Sashe 40
Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba daya babu wanda yayi barcin kirki, Naufal yakan shigo akai akai ya duba su. Saidai kuma Fadeela tayi shiru bata ma cewa komai, kana ganinta kasan cewa kukan zuci takeyi wanda yafi na bayyane ciwo.
Hawaye neke gangaro mata ɗaya bayan ɗaya. Haka har gari ya waye, suka fara shirin komawa gida.
Khattab yanata tunanin dogon suma tayi, Naufal ma haka. Amma Doctors sun masu confirming lallai babu rai a tareda ita.
Anyi making preparations na tafiya da ita gida, shikuma Naufal ya tukasu zuwa gida saboda Deela tana jego kuma sanyi ya fara shigarta.
Cikin gida kuma anata koke koke, Anty Saudah ce tace duk wanda ke kaunar Miemie yayi mata addu’a instead. Daga nan aka rage hayaniya sai masu hawaye kawai.
Shiko Khattab dakyar ya iya tuka kansa zuwa gida. Yana shiga falo babu sallama ya tarar da Daddynshi da Mommy akan dinning suna kalaci.
Ko kallonsu baiyi ba ya haye sama inda ɗakinsa, yana shiga ya banko kofa Karab. Hayewa gadonsa yayi ya kwanta rub da ciki.
Anan ya soma sabon kuka, yanayi yana shesheka gashi muryanshi ya dishe. Mommy ce ta bishi domin ba ɗabi’arsa bane, kofa taji a garke saita firgita.
Komawa tayi wajen IG ta gaya mashi, nan take ya dauke wayarsa dake gefe ya kira Abba. Anan ne ake sanar dashi rasuwar kuma jana’iza karfe 9 na safe.
Yana soma salati Mommy ta gane cewa rasuwa Miemie tayi, nan take tansoma gumi. Kawai tunanin irin halin da Khattab zai shiga take, Allahu Musta’an ta faɗa a fili.
Su Fadeela tana komawa gida sukayi ido da Anty, hawaye ya soma malalo ma Deela amma batace komai ba. Dama ruwan zafi yana jiranta, Hajia Rabi ta chuɗa ta da kanta.
Tayi ɗan kan gado, an kuma kawo mata abinci amma ci takeyi kamar magani. Fuskanta a cunkushe babu annuri kwata kwata gashi ta daina magana.
Suma Forensic tun kafin isowar su Naufal gidan suka zo suka fara aiki gadan gadan. Kokari sukeyi suga wani trace da zaiyi leading ɗinsu wajen gane wanda yayi wannan ɗanyan aikin.
Dama mutane sunfi bada karfi idan Miemie ta tashi zata faɗa koma waye amma kuma ta rasu. Tabbas kuma Miemie taga wanda yayi mata haka saboda bincike ya nuna a jikinta tayi dambe da mutumin kafin aka buga mata karfe.
9am.....
Mutane sun hallara za’ayi ma Laurat Hussain Beli watau Miemie sallah. Shi Khattab kulle kanshi yayi cikin ɗaki yaki zuwa, yana cikin kwance saiga Lili tazo da shiririta wai tana so suyi magana.
Bai kulata ba haka ta gama tsayuwa ta tafi tareda watsa ashar. Ita kuma Yasmeenah tayi kiran duniya Naufal bai ɗauka ba, shi yana kyautata zaton da saka hannunta wajen wannan aika aikan.
Jira yakeyi agama jana’iza ya raka ‘yan sanda har gidansu suyi gaba da ita. Idan yaso bayan sun kulleta su saka ɗanmakullin cikin rafi.
Mommy ɗinta ne ke kallon NTA ita kuma tazo wucewa sai taga hoton Pha’eexah ɓaro ɓaro wai ta ɓata. Tashin hankali ta shiga sosai saboda ta ganta kafinta jiya.
Daga nana kuma sai taga sanarwa akan rasuwar Miemie, anan tayi mutuwan tsaye saboda abin yayi yawa. Sai alocacin ta gane abinda yasa Naufal baya daukar wayanta.
Shiryawa tayi tsab da niyyar zuwa tayi mashi ta’aziyya. Ita kuma Mommy Khattab ta shirya zata gidan gona ta’aziyya, lili ta tambayeta ina zata saita ce “Wanda Khattab yakeso dazu ta rasu”
Taɓe baki Lili tayi sai tayi Magana ciki ciki, “To ni ina ruwana” ashe Mommy taji.
“Babu ruwanki Halima, amma bari nayi maki albishir ko bayan raina ban yarda Khattab ya aureki ba. Na gwammace ya zauna babu aure”
“Babu ruwanki koh?” Mommy tayita nanatawa tana tafiya saboda taji haushi sosai. Ita kuma Lili kuka takeyi saboda bata san meyasa uwar mijinta ta tsaneta haka for no reason.
Gaskiya yanzu bataga lafin da wasu matan ke fada “Idan Uwar mijina nada kirki Allah ka barmin ita, if not Allah ka kasheta tun kafin in shiga”
******
Anyi sallah kuma an kai Miemie gidanta na gaskiya, mutane sunzo sosai saboda kyawawan ɗabiun ta dukda ma tanada taɓun hankali.
Kowa fatan hasken kabari yake mata, Naufal shi ya jagoranci sakata a rami kuma ya tabbatar babu wani guri daya buɗe.
Bayan nan police station ya wuce kai tsaye saboda yaji labarin bincike amma basu bashi wani labari mai daɗi ba. Shi yanzu hankalinsa ya rabu kashi uku.
Na farko mutuwar Miemie, sai kuma ɓatan yarsa ga kuma matarsa ta shiga wani yanayi. Haka suka zauna a gidan gona anata karban gaisuwa.
Baiyi mamakin rashin gainin Khattab ba saboda yasan zaifi kowa missing ɗinta. Sun gaisa da mahaifiyarsa da kuma Mahafinsa kuma shima anjima yayi alkawarin zuwa duba shi.
Ita kuma Deela ɗakin Miemie ta koma zama. Hawaye takeyi bata cewa komai gashi nonota sai ruwa yakeyi saboda rashin tsotso. Duk sai jika mata riga yayi, gashi tana jin alamun kukan Pha’eexah a ranta.
Ita tasan ɗiyar ta tanada rai amma kuma babu ita babu dalilinta. Haka ake zuwa mata gaisuwa, binsu da ido kawai takeyi bata cewa komai.
Koda Yan sanda suka zo karban statement wajenta kallonsu kawai taketa yi, Mansura ce ta faɗa abinda ya faru.
Wajen azahar saiga Yasmeenah tazo sanye cikin purple After dress tayi wrapping kanta irin na Arabs. Tana parking a waje saboda kowa nan ya ajiye nasa.
Naufal yana hangota daga nesa saiya tashi da sauri ya nufa inda take. Ita kuma tana tafiya sannu a hankali saita hange shi.
Wajen dayake ta nufa tana kokarin masa magana kenan, shikuma baiyi wata wata ba ya dauketa da mari. Kafin ta ankara ya kara mata guda ɗaya sannan ya hambareta da kafarsa a cikinta.
Rike ciki tayi ta faɗi kasa tana kuka, a hasalce ya fara mata masifa.
“ke dan Ubanki ina yarinya na?” kallonsa cikin rashin fahimta tayi tana kokarin gane meyasa yake mata irin tambayar.
Fincikarta yayi ya shake, “Ina yarinya na nace dan ubanki? Ki gaggauta fito da ita ko ki yabama aya zakinta.”
“Halan kishi hauka ne? Zaki zo ki daukan min yarinya kuma ki kashe min k’anwa.”
“Infact Uban wa yace kizo gidan suna, shishigi da shiga sharo ba shanu”
“Naufal meye haka? Sai kace bakada tawakkali?” Anty Saudah tace.
Sakin Yasmeenah yayi saita ɗurkusa tana kuka, ita yau abin al’ajabi take gani. Wai daga zuwa gidan rasuwa ance ita tayi kisan.
Jiki babu kwari ta shiga cikin gida, tana tafe kowa yana mata kallon muguwa. Haka har takai ɗakin da Deela take, Fadeela tana ganinta ta rufe ido bata sake buɗewa.
Hawaye kawai taketa yi, haka Yasmeenah ta gama zamanta ta tafi. A wajen fita sai tayi kicibis da Naufal, ja da baya tayi saboda ta tsorata dashi.
Zai buɗe baki yayi magana saiga Yan sanda sunzo mata tambayoyi as protocol. Ana mata tambaya tana kuma amsawa kuma kana ganinta Kasan akwai alamar gaskiya a tareda ita.
Shi karin kanshi Naufal ya karaya amma bai nuna ba. Abba ne yace tace ma iyayenta biki nanda kwana biyar ne babu ɗagawa.
Dama Daddyn ta ya kirashi a waya yayi mashi ta’aziyya kasancewa yana Lagos. Naufal ya fara korafi akan a ɗaga bikin amma Abba ya dakatar dashi.
“Bana son karanci da shiririta Mallam! Kai kace kana so kuma dole ayi babu fashi”
Yasmeenah taji daɗi sosai saboda har kasa ta ɗuka tayi godiya which dama godiya ba ɗabi’anta bane. Harga Allah idan ba’ayi bikin ba zata shiga tashin hankali saboda magunguna na mata daketa dirka.
Da yamma......
Naufal ne yaje da kanshi ya ba Fadeela abinci bayan ta fito daga wanka. Ita yanzu ta daina magana ko musu, yin komai takeyi sannu a hankali amma bata cewa uffan.
Haka ya ciyar da ita harta koshi, yana isarta saita kawar da fuskanta. Magana yayi mata na duniya amma taki amsa shi, daya takura mata saita soma hawaye, dole ya hakura rai baiso ba yabar ɗikin.
Hanyar gidansu Khattab ya nufa tunda dama ya taɓa zuwa sanda Miemie tayi ciwo akanshi. A falo ya tarar da Mommy da Lili.
Dukawa yayi suka sake gaisuwan mutunci da Mommy tunda dama sun haɗu dazu. Ita kuma Lili ‘sannu’ tace ta cigaba da ɓare gyada tana murzawa cikin bakinta.
“kaje upstairs, first room on your left shine ɗakinsa” Mommy tace
“Nagode sosai” ya amsa
Zuwa yayi yana buga kofa a hankali amma babu wanda ya amsa shi, lokacin Khattab shikuma ya soma barci sai yaji bugun kofa. Duk zatonsa Lili ne, tsaki yayi saiya ɗaura pillow a kanshi saboda ya rage noise.
“buɗe mana, nine fah!” murya yaji kamar na Naufal, kasa kunne yayi ko kizo ne amma ya sake jin muryan Naufal.
Da sauri ya tashi ya buɗe, yana ganin fuskar Naufal saiya fashe da kuka.”Dalla Mallam meye haka? Kashe kanka kake so kayi kamar baka yarda da kaddara ba”
“YaNaufal kasheta fah akayi, i can’t imagine the pain she went through” ya faɗa cikin Muryar kuka.
Patting bayansa Naufal yayi saboda shima yana dab da hawaye. “Kaci abinci kuwa?”
“Yanzu zan ci”
“Haba Khattab tun jiya fah” kallonsa Naufal yayi yana tunani saiya tashi ya fita. Downstairs yaje saiya gaya ma Mommy abinci yakeso na Khattab.
Alamun zata tashi saiya dakatar da ita, “tashi ki samu ma Khattab abinci” ya faɗa ma Lili. Watsa mashi harara tayi saita basar.
Mommy ce kunya ya soma ɗawainiyan da ita, “bari kawai naje” Mommy tace.
“Ita wancan meyasa bazata ba?” ya tambaya yana kallon Lili. Sai kuma ya soma masifa tunda dama yanzu ya koya gashi yana neman inda zaiyi pouring frustration ɗinshi.
“Bada ke nakeyi ba? Better hurry up Kije ki kawo min abinci kafin na saɓa maki. Niba ɗan nan gidan bane yanzu zan saɓa maki”
“Bakida hankali ne Mommy tana maki magana kin kyaleta, waye sa’anki? You have lost your goddamn mind, idiot kawai”
Mamaki ya kamata yanda yazo yana mata masifa, amma kuma ta mik’e saboda ta lura kanshi yana motsawa kafin ya jibgeta. Tana jan kafa tana tura baki har taje dinning ta dauko cooler.
“maza ki kai mashi sai ki dawo ki dauko mashi ruwa.” Haka tayi abinda yace, Mommy ce ta fara kuka.
“wai da yanzu wannan akeso a lika ma Khattab, munzo mun samu Miemie shine rai yayi halinsa”
“Yi hakuri Mommy, dangana kawai zamuyi”
Hawaye neke gangaro mata ɗaya bayan ɗaya. Haka har gari ya waye, suka fara shirin komawa gida.
Khattab yanata tunanin dogon suma tayi, Naufal ma haka. Amma Doctors sun masu confirming lallai babu rai a tareda ita.
Anyi making preparations na tafiya da ita gida, shikuma Naufal ya tukasu zuwa gida saboda Deela tana jego kuma sanyi ya fara shigarta.
Cikin gida kuma anata koke koke, Anty Saudah ce tace duk wanda ke kaunar Miemie yayi mata addu’a instead. Daga nan aka rage hayaniya sai masu hawaye kawai.
Shiko Khattab dakyar ya iya tuka kansa zuwa gida. Yana shiga falo babu sallama ya tarar da Daddynshi da Mommy akan dinning suna kalaci.
Ko kallonsu baiyi ba ya haye sama inda ɗakinsa, yana shiga ya banko kofa Karab. Hayewa gadonsa yayi ya kwanta rub da ciki.
Anan ya soma sabon kuka, yanayi yana shesheka gashi muryanshi ya dishe. Mommy ce ta bishi domin ba ɗabi’arsa bane, kofa taji a garke saita firgita.
Komawa tayi wajen IG ta gaya mashi, nan take ya dauke wayarsa dake gefe ya kira Abba. Anan ne ake sanar dashi rasuwar kuma jana’iza karfe 9 na safe.
Yana soma salati Mommy ta gane cewa rasuwa Miemie tayi, nan take tansoma gumi. Kawai tunanin irin halin da Khattab zai shiga take, Allahu Musta’an ta faɗa a fili.
Su Fadeela tana komawa gida sukayi ido da Anty, hawaye ya soma malalo ma Deela amma batace komai ba. Dama ruwan zafi yana jiranta, Hajia Rabi ta chuɗa ta da kanta.
Tayi ɗan kan gado, an kuma kawo mata abinci amma ci takeyi kamar magani. Fuskanta a cunkushe babu annuri kwata kwata gashi ta daina magana.
Suma Forensic tun kafin isowar su Naufal gidan suka zo suka fara aiki gadan gadan. Kokari sukeyi suga wani trace da zaiyi leading ɗinsu wajen gane wanda yayi wannan ɗanyan aikin.
Dama mutane sunfi bada karfi idan Miemie ta tashi zata faɗa koma waye amma kuma ta rasu. Tabbas kuma Miemie taga wanda yayi mata haka saboda bincike ya nuna a jikinta tayi dambe da mutumin kafin aka buga mata karfe.
9am.....
Mutane sun hallara za’ayi ma Laurat Hussain Beli watau Miemie sallah. Shi Khattab kulle kanshi yayi cikin ɗaki yaki zuwa, yana cikin kwance saiga Lili tazo da shiririta wai tana so suyi magana.
Bai kulata ba haka ta gama tsayuwa ta tafi tareda watsa ashar. Ita kuma Yasmeenah tayi kiran duniya Naufal bai ɗauka ba, shi yana kyautata zaton da saka hannunta wajen wannan aika aikan.
Jira yakeyi agama jana’iza ya raka ‘yan sanda har gidansu suyi gaba da ita. Idan yaso bayan sun kulleta su saka ɗanmakullin cikin rafi.
Mommy ɗinta ne ke kallon NTA ita kuma tazo wucewa sai taga hoton Pha’eexah ɓaro ɓaro wai ta ɓata. Tashin hankali ta shiga sosai saboda ta ganta kafinta jiya.
Daga nana kuma sai taga sanarwa akan rasuwar Miemie, anan tayi mutuwan tsaye saboda abin yayi yawa. Sai alocacin ta gane abinda yasa Naufal baya daukar wayanta.
Shiryawa tayi tsab da niyyar zuwa tayi mashi ta’aziyya. Ita kuma Mommy Khattab ta shirya zata gidan gona ta’aziyya, lili ta tambayeta ina zata saita ce “Wanda Khattab yakeso dazu ta rasu”
Taɓe baki Lili tayi sai tayi Magana ciki ciki, “To ni ina ruwana” ashe Mommy taji.
“Babu ruwanki Halima, amma bari nayi maki albishir ko bayan raina ban yarda Khattab ya aureki ba. Na gwammace ya zauna babu aure”
“Babu ruwanki koh?” Mommy tayita nanatawa tana tafiya saboda taji haushi sosai. Ita kuma Lili kuka takeyi saboda bata san meyasa uwar mijinta ta tsaneta haka for no reason.
Gaskiya yanzu bataga lafin da wasu matan ke fada “Idan Uwar mijina nada kirki Allah ka barmin ita, if not Allah ka kasheta tun kafin in shiga”
******
Anyi sallah kuma an kai Miemie gidanta na gaskiya, mutane sunzo sosai saboda kyawawan ɗabiun ta dukda ma tanada taɓun hankali.
Kowa fatan hasken kabari yake mata, Naufal shi ya jagoranci sakata a rami kuma ya tabbatar babu wani guri daya buɗe.
Bayan nan police station ya wuce kai tsaye saboda yaji labarin bincike amma basu bashi wani labari mai daɗi ba. Shi yanzu hankalinsa ya rabu kashi uku.
Na farko mutuwar Miemie, sai kuma ɓatan yarsa ga kuma matarsa ta shiga wani yanayi. Haka suka zauna a gidan gona anata karban gaisuwa.
Baiyi mamakin rashin gainin Khattab ba saboda yasan zaifi kowa missing ɗinta. Sun gaisa da mahaifiyarsa da kuma Mahafinsa kuma shima anjima yayi alkawarin zuwa duba shi.
Ita kuma Deela ɗakin Miemie ta koma zama. Hawaye takeyi bata cewa komai gashi nonota sai ruwa yakeyi saboda rashin tsotso. Duk sai jika mata riga yayi, gashi tana jin alamun kukan Pha’eexah a ranta.
Ita tasan ɗiyar ta tanada rai amma kuma babu ita babu dalilinta. Haka ake zuwa mata gaisuwa, binsu da ido kawai takeyi bata cewa komai.
Koda Yan sanda suka zo karban statement wajenta kallonsu kawai taketa yi, Mansura ce ta faɗa abinda ya faru.
Wajen azahar saiga Yasmeenah tazo sanye cikin purple After dress tayi wrapping kanta irin na Arabs. Tana parking a waje saboda kowa nan ya ajiye nasa.
Naufal yana hangota daga nesa saiya tashi da sauri ya nufa inda take. Ita kuma tana tafiya sannu a hankali saita hange shi.
Wajen dayake ta nufa tana kokarin masa magana kenan, shikuma baiyi wata wata ba ya dauketa da mari. Kafin ta ankara ya kara mata guda ɗaya sannan ya hambareta da kafarsa a cikinta.
Rike ciki tayi ta faɗi kasa tana kuka, a hasalce ya fara mata masifa.
“ke dan Ubanki ina yarinya na?” kallonsa cikin rashin fahimta tayi tana kokarin gane meyasa yake mata irin tambayar.
Fincikarta yayi ya shake, “Ina yarinya na nace dan ubanki? Ki gaggauta fito da ita ko ki yabama aya zakinta.”
“Halan kishi hauka ne? Zaki zo ki daukan min yarinya kuma ki kashe min k’anwa.”
“Infact Uban wa yace kizo gidan suna, shishigi da shiga sharo ba shanu”
“Naufal meye haka? Sai kace bakada tawakkali?” Anty Saudah tace.
Sakin Yasmeenah yayi saita ɗurkusa tana kuka, ita yau abin al’ajabi take gani. Wai daga zuwa gidan rasuwa ance ita tayi kisan.
Jiki babu kwari ta shiga cikin gida, tana tafe kowa yana mata kallon muguwa. Haka har takai ɗakin da Deela take, Fadeela tana ganinta ta rufe ido bata sake buɗewa.
Hawaye kawai taketa yi, haka Yasmeenah ta gama zamanta ta tafi. A wajen fita sai tayi kicibis da Naufal, ja da baya tayi saboda ta tsorata dashi.
Zai buɗe baki yayi magana saiga Yan sanda sunzo mata tambayoyi as protocol. Ana mata tambaya tana kuma amsawa kuma kana ganinta Kasan akwai alamar gaskiya a tareda ita.
Shi karin kanshi Naufal ya karaya amma bai nuna ba. Abba ne yace tace ma iyayenta biki nanda kwana biyar ne babu ɗagawa.
Dama Daddyn ta ya kirashi a waya yayi mashi ta’aziyya kasancewa yana Lagos. Naufal ya fara korafi akan a ɗaga bikin amma Abba ya dakatar dashi.
“Bana son karanci da shiririta Mallam! Kai kace kana so kuma dole ayi babu fashi”
Yasmeenah taji daɗi sosai saboda har kasa ta ɗuka tayi godiya which dama godiya ba ɗabi’anta bane. Harga Allah idan ba’ayi bikin ba zata shiga tashin hankali saboda magunguna na mata daketa dirka.
Da yamma......
Naufal ne yaje da kanshi ya ba Fadeela abinci bayan ta fito daga wanka. Ita yanzu ta daina magana ko musu, yin komai takeyi sannu a hankali amma bata cewa uffan.
Haka ya ciyar da ita harta koshi, yana isarta saita kawar da fuskanta. Magana yayi mata na duniya amma taki amsa shi, daya takura mata saita soma hawaye, dole ya hakura rai baiso ba yabar ɗikin.
Hanyar gidansu Khattab ya nufa tunda dama ya taɓa zuwa sanda Miemie tayi ciwo akanshi. A falo ya tarar da Mommy da Lili.
Dukawa yayi suka sake gaisuwan mutunci da Mommy tunda dama sun haɗu dazu. Ita kuma Lili ‘sannu’ tace ta cigaba da ɓare gyada tana murzawa cikin bakinta.
“kaje upstairs, first room on your left shine ɗakinsa” Mommy tace
“Nagode sosai” ya amsa
Zuwa yayi yana buga kofa a hankali amma babu wanda ya amsa shi, lokacin Khattab shikuma ya soma barci sai yaji bugun kofa. Duk zatonsa Lili ne, tsaki yayi saiya ɗaura pillow a kanshi saboda ya rage noise.
“buɗe mana, nine fah!” murya yaji kamar na Naufal, kasa kunne yayi ko kizo ne amma ya sake jin muryan Naufal.
Da sauri ya tashi ya buɗe, yana ganin fuskar Naufal saiya fashe da kuka.”Dalla Mallam meye haka? Kashe kanka kake so kayi kamar baka yarda da kaddara ba”
“YaNaufal kasheta fah akayi, i can’t imagine the pain she went through” ya faɗa cikin Muryar kuka.
Patting bayansa Naufal yayi saboda shima yana dab da hawaye. “Kaci abinci kuwa?”
“Yanzu zan ci”
“Haba Khattab tun jiya fah” kallonsa Naufal yayi yana tunani saiya tashi ya fita. Downstairs yaje saiya gaya ma Mommy abinci yakeso na Khattab.
Alamun zata tashi saiya dakatar da ita, “tashi ki samu ma Khattab abinci” ya faɗa ma Lili. Watsa mashi harara tayi saita basar.
Mommy ce kunya ya soma ɗawainiyan da ita, “bari kawai naje” Mommy tace.
“Ita wancan meyasa bazata ba?” ya tambaya yana kallon Lili. Sai kuma ya soma masifa tunda dama yanzu ya koya gashi yana neman inda zaiyi pouring frustration ɗinshi.
“Bada ke nakeyi ba? Better hurry up Kije ki kawo min abinci kafin na saɓa maki. Niba ɗan nan gidan bane yanzu zan saɓa maki”
“Bakida hankali ne Mommy tana maki magana kin kyaleta, waye sa’anki? You have lost your goddamn mind, idiot kawai”
Mamaki ya kamata yanda yazo yana mata masifa, amma kuma ta mik’e saboda ta lura kanshi yana motsawa kafin ya jibgeta. Tana jan kafa tana tura baki har taje dinning ta dauko cooler.
“maza ki kai mashi sai ki dawo ki dauko mashi ruwa.” Haka tayi abinda yace, Mommy ce ta fara kuka.
“wai da yanzu wannan akeso a lika ma Khattab, munzo mun samu Miemie shine rai yayi halinsa”
“Yi hakuri Mommy, dangana kawai zamuyi”