Sashe 42
Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kinsan cewa Fadeela batada karfin jikin da zata yi maki girki, kuma anyi rasuwa balle su Anty ko Abla suyi. Please why can't you be understanding mana"
"Kasan Allah bazan yiba, besides idan baka lura ba barina fahimtar dakai. Bafa yar aiki ka auro ba, nifa matarka ce"
"Yanzu danke matana ne saiki barni da yunwa"
Ko kallonsa batayi ba, asalima daukan remote tayi ta canza channel which abinda Deela bata masa. Sam babu raini tsakanin shida ita, amma wannan tun jiya take gasa masa magana san ranta.
Big Brother ta kunna, wani dan gidan aka nuna saita daka tsalle tana murna, "Kai TTT kana burgeni"
Kwafa Naufal yayi yaje ɗaki ya dauko wallet ɗinshi, daga nan wani Kiosk dake bakin anguwan su yaje. Kayan shayi ya siyo da kwai da sardine.
Inda ya barta nan ya sameta sai kallo takeyi, "Bisola meye haka?" Yasmeenah ta faɗa tana ɓata rai.
Dire ledan yayi akan centre table.
"Okay ga kayan shayi na kawo, Latte zaki haɗa min sai kuma ki soya kwai tareda sardine. Ba wani aikin wuya bane"
Bata ko kalleshi ba, asalima haɗa rai tayi. "Tunda ba wuya saika yi da kanka mana"
"Sannu me wayo! Kai ka hakince akan Couch zata takura min" baiso tankawa ba amma yace gwara ya kwaɓeta kafin raini ya shiga tsakanin su.
"Meye haka kikeyi tun dazu? Don ina kyaleki shine kike so ki raina ni"
"Ni dai ka daina min ihu tunda bakai ka haifeni ba" ta faɗa ciki ciki,
Mikewa yayi ya shiga kitchen ɗin Deela ya dauko Mug, hawa sama yayi ya shiga bayi ya ɗebo ruwan zafi.
Daukar kayan shayin yayi ya nufa dinning, komawa kitchen yayi ya dauko cokali da plate. Zuba sardine din yayi saiya haɗa coffee mara madara ya soma sha.
Yanayi yana haɗa bread da kifi, ya tabbata idan ya biye ma Meenah yunwa zai iya kaishi lahira.
Yana cikin ci sai itama tazo domin ta saka wani abu cikin bakinta, ko kallonsa batayi ba ta fara gabza bread da sauran sardine ɗin. Bata sha shayi dama bata sha.
Baice mata komai ba har suka gama brunch (Breakfast /lunch). Komawa yayi kan couch ya canza channel. Zuciyar shi sai zafi yakeyi yana tafasa, baima san yadda zasuyi ba wajen abincin rana.
Lallai hankali baiwa ne kuma ba'a shekaru suke ba, Yasmeenah ta girma Fadeela da kusan shekara biyu amma Deela ta fita hankali. Suna zaune suna kallo saiga Huzaifah ya shigo da Haisam.
Ba Naufal ba har Meenah sai da tayi mamakin ganin su, musamman Huzaifah. Haushin Meenah Naufal yakeji saboda bata wani gaggawa ta rufe jikinta. Ita kuma ba yau suka saba ganinta haka ba.
Haka shigarta yake ko cikin gidansu, kayanta kenan su leggings da bom shorts. Mikewa tsaye tayi domin ta kawo masu ruwa. Tana tafe tana juya jiki which yana yinta ne.
Gashi duk jikinta rawa yakeyi kamar ka saka ruwa cikin leda. Huzaifah ya kalleta sosai kuma yaji daɗi har cikin ranshi.
Ta dawo da chi exotic da kuma dubulan da alkaki which dama tazo da abinta na tarban baki. Su Huzaifah sunci sunata hira, itama sama sama takeyi saboda sun daina shiri da daɗewa.
Bayan almost 40 mins saiya tashi wai su tafi, dama yazo yaga lafianta ne a matsayin sa na babban Wanta. Zata mike ta rakasu sai Naufal ya fincike ta. Dole ta zauna sai shi ya rakasu.
"Wancan Huzaifah meye matsalar sa?" Naufal yake tambayar Meenah bayan ya dawo daga rakiya.
Dariya Meenah tayi tana rausaya kai saita soma magana cikin yauki, "haba Mine kar kace kishi kake yi?"
"Ba maganar kishi bane kawai i dont Like him ne, koko im not allowed to say my mind. Besides Bakiga yadda yake kallon ki bane"
"Haka yake idan ma yadda ya kalleni ne, i think nature dinsa ne. Kosu Lubna da Laila haka yake kallon su."
"besides munyi faɗa i think ya gane kuresa yasa yakeso yayi squashing ɗin komai. Everything ya zama past tense tunda yanzu nayi aure"
"Koba wannan ba he is my brother for heaven sake ai bazan iya hanashi zuwa wajena ba. Its just kamar nace Abla karta zo ko Bilqees.. Kaga ai its not even making sense mana"
"He is not Abla ko Bilqees, kuma Nidai i hate him"
Ya faɗa sai yayi hanyar upstairs, "better learn to like him saboda bazan rabu da family ɗina ba wai a dole nayi aure" ta mayar masa. Dama haka take, duk me kace saita baka amsa.
4:30pm....
Naufal ya idar da sallah saiya saka manyan kaya saboda suje su gaishe da yan gidansu. Baici komai ba banda cikinsa da ke wakar yori yori.
Ita kuma Yasmeenah Big Brother Nigeria take Kallo abinta a falo, da yunwa ya soma ɗibarta saita dauko bread ta ajiye gefe tana tsakura. Ko azahar batayi ba balle wani la'asar.
Ga kuma sauran exotic wanda su Huzaifah suka sha bata kawar ba.
Shita rinka gyangyama. Yana saukowa ya ganta tana kallo, "jeki shirya zamu gidan gona"
"Meyasa?" tace tana wani kallonsa.
"Bcs i say so" ya faɗa saiya fice ya wuce chan bakin gate domin yasha iska kuma ya jirata.
Rai a jagule taje ta soma shiri, lace ta saka mai ɗan karan tsada, ɗinkin kimono akayi saita dauki mayafi. Fuskanta shake da makeup, yana ganinta yayi fuska kamar bai ganta ba.
Data gaji da tsayuwa saita fara sababi, "Haba kace zamu fita kuma ka shanya ni kamar kayan wanki, idan bazaka ba saika min bayani na koma daki. A duniya wulakanci ne bana so"
Yaji kunya sosai saboda dukda Maigadi yana nesa da inda suke dole yaji saboda yadda ta ɗaga muryanta chan kurya. Wai yau matarsa ke daka mashi tsawa kamar ɗanta.
Idan baiyi wasa ba Yasmeenah tana dab da mayar dashi mijin Hajia. "da makeup zaki gidan mutuwa"
"Toh ba saika faɗa minba,sai ka shanyani kamar wata shargi" soma tafiya tayi tana gogewa da haɓan gyalenta.
Shima tasowa yayi suka shiga mota, babu wanda yace komai sai tafiya akeyi, itace tayi connecting wayar ta da Aux ta kunna wakar Wizkid mai suna Daddy Yo. Haka ta rinka yi har suka isa ciki.
Sama sama tayi ma kowa, ita yanzu bata damuda kallon dasuke mata ba saboda bakin alkalami ya bushe yanzu Naufal nata ne.
Koda aka haɗasu ana masu nasiha akan hakuri da sauran al'amura na rayuwa, attention ɗinta yafi karkata akan TV while ita Deela kanta yana kasa.
Bayan nan aka kawo masu abinci suci, daga ita har Naufal sunci sosai saboda yunwa yana addabar su, tuwan shinkafa ne da miyan taushe sai kuma kunun aya.
Abba ne ya shigo yana neman Abla ta kaima Khattab abinci saboda rabonsa da gidan tun Miemie na raye.
Dama Naufal ya gama ci saiya tashi domin su gaisa, a garden ya iske Khattab yana wasa da Sunflowers.
Tausayin shi yake sosai saboda Miemie ta shuka da hannunta.
Khattab yana ganin Naufal ya mike da fara'arsa, hakuri ya soma bashi akan rashin zuwa bikinsa da baiyi ba. Acewarsa kwanan sa huɗu a asibiti sai dazu aka sallame shi.
Jaje Naufal yayi mashi sai yace su koma falon baki ya zauna, Naufal saiya koma ciki domin ya faɗa ma Abla inda zata kai abinci.
Yana zaune ya kifa kansa akan cinyarsa, baisan da zuwanta ba saiya ganta a gabansa. Baya ya matsa a firgice har saida ta tsorata.
"Haskena kin dawo ne?" ya faɗa a tsorace. Sai kuma ya fara mika hannunsa dake rawa yana so ya taɓa fuskarta yaji ko itace ɗin.
#NiDaDiyata
*Dedicated to all the family of this book, because yanzu mun zama yan uwa*
~Yarinya Mai DIMPLΣS~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 37 ✨✨✨
On the authority of Abu Dhar Jundub bin Junadah, and Muadh bin Jabal that the messenger of Allah said : "Fear Allah wherever you are, and follow up a bad deed with a good one and it will wipe it out, and behave well towards people." Tirmithi narrated the Hadith and said it was fine, and in another version, said ture and fine.
**********
Ikon Allah Abla ta tsaya gani, duk ya ruɗe babu gaira babu dalili, though ranta yana bata cewa kila shima yana ganin gizon da akace tanayida Miemie. Sai dai ba wani big deal bane dazai rude haka kamar yayi gamo.
Bata hanashi taɓa fuskarta ba saida itama ta kafa mashi ido kamar yadda ya kafa mata. Yana taɓata yaji mutum ne saiya sake baya ya rufe idonsa. Rufa ke keto masa duk ya firgita, saiga Naufal ya shigo.
“Yauwa Abla dama ke nake nema”
Kallon Khattab yayi yaga ya sukurkuce, Cikin damuwa ya soma masa magana.
“Lafiya kake zufa duk Ac dakin cikin nan?”
“I think shima yana ganin Miemie a fuskata ne” ta amsa a sanyaye
“Ohhh! Of course Abla ne, yes im not running mad” Khattab ya faɗa yana ajiyar zuciya a hankali, handkerchief fari ya ciro daga cikin aljihunsa ya share zufan Fuskarsa.
Da farko ya dauka yayi gamo ne, sai kuma ya sha hauka ya somayi. Zuwan Naufal ba karamin relief ya bashi ba. Ita kuma mikewa tayi ta bar wajen tana matse kwalla.
Abin ya fara isanta, hala mutane basu lura itama tana missn Miemie bane, duk inda taje sai an firgita kuma ba’a lura itama tana jin ciwon abun cikin ranta.
Shi kuma fasa cin abincin yayi saiya tafi gida kawai, kwanciyar rub da ciki yayi akan gadonsa. Kawai tunanin yanda Abla batada bambanci da Miemie ne yakeyi. Magrib aka kira saiya tashi ya wuce masjid.
A hanyar gate ya haɗu da Lili tana dawowa daga anguwa, da gudu ta karasa inda yake ta rungume sa. Dama rabon data haɗu dashi tun shekaran jiya.
“YaKhattab naji daɗin ganinka Wallahi”
“Na hanaki rikeni, wai meyasa bakya jine?”
“Toh fah ji wani sanabe, wallahi iyayi da kakeyi kamar baka jin dadi idan na rike ka bani mamaki yakeyi”
“Eh naji nidai sakeni kawai kinga masallaci zani kafin na makara”
“Anaso ana kaiwa kasuwa” tace saita sake shi. Harya soma tafiya wajen taku biyar haka saiya juya, “Lili” ya kirata.
Itama waigowa tayi tana rarraba idanu, “ya akayi ne Yaya?”
"Kasan Allah bazan yiba, besides idan baka lura ba barina fahimtar dakai. Bafa yar aiki ka auro ba, nifa matarka ce"
"Yanzu danke matana ne saiki barni da yunwa"
Ko kallonsa batayi ba, asalima daukan remote tayi ta canza channel which abinda Deela bata masa. Sam babu raini tsakanin shida ita, amma wannan tun jiya take gasa masa magana san ranta.
Big Brother ta kunna, wani dan gidan aka nuna saita daka tsalle tana murna, "Kai TTT kana burgeni"
Kwafa Naufal yayi yaje ɗaki ya dauko wallet ɗinshi, daga nan wani Kiosk dake bakin anguwan su yaje. Kayan shayi ya siyo da kwai da sardine.
Inda ya barta nan ya sameta sai kallo takeyi, "Bisola meye haka?" Yasmeenah ta faɗa tana ɓata rai.
Dire ledan yayi akan centre table.
"Okay ga kayan shayi na kawo, Latte zaki haɗa min sai kuma ki soya kwai tareda sardine. Ba wani aikin wuya bane"
Bata ko kalleshi ba, asalima haɗa rai tayi. "Tunda ba wuya saika yi da kanka mana"
"Sannu me wayo! Kai ka hakince akan Couch zata takura min" baiso tankawa ba amma yace gwara ya kwaɓeta kafin raini ya shiga tsakanin su.
"Meye haka kikeyi tun dazu? Don ina kyaleki shine kike so ki raina ni"
"Ni dai ka daina min ihu tunda bakai ka haifeni ba" ta faɗa ciki ciki,
Mikewa yayi ya shiga kitchen ɗin Deela ya dauko Mug, hawa sama yayi ya shiga bayi ya ɗebo ruwan zafi.
Daukar kayan shayin yayi ya nufa dinning, komawa kitchen yayi ya dauko cokali da plate. Zuba sardine din yayi saiya haɗa coffee mara madara ya soma sha.
Yanayi yana haɗa bread da kifi, ya tabbata idan ya biye ma Meenah yunwa zai iya kaishi lahira.
Yana cikin ci sai itama tazo domin ta saka wani abu cikin bakinta, ko kallonsa batayi ba ta fara gabza bread da sauran sardine ɗin. Bata sha shayi dama bata sha.
Baice mata komai ba har suka gama brunch (Breakfast /lunch). Komawa yayi kan couch ya canza channel. Zuciyar shi sai zafi yakeyi yana tafasa, baima san yadda zasuyi ba wajen abincin rana.
Lallai hankali baiwa ne kuma ba'a shekaru suke ba, Yasmeenah ta girma Fadeela da kusan shekara biyu amma Deela ta fita hankali. Suna zaune suna kallo saiga Huzaifah ya shigo da Haisam.
Ba Naufal ba har Meenah sai da tayi mamakin ganin su, musamman Huzaifah. Haushin Meenah Naufal yakeji saboda bata wani gaggawa ta rufe jikinta. Ita kuma ba yau suka saba ganinta haka ba.
Haka shigarta yake ko cikin gidansu, kayanta kenan su leggings da bom shorts. Mikewa tsaye tayi domin ta kawo masu ruwa. Tana tafe tana juya jiki which yana yinta ne.
Gashi duk jikinta rawa yakeyi kamar ka saka ruwa cikin leda. Huzaifah ya kalleta sosai kuma yaji daɗi har cikin ranshi.
Ta dawo da chi exotic da kuma dubulan da alkaki which dama tazo da abinta na tarban baki. Su Huzaifah sunci sunata hira, itama sama sama takeyi saboda sun daina shiri da daɗewa.
Bayan almost 40 mins saiya tashi wai su tafi, dama yazo yaga lafianta ne a matsayin sa na babban Wanta. Zata mike ta rakasu sai Naufal ya fincike ta. Dole ta zauna sai shi ya rakasu.
"Wancan Huzaifah meye matsalar sa?" Naufal yake tambayar Meenah bayan ya dawo daga rakiya.
Dariya Meenah tayi tana rausaya kai saita soma magana cikin yauki, "haba Mine kar kace kishi kake yi?"
"Ba maganar kishi bane kawai i dont Like him ne, koko im not allowed to say my mind. Besides Bakiga yadda yake kallon ki bane"
"Haka yake idan ma yadda ya kalleni ne, i think nature dinsa ne. Kosu Lubna da Laila haka yake kallon su."
"besides munyi faɗa i think ya gane kuresa yasa yakeso yayi squashing ɗin komai. Everything ya zama past tense tunda yanzu nayi aure"
"Koba wannan ba he is my brother for heaven sake ai bazan iya hanashi zuwa wajena ba. Its just kamar nace Abla karta zo ko Bilqees.. Kaga ai its not even making sense mana"
"He is not Abla ko Bilqees, kuma Nidai i hate him"
Ya faɗa sai yayi hanyar upstairs, "better learn to like him saboda bazan rabu da family ɗina ba wai a dole nayi aure" ta mayar masa. Dama haka take, duk me kace saita baka amsa.
4:30pm....
Naufal ya idar da sallah saiya saka manyan kaya saboda suje su gaishe da yan gidansu. Baici komai ba banda cikinsa da ke wakar yori yori.
Ita kuma Yasmeenah Big Brother Nigeria take Kallo abinta a falo, da yunwa ya soma ɗibarta saita dauko bread ta ajiye gefe tana tsakura. Ko azahar batayi ba balle wani la'asar.
Ga kuma sauran exotic wanda su Huzaifah suka sha bata kawar ba.
Shita rinka gyangyama. Yana saukowa ya ganta tana kallo, "jeki shirya zamu gidan gona"
"Meyasa?" tace tana wani kallonsa.
"Bcs i say so" ya faɗa saiya fice ya wuce chan bakin gate domin yasha iska kuma ya jirata.
Rai a jagule taje ta soma shiri, lace ta saka mai ɗan karan tsada, ɗinkin kimono akayi saita dauki mayafi. Fuskanta shake da makeup, yana ganinta yayi fuska kamar bai ganta ba.
Data gaji da tsayuwa saita fara sababi, "Haba kace zamu fita kuma ka shanya ni kamar kayan wanki, idan bazaka ba saika min bayani na koma daki. A duniya wulakanci ne bana so"
Yaji kunya sosai saboda dukda Maigadi yana nesa da inda suke dole yaji saboda yadda ta ɗaga muryanta chan kurya. Wai yau matarsa ke daka mashi tsawa kamar ɗanta.
Idan baiyi wasa ba Yasmeenah tana dab da mayar dashi mijin Hajia. "da makeup zaki gidan mutuwa"
"Toh ba saika faɗa minba,sai ka shanyani kamar wata shargi" soma tafiya tayi tana gogewa da haɓan gyalenta.
Shima tasowa yayi suka shiga mota, babu wanda yace komai sai tafiya akeyi, itace tayi connecting wayar ta da Aux ta kunna wakar Wizkid mai suna Daddy Yo. Haka ta rinka yi har suka isa ciki.
Sama sama tayi ma kowa, ita yanzu bata damuda kallon dasuke mata ba saboda bakin alkalami ya bushe yanzu Naufal nata ne.
Koda aka haɗasu ana masu nasiha akan hakuri da sauran al'amura na rayuwa, attention ɗinta yafi karkata akan TV while ita Deela kanta yana kasa.
Bayan nan aka kawo masu abinci suci, daga ita har Naufal sunci sosai saboda yunwa yana addabar su, tuwan shinkafa ne da miyan taushe sai kuma kunun aya.
Abba ne ya shigo yana neman Abla ta kaima Khattab abinci saboda rabonsa da gidan tun Miemie na raye.
Dama Naufal ya gama ci saiya tashi domin su gaisa, a garden ya iske Khattab yana wasa da Sunflowers.
Tausayin shi yake sosai saboda Miemie ta shuka da hannunta.
Khattab yana ganin Naufal ya mike da fara'arsa, hakuri ya soma bashi akan rashin zuwa bikinsa da baiyi ba. Acewarsa kwanan sa huɗu a asibiti sai dazu aka sallame shi.
Jaje Naufal yayi mashi sai yace su koma falon baki ya zauna, Naufal saiya koma ciki domin ya faɗa ma Abla inda zata kai abinci.
Yana zaune ya kifa kansa akan cinyarsa, baisan da zuwanta ba saiya ganta a gabansa. Baya ya matsa a firgice har saida ta tsorata.
"Haskena kin dawo ne?" ya faɗa a tsorace. Sai kuma ya fara mika hannunsa dake rawa yana so ya taɓa fuskarta yaji ko itace ɗin.
#NiDaDiyata
*Dedicated to all the family of this book, because yanzu mun zama yan uwa*
~Yarinya Mai DIMPLΣS~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 37 ✨✨✨
On the authority of Abu Dhar Jundub bin Junadah, and Muadh bin Jabal that the messenger of Allah said : "Fear Allah wherever you are, and follow up a bad deed with a good one and it will wipe it out, and behave well towards people." Tirmithi narrated the Hadith and said it was fine, and in another version, said ture and fine.
**********
Ikon Allah Abla ta tsaya gani, duk ya ruɗe babu gaira babu dalili, though ranta yana bata cewa kila shima yana ganin gizon da akace tanayida Miemie. Sai dai ba wani big deal bane dazai rude haka kamar yayi gamo.
Bata hanashi taɓa fuskarta ba saida itama ta kafa mashi ido kamar yadda ya kafa mata. Yana taɓata yaji mutum ne saiya sake baya ya rufe idonsa. Rufa ke keto masa duk ya firgita, saiga Naufal ya shigo.
“Yauwa Abla dama ke nake nema”
Kallon Khattab yayi yaga ya sukurkuce, Cikin damuwa ya soma masa magana.
“Lafiya kake zufa duk Ac dakin cikin nan?”
“I think shima yana ganin Miemie a fuskata ne” ta amsa a sanyaye
“Ohhh! Of course Abla ne, yes im not running mad” Khattab ya faɗa yana ajiyar zuciya a hankali, handkerchief fari ya ciro daga cikin aljihunsa ya share zufan Fuskarsa.
Da farko ya dauka yayi gamo ne, sai kuma ya sha hauka ya somayi. Zuwan Naufal ba karamin relief ya bashi ba. Ita kuma mikewa tayi ta bar wajen tana matse kwalla.
Abin ya fara isanta, hala mutane basu lura itama tana missn Miemie bane, duk inda taje sai an firgita kuma ba’a lura itama tana jin ciwon abun cikin ranta.
Shi kuma fasa cin abincin yayi saiya tafi gida kawai, kwanciyar rub da ciki yayi akan gadonsa. Kawai tunanin yanda Abla batada bambanci da Miemie ne yakeyi. Magrib aka kira saiya tashi ya wuce masjid.
A hanyar gate ya haɗu da Lili tana dawowa daga anguwa, da gudu ta karasa inda yake ta rungume sa. Dama rabon data haɗu dashi tun shekaran jiya.
“YaKhattab naji daɗin ganinka Wallahi”
“Na hanaki rikeni, wai meyasa bakya jine?”
“Toh fah ji wani sanabe, wallahi iyayi da kakeyi kamar baka jin dadi idan na rike ka bani mamaki yakeyi”
“Eh naji nidai sakeni kawai kinga masallaci zani kafin na makara”
“Anaso ana kaiwa kasuwa” tace saita sake shi. Harya soma tafiya wajen taku biyar haka saiya juya, “Lili” ya kirata.
Itama waigowa tayi tana rarraba idanu, “ya akayi ne Yaya?”