← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 48

Sashe 38

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Taro ya kusan watsewa, mutane sun soma tafiya. An kawo gara daga gidanmu, akwatuna uku da kit akayi mani daga wajen dangina.

Kayan abinci shake kamar su shinkafa, semovita, taliya dasu mangyaɗa. Wani mota ne ya shigo cikin gidan.

Miemie locacin tana haɗa kujerun da akayi amfani dasu. Wani mota ne ya shigo sai taga yan mata su uku sun fito suna feleke. Sannu a hankali taje ta gaida su. A yatsine Meenah ta amsa, Laila ne da Lubna suka amsa da kyau.

Daga nan suka tambayeta inda mai jego take, “Ku biyoni” tace masu.
Sannu a hankali suka bita har inda nake, ni kuma na fito daga wankar dare har na saka Lace wanda akayi zani da riga simple dinki.

Fuskana babu komai sai natural beauty ɗina, su Mansura kuwa anata kwalliya zasu tafi saboda saurayinta zai zo daukar ta.

Su Laila suka shiga suka tsaya a bakin kofa, sallama sukayi tareda gaisuwa a tsartsaye. Ina ganin su na gane su, itama Mansura ma haka.

Nan take muka haɗa girar sama dana kasa. Mika ma Miemie katon sallaya nayi akan ta shimfiɗa masu.
“Miemie jeki kawo ma amaryan Yayanki abinci koh?” Mansura ta faɗa rai a haɗe.

“OMG keh ce Miemie? wallahi MINE yana bani labarin ki all the time” Yasmeenah ta faɗa tana washe hakora.

“Allah sarki” kawai tace tareda balla mata harara. Haushi ne ya kamata wai ace yanzu YaNaufal wannan yar iskan zai auro.

Laila ce cikin fara’a tace a mika mata jaririya su gani, daga nan ta tambaya sunar ɗiyar. Yarinyar tanata ma Laila  murmushi har dimples ɗinta yana nunawa.

Nan take Yasmeenah taji sha’awar ta, har cikin ranta taji soyayyarta. Gata tana kama sosai da Mine ɗinta, fuskar da kuma idanun.

Itama mika hannu tayi a mika mata, tana karba ta fara mata wasa saita ta fashe da kuka maimakon dariya. Tanata jijigata a hankali amma taki shiru, Lubna ne ta karba domin ta gwada.

Itama batayi shiru ba, ina daga kwance akan gado na hakince ni a dole matar gida. Anty Saudah ce ta shigo sai suka mika mata Pha’eexah “Jikata,kunyarsu kikeyi?” Anty tace.

“She is not comfortable ne kawai around strangers” nace ina gimtse baki.

Yasmeenah tasan magana ta gaya mata amma babu komai, nanda Next week Zata zama matarshi.

An kawo abinci Meenah ko kallo batayi ba, kawai latsa wayar ta takeyi tana murmushi. Su Laila ne suke cin samosa da cake.

Miemie ce ta shigo da sauri tareda wayana a hannunta wai YaNaufal yana kirana. Saidai kafin na dauka ya tsinke, Daga nan saita soma wasa ni.

“ Anty yar gayu uwar gida sarautan mata, kece ta farko kuma kece ta karshe a zuciyar Yaya. You bring out the best in him” guɗa tayi kana ta cigaba da wasani.

“ ke kura ce kuma dole karnuka suji tsoron ki, walkiya mai haskaka gari, ɗawisu adon tafiya.....” Zata cigaba saina tsinke ta. Ina dariya nace, “Ya isa haka mana, It’s getting lame”

Itama Miemie dariya takeyi harda Mansura da Sadiya, “Anty ai gaskiya na faɗa”

Su Yasmeenah haushi sukaji sosai, mikewa tsaye tayi wai zasu tafi, Laila ce tace Uwar gida bazaki raka muba, harda bazan kula maganar ba sai Mansura ta tashi wai itama zata tafi.
Mika ma min kayan gaisuwan su sukayi kuma na gode masu sosai. An ajiye Pha’eexah cikin Craddle ɗinta saboda ta fara barci.

Miemie ce ta zauna da ita saboda ɗakin babu kowa. Nikuma ina rike da  souvenir ɗinsu Meenah a hannuna har wajen motarsu kana na mik’a masu.

Basu tafi ba nan take wai suna jiran friend ɗinsu dake unguwar ta zo ta samesu, sallama nayi masu kana na karasa wajen Motana inda Mansura take.

Munata hira abinmu sai mukaji ihu daga cikin gida anayi ana salati. Da sauri muka karasa wajen shine akace wuta ne ya kama a dakin mai jego.

Da gudu muka ruga domin baby Pha’eexah tana ciki, muna karasawa mukaga wuta yana ci fal fal fal kuma kamar chinnawa akayi.

Kuka na barke dashi inayi ina kururuwa. Gashi kuma kofa a rufe gam babu daman shiga. Bubbugawa nakeyi ina kiran sunar yarinya na.

Mutane anyi charko charko ana kuka,gashi an kasa shiga ciki. Duk abinda akeyi babu Miemie babu dalilinta.

Wani cousin ɗin Naufal mai suna Hadi yazo ya rinka dukan kofar, daga bisani sai gashi ya buɗe. Da gudu naje zan shiga amma wuta ya korani baya.
Ruwa aka watsa mashi amma kamar ana karawa ne, ina kuka duk na fita hayacina gashi kuma saura kadan ya karasa Craddle din Pha’eexah.

Omo aka saka cikin bokatin ruwa sai aka watsa ma wutan sai ya fara lafawa, ina shiga na soma gudu kenan sai nayi tuntube da abu. Kallon da zanyi saina ga Miemie ce kwance a sume jini yana malalo mata daga fuska da alamun ta bige ne.

Gashi wuta ya soma cin wajen cikinta. Kuka na sake fashewa da shi saboda ban taɓa ganin tashin hankali irin wannan ba. Da sauri na tashi domin naje na dauko Pha’eexah tunda ya kusa karasawa inda take.

Nan naga babu yarinya, gashi kuma wutan bai fara cin wajen ba. Dama yafi karfi a bakin kofa. Waige waige na samoyi ina kuka. Wata sabuwa kuma inji yan cha cha!

Wayam kawai saboda babu alamar yarinyar nan a cikin ɗakin. Da gudu aka janye Miemie waje aka soma watsa mata ruwa amma hayaki yayi yawa a lungs ɗinta. Ko motsawa batayi ba kuma da kyar in akwai rai a tareda ita.

kuka nakeyi sosai saboda tashin hankali baya misaltuwa, babu Pha'eexah gashi kuma Miemie rai yana hannun Allah. Duk na sukurkuce na kasa saisaita tunanina a waje guda.
Wani tunani nayi saina ruga parking lot nayi ko zan ga Yasmeenah da ayarinta amma babu su a wajen.

Nan take na yanke jiki na faɗi sumammiya.

#NiDaDiyata

~Yarinya Mai Dimples~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 34 ✨✨✨

It was narrated form Anas that the Messenger of Allah said "None of you should wish for death because of some harm that befalls him, rather he should say: 'Allahumma ahini ma kanatil-hayatu khairanli wa tawaffani idha kanatil-wafatu khairanli (O Allah, keep me alive so alive so long as life is good for me, and cause me to die when death is good for me.)"' (Sahih)

***********

Nan take mutane sukayo kan Fadeela tareda kwanon ruwa, watsa mata akayi ana mata fifita.Tana farfaɗowa taga mutane charko-charko akanta tasan cewa ba mafarki takeyi ba da gaske ne.

Nanta sake barkewa da kuka mai tsuma rai, ita kuma Anty Saudah tana chan tana ganin tashin hankali saboda Miemie bata motsi har locacin.

Hadi ne ya sungumeta ya tafi da ita cikin Mota saboda zasu asibiti. Haka Anty tabi sahun shi a ruɗe ko mayafi babu, a hanya ne wajen parking lot wata ta mik’a mata hijabi.

Deela na ganinsu ta mik’e wai zata bi su, anyi anyi a hanata tareda cewa ta zauna a gida kila Babyn an fita da ita unguwa ne.

Nan Deela ta fashe da kuka, zama tayi dirshan a parking lot sai rizgar kuka takeyi. Kana ganinta gwanin ban tausayi, Hajia Rabi tazo ta janyeta daga wajen saboda maraice ne kafin sanyi ya shigeta.

Bilqees ne ta kira Naufal ta faɗa mashi abinda ake ciki, dama locacin yana hanyar layinsu. Juyawa yayi ya nufa hanyar asibiti.

Abinda yasa bai fara zuwa wajen Deela ba yasan cewa she is a strong woman unlike Anty Saudah. Yana isa locacin an shigar da ita ER, Hadi ne yayimasa bayani a gurguje.

Ita lokacin Anty Saudah tana kan kujera tanata kuka a hankali. Tunani ɗaya  yake mata yawo a kai, ya zata yi idan ta rasa yarta ɗaya tilo. Nan ta soma kuka a bayyane, Naufal duk zafin dayake ji a ranshi ya shanye yana bata hakuri.

Itakuma Fadeela tanata kuka kamar ranta zai fita, bata san Wanne yafi mata ciwo ba. K'onewan da Miemie tayi kokuma ɓacewan da Pha’eexah tayi?

Idanta yayi jazur kamar garwashi domin kuka kuma kanta sai sara yakeyi. Ji takeyi  kamar Allah ya dauki ranta ta huta da wannan tashin hankali.

Suma su Mommy sunajin abinda ya faru tazo gidan gona, anan kuma Fadeela ta soma sabon kuka, Mommy bata hanata ba illa tayata.

Haka suka runguma juna sunayi gwanin ban tausayi, kowa a wajen tausaya masu yakeyi. Gashi Fadeela tayi trying wayar Naufal bai dauka ba.
Sabon kuka ta somayi  saboda duk a zaton ta yana wajen Yasmeenah ne. Cema Mommy tayi bari taje asibiti wajen Miemie da Anty tunda anyi ransacking gidan ba’a ga Pha’eexah ba. Zamanta anan baxai fito da ita ba.

Mommy bata hanata ba saboda ita ta tuka ma motar da suka tafi.
Shikuma cikin ruɗewa ya bar wayar a cikin motarsa. Yasa bazai san wanda ke kiran sa ba. Su Grand Kadi da Abba sun tafi police station dasu gidan radio.

A wajen police station ɗinne sukaga IG watau babban Khattab yazo duba abu wajen DPO. Nan take ya saka kwararrun yan sanda akan case ɗin kuma yayi masu alkawarin basu huta ba sai anga duk wanda akwai saka hannunsa a cikin abun.

IG da kanshi ya kira Khattab ya faɗa mashi halinda ake ciki, anan fah Khattab ya ruɗe. Mukullin motarsa ya figa ya soma gudu babu ji ba gani.
Sau biyu yana kusan aukawa ma trailer amma yana kaucewa da wuri.

Haka yaketa yi harya kai asibitin.
Ko rufe motarsa baiyi da kyau ba ya soma gudu ciki, lokacin kuma yayi daidai da isarsu Fadeela.

Suna tsaye a bakin Emergency Room babu wanda ya fito daga ciki, likitoci ne keta aikinsu.
Anty Saudah tana ganin Fadeela saita sake barkewa da wani sabon kuka, nan suka rinka yi su biyu. Duk cikin family suna cikin wanda sukafi shakuwa da ita.

Shima Khattab yana ganin yadda suke kuka saiya kame chan kurya yana kuka. Hankalin Deela ya kwanta dataga Naufal a wajen.

Tsagaita kukanta tayi taje inda yake ya dafa kumatu yana tunani ta zauna, riko masa hannu tayi ta soma magana cikin kuka, “Pha’eexah ta.........” saita barke da kuka, kwantawa tayi akan kafadarsa tana kuka wiwi.
Chapter 38 · 0% Book details