifar masa.
Zuwa yayi cikin ɗakin saiya tarar da Deela ta shingiɗa, zama daga chan bakin kofa amma ta ciki. Tagumi yayi saiya soma gyangyaɗi saboda gajiya.
Itama barci yana daukarta amma tana buɗe idonta ta. Suna cikin haka sai barci ya dauke su duka. Basu suka farka ba sai sanda Naufal ya dawo da Abla.
“Ya akayi wanchan abin ya daina motsi? Naufal ne ya tambaya sanda ya shigo kana ya nufa hanyar ECG da aka haɗa da jikin Miemie.
A firgice suka tashi, Deela tana mitsike ido Shikuma Khattab ya zura da gudu wajen gadon. Saka kunnen shi akan kirjinta yayi amma baya jin alamun bugun zuciya.
“Why is she not breathing?” Deela ta faɗa hankali a tashe.
Da sauri ya mayar da kunnen sa wajen hanncinta tareda cire Oxygen tube ko zaiji alamun shakar numfashi amma wayam.
Innalillahi wa inna ilayhi rajiun ra rinka maimaitawa yana yi yana jijigata amma bata motsa ba, asalima jikinta a kankame.
Fadeela ce ta tsandara ihu saita sulale kasa, da sauri Naufal ya tarbota. Bata hakuri ya somayi yace kila wani abune daban.
Ko ba’a faɗa mashi ba yasan Miemie ta koma gidanta na gaskiya. The worst part shine an kasheta ne bawai hakanan bane, tunanin sa ɗaya how can someone be this cruel?
Abla zuwa tayi ta rungume Deela sunata kuka tare, Fadeela ne ke magana cikin kuka a hankali, “Innalillahi wa inna ilayhi rajiun, shikenan Miemie ta tafi barmu”
Shikuma Khattab gefe yake ya zauna a kasa zaman dirshan, kwakwalwarsa sai tafasa yakeyi. Shi tunda yaji labarin accident ɗin yasan za’a yi haka.
Yau gaba ɗaya sai maganar mutuwa takeyi da kuma rok’on sa gafara. Har haushi yaji yayi mata magana, ce masa tayi “you never know when you’ll die, gwara ka shirya kafin lokacin ka”
Duk kalamanta yanzu yawo yake masa a kai, saidai yanzu Idonshi ya kafe. Yama kasa kuka, salati kawai yake cikin ransa. Kirjinsa zafi yakeyi ga gudu da sauri kamar zai fashe.
Ji yayi kamar an daura mashi katon dutse cikin kirjinsa, ga kuma miyau na bakinsa ya kafe k'ab. Karkarwa kawai yakeyi kamar yana jin sanyi.
Shikuma Naufal komawa yayi bakin Varenda yayi tagumi, abin daure masa kai yayi wai dazu ya ganta yanzu kuma ta rasu. Daukar wayarsa yayi domin ya kira ABBA.
“Assalamu Alaikum, ya akayi ne Naufal” Abba yace ta ɗayan ɓangaren. Naufal bai iya amsa sallamar ba, kawai magana ya soma.
“Abba shikenan Miemie ta tafi ta barmu. Abba Miemie ta rasu, ta koma gidanta na gaskiya”
“Innalillahi wa inna ilayhi rajiun” abinda Abba ya iya faɗi kenan.
Shikuma Naufal wasu zafafan hawaye suka soma gangarowa daga idanunsa, da farko kadan kadan sai kuma suka fara gudu.
#NiDaDiyata
~Yarinya Mai DIMPLΣS~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 35 ✨✨✨
'Imran bin Husain (May Allah be pleased with them) reported: Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "Shyness does not bring anything except good."[Al-Bukhari and Muslim].In a narration of Muslim: Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "All of shyness is good."
***********
Kullu Nafsin Za’katul maut. Valar Morghulis. Kowane mai rai mamaci ne, sai dai zamuyi fatan mu cika da kyau da imani.
Fadeela da Abla suna cikin ɗakin suna hawaye, jiki babu kwari Abla ta mik’e tsaye taje inda gadon yake ta rufe mata jiki da mayafi.
Mamakin mutuwar Miemie takeyi, abin yayi mata zuwan ba zata. Addu’a yanzu kawai zata ya Allah yakai haske kabarinta, ya kuma basu hakurin jure rashinta.
Lokacin yayi daidai da fitowan wani doctor, da sauri suka tashi kowa yana so yaji me ake ciki. Shikuma Dr din baice komai ba zai ratsa su ya wuce.
Khattab ne finkico shi yana masa masifa “Meye haka Doctor kana ganin mu tsaye zaka wani ratsa mu ka wuce”
“Mallam sakeni mana” Doctor yace
“Basan sake ba ɗin, dan rainin wayo” ya amsa
Naufal ne ya shiga tsakanin su, shima yaji haushin abinda Dr din yayi kuma yaji daɗin yadda Khattab ya saisaita shi. Kawai baya jin daɗin jikinsa ne da sai yayi ma Doctor ɗin dukan tsiya.
Doctor ɗin ya soma tafiya abinsa tareda nuna Khattab da yatsa yana hararar shi, Mommy tayi magana daga zaune.
“Doctor Haba mana ya zaka wuce mu baka ce mana komai ba”
“Kiyi hakuri Mama, jini zani store in dauko” saiya tafi.
Yaje ya dauko zai shiga ciki sai Naufal ya tambayeshi “Doctor please ta farfardo kuwa?”
“Kuyi hakuri shi muke kokarin yi” nan take Khattab ya fashe da kuka, wai ace kusan awanta uku a ciki amma an kasa tada ta. Shima baya maso ya kawo wani mugun tunani waiko bazata farka ba.
Daddyn shine ya shigo tareda Grand Kadi da sauran jama’a. “Meye haka kake yi kamar mara tawakkali? Maimakon kayi mata addu’a” Daddyn shi ya faɗa.
Mikewa yayi ya tafi kurya inda yake kukanshi babu mai kwaɓansa.
9:30 pm......
Locacin wasu Doctors su huɗu suka fito duk suna zufa, ga kuma leberori suma suna fitowa da Miemie akan gadon da ake turawa.
Da sauri yan uwan Miemie sukayi wajen ta, kana ganinta saita baka tausayi matuka. Duk bandage a jikinta manya manya, daga fuskanta, cikinta haɗe da bayanta, kafar dama da kuma hannun damanta.
Ga wani an zagaye goshinta dashi, sannan an saka mata Oxygen domin shakar numfashi. Da sauri suka rinka bin gadon dakin da aka ware masu.
Daga nan wani Doctor mai suna Abdullahi ya soma magana, “Bincike ya nuna cewa ba bigewa tayi ba, an buga mata kanta da sledgehammer ne. Kafin wutan ya soma ci”
Salati kowa ya somayi, masu matse kwalla kuma kamar su Fadeela da Anty suka soma. Kowa Mamaki yakeyi wai da gangan akaso kashe Miemie. Dr ne ya cigaba magana.
“Munyi kokari munga munyi stabilizing ɗinta amma gaskiyar magana shine sai anyi addu’a saboda har yanzu jini yana fitowa daga cikin kanta kadan kadan”
“Kuma hayaki yayi yawa a cikin lungs ɗinta, yanzu dai idonta biyu kuma tana jinku. Amma bansan ko zata iya magana ba ko buɗe idonta”
Daga nan sai Naufal ya tambaya asalin meya faru, Fadeela ta labarta masu komai daga zuwan su Yasmeenah har batan Pha’eexah da kuma konewan Miemie.
Kuka takeyi sosai saboda tana tunanin yau zata rasa mutane biyu da sukeda mahimmanci a rayuwarta. Duk juriyar da Khattab yake kokarin Nunawa saida wani hawaye na takaici ya gangaro daga idanunsa.
Shiko Naufal abin duniya yayi masa chunkoso, ‘yarsa ta ɓace ga kuma k’anwarsa rai yana hannun Allah. Zuciyar shi sai zafi yakeyi yana tafasa, shiko kuka ya samu yayi ko zaiji sanyi amma ya kasa.
Idanunsa a kafe sai zallan ɓacin rai dake bayyana, tausayin kowa yake a wajen musamman wanda abin yafi shafa kamar Khattab, Anty da kuma Fadeela.
Doctor yace su Abba su biyoshi office zai masu magana, duk sun watse sai Khattab yaje inda Miemie ke kwance.
Rike mata hannu yayi yana rero kuka, ko ajikinsa baya jin kunyarsu Anty ko Deela. Baice komai ba haka ya kafa ma fuskanta da baka ganin komai daga bandage da Oxygen.
Saida yayi ma’ishi sai ya fara magana still hawaye yana malalo mashi daga idanu. Abinda yasa yaketa kuka baifi yadda yau da rana Miemie ke masa maganar mutuwa.
“Yaya Khattab idan na mutu ya zakayi?” “Miemie meye haka?” “Please just answer me” “Bazaki mutu ba sai munyi aure kin haifan min yara masu kalan ‘yan gidan ku” dariya tayi kafin tace “You never know......”
Kuka ya sakeyi sosai daya tuna abinda ya wakana tsakanin shida Miemie da azahar dazu. Cikin kuka yace, “Please Haskena ki tashi karki mutu. Nasan anso a kasheki ne amma ina so ki basu kunya by staying alive”
“Kuma i promise you duk wanda yayi ɗanyen aikin nan za’a kamashi duk inda yake.....” saiya cigaba da kuka.
Rike mata hannu yayi yana matsawa a hankali, itama ta rike masa hannu amma idanun ta a rufe. Suna cikin haka sai su Naufal da Abba suka dawo.
Yanda suka ga Khattab jaɓe jaɓe da hawaye gwanin ban tausayi, ita Anty tana tausayin shi saboda yama fita damuwa.
“Meye haka kake kuka? Wayace maka mutuwa zatayi?” Naufal ya faɗa a takaice. Mikewa Khattab yayi yana jan manjina saiya bar ɗakin gaba daya.
Motarsa ya koma kai tsaye, sai a lokacin ya lura baima kulle ba. Kifa kai yayi akan steering yana sheshek’ar kuka.
Itakuma Deela zuwa tayi tana shafa mata goshinta wanda akwai bandage akai, hawaye itama takeyi saita soma magana da dishenshen muryanta.
“Please Miemie ki tashi kinji, kinga an tafi da little one. Im sure zaki san wanda yayi wannan abun....” kuka ta barke dashi mai kara, su Mommy da Anty sunata matse kwalla saboda tausayin Deela.
Tabbas zata shiga wani yanayi idan ta rasa Miemie kuma bayan ta rasa ‘yarta. Ciwon Miemie yanzu ya hanata kukan rashin yarta.
Naufal ne ya janyo Kujera ya zauna dab da ita, bubbuga mata baya yayi ya kwantar da ita akan kafaɗarsa.
“Kiyi hakuri kinji, in sha Allah komai zai daidaita”
“Allah yasa” ta amsa.
Suna haka kowa yana addu’a a ranshi. Abba ne yace masu Fadeela su tafi da Anty. Akwai nurses da aka ware zasu rinka dubata kafin gari ya waye.
Kuka Deela ta barke dashi wai baza’a bar Miemie ta kwana ita kadai da bare ba. Hakuri aka rinka bata amma taki shiru. Naufal ne yace zaije ya dauko Abla ta kwana da ita.
Anan ta rage kukanta sai tace yaje ya dawo zata zauna da ita tukun kafin yazo ya mayar da ita gida idan an dauko Abla ɗin. Kowa ya tafi tareda mata addu’a.
Naufal ya tafi ya dauko Abla, yana parking lot dasu Anty da Abba za’a tafi sai suka ga Khattab cikin motarsa yana kuka. Tadashi aka yi ya tafi gida sai yace ba yanzu ba tukun.
Abba ne yace ya shiga ciki ya zauna kafin Naufal yaje ya dawo saiya tafi. Shiga yayi ciki jiki babu kwari duk ya gaji. Ga wani matsananci ciwon kai da kuka da haifar masa.
Zuwa yayi cikin ɗakin saiya tarar da Deela ta shingiɗa, zama daga chan bakin kofa amma ta ciki. Tagumi yayi saiya soma gyangyaɗi saboda gajiya.
Itama barci yana daukarta amma tana buɗe idonta ta. Suna cikin haka sai barci ya dauke su duka. Basu suka farka ba sai sanda Naufal ya dawo da Abla.
“Ya akayi wanchan abin ya daina motsi? Naufal ne ya tambaya sanda ya shigo kana ya nufa hanyar ECG da aka haɗa da jikin Miemie.
A firgice suka tashi, Deela tana mitsike ido Shikuma Khattab ya zura da gudu wajen gadon. Saka kunnen shi akan kirjinta yayi amma baya jin alamun bugun zuciya.
“Why is she not breathing?” Deela ta faɗa hankali a tashe.
Da sauri ya mayar da kunnen sa wajen hanncinta tareda cire Oxygen tube ko zaiji alamun shakar numfashi amma wayam.
Innalillahi wa inna ilayhi rajiun ra rinka maimaitawa yana yi yana jijigata amma bata motsa ba, asalima jikinta a kankame.
Fadeela ce ta tsandara ihu saita sulale kasa, da sauri Naufal ya tarbota. Bata hakuri ya somayi yace kila wani abune daban.
Ko ba’a faɗa mashi ba yasan Miemie ta koma gidanta na gaskiya. The worst part shine an kasheta ne bawai hakanan bane, tunanin sa ɗaya how can someone be this cruel?
Abla zuwa tayi ta rungume Deela sunata kuka tare, Fadeela ne ke magana cikin kuka a hankali, “Innalillahi wa inna ilayhi rajiun, shikenan Miemie ta tafi barmu”
Shikuma Khattab gefe yake ya zauna a kasa zaman dirshan, kwakwalwarsa sai tafasa yakeyi. Shi tunda yaji labarin accident ɗin yasan za’a yi haka.
Yau gaba ɗaya sai maganar mutuwa takeyi da kuma rok’on sa gafara. Har haushi yaji yayi mata magana, ce masa tayi “you never know when you’ll die, gwara ka shirya kafin lokacin ka”
Duk kalamanta yanzu yawo yake masa a kai, saidai yanzu Idonshi ya kafe. Yama kasa kuka, salati kawai yake cikin ransa. Kirjinsa zafi yakeyi ga gudu da sauri kamar zai fashe.
Ji yayi kamar an daura mashi katon dutse cikin kirjinsa, ga kuma miyau na bakinsa ya kafe k'ab. Karkarwa kawai yakeyi kamar yana jin sanyi.
Shikuma Naufal komawa yayi bakin Varenda yayi tagumi, abin daure masa kai yayi wai dazu ya ganta yanzu kuma ta rasu. Daukar wayarsa yayi domin ya kira ABBA.
“Assalamu Alaikum, ya akayi ne Naufal” Abba yace ta ɗayan ɓangaren. Naufal bai iya amsa sallamar ba, kawai magana ya soma.
“Abba shikenan Miemie ta tafi ta barmu. Abba Miemie ta rasu, ta koma gidanta na gaskiya”
“Innalillahi wa inna ilayhi rajiun” abinda Abba ya iya faɗi kenan.
Shikuma Naufal wasu zafafan hawaye suka soma gangarowa daga idanunsa, da farko kadan kadan sai kuma suka fara gudu.
#NiDaDiyata
~Yarinya Mai DIMPLΣS~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 35 ✨✨✨
'Imran bin Husain (May Allah be pleased with them) reported: Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "Shyness does not bring anything except good."[Al-Bukhari and Muslim].In a narration of Muslim: Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "All of shyness is good."
***********
Kullu Nafsin Za’katul maut. Valar Morghulis. Kowane mai rai mamaci ne, sai dai zamuyi fatan mu cika da kyau da imani.
Fadeela da Abla suna cikin ɗakin suna hawaye, jiki babu kwari Abla ta mik’e tsaye taje inda gadon yake ta rufe mata jiki da mayafi.
Mamakin mutuwar Miemie takeyi, abin yayi mata zuwan ba zata. Addu’a yanzu kawai zata ya Allah yakai haske kabarinta, ya kuma basu hakurin jure rashinta.