← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 48

Sashe 32

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yaji dadi sosai saboda da kanshi zaiyi bikon abinsa, ba fariya ba amma yasan ya kware a watsa kalamai. Abin ya daure mashi kai dayaga har yanzu bata sauko ba.

Shidai Fadeela daya sani batada riko amma yanda wannan ke kumbure kumbure. Zama yayi akayi gaisuwa da Anty Saudah, koda aka kai masa breakfast shayi kadan ya kurba.

Anty ta lura yana inda inda saita mashi magana, “Lafiya dai koh?”

“Dama bansan ko meta faɗa miki bane?”

“Ban gane me kake nufi ba?”

“Ina nufin ta faɗa maki dalilin zuwanta ne”

“Eh tace yanzu bakada wani sana’a sai gantali yasa ta dawo nan har Allah ya sauketa lafiya”

Shiru yayi, sai dai kuma yaji daɗi data rufa mashi asiri. Koba komai ta kara nuna masa ita mace ta gari ce.

Tashi yayi ya bar Anty wajen zaune saiya tafi ɗakin da Fadeela take. Ita kuma bayan ta bar falon laptop ɗinta ta kunna tana kallon wani horror film mai suna Rings.

Tanayi tana matse ido tareda rungumar pillow saiga Naufal yazo, ko sallamarsa a ciki ta amsa saita cigaba da kallonta.

Mamaki ya kamashi sosai saboda ko gaida shi bata yi ba, asalima haɗa girar sama dana kasa tayi tamau tareda tsuke bakinta. Yana tsaye a bakin kofa yaga batada niyyar mashi magana.

Shine ya soma magana kasa kasa cikin lallami da lumana, “Kinki kallona kuma ko gaishe ni bakiyi ba kin kyauta kenan, koma mene maki bai kamata ki dauki zafi dani........”

Bata bari ya karasa maganar ba tayi pausing film ɗin saita figi wayanta ta shige bayi tareda banko kofa ‘dam’

Abinda yasa ta wuce ta kyaleshi baifi yanda ranta ya ɓaci sosai ba, saboda tayi alkawarin randa zata bashi amsa sai yayi mamakinta but yanzu gasu Anty bata so suji.

Shikuma sororo ya tsaya shake da mamaki daya lura babu wasa a abinda takeyi, asalima kamar soyayyarsa ya fice mata a rai farad ɗaya. Haka ya rinka kallon hannun daya mareta dashi yana jin haushin kanshi saboda gashi yanzu ya kaishi ya baro.

Ranshi na mashi kuna saboda baisan yadda zai yi da ita ba, dayake bata taɓa daukar zafi dashi ba so baima san me zaiyi ya wanke kanshi ba.

Haka yayita tsayuwa gefen kofa ya jinjina da bango tareda daura hannu daya akan kwankwaso, ɗayan kuma ya dafe kai dashi. daya lura batada niyyar fitowa saiya fita, yana komawa falo saiya tarad da Yasmeenah tayi masa Missed calls kamar zata rusa mashi waya.

Haka ya tashi yaje with the aim Zai dawo anjima ya dauki Fadeela su tafi gida. Ita kuma saida ta tabbatar ya tafi kafin ta fito tareda komawa ta kammala kollonta. Murguɗa baki tayi tareda magana a fili, "Babu inda zani, zama daram dam"

Koda taji dawowarsa da daddare saita garke kofanta, yana turawa yaji karfi. Yafi minti uku tsaye yana tattara tunanin sa waje guda, “Abin yarinyar nan da gaske nefa!” ya faɗa cikin ransa.

Gwiwa babu kwari yayi hira kadan tareda cin abinci saiya wuce gida, yanzu babu mai kwabarsa yayi waya da Yasmeenah sosai. Ita kuma murna fal ranta duk tsammanin ta agaban Deela yake wayan.

Sai wani rangaji da kafa takeyi tanata mashi shagwaba, Sam Shikuma bai faɗa mata Deela ta gujeshi ba saboda yasan halinta na rashin hankali zata rinka ziyarar sa tayi making situation ɗinsa ya tabarbare. Kawai yace yayi handling komai bazata sake ba. Ita kuma harda samun waje wai sai Deela ta bata hakuri, wani irin kallo ya watsa mata kana ya soma magana a hasalce.

“Halan bakida hankali ne? Matana mother of my child kike so ta kiraki? Better watch ur tongue”

Kwafa tayi tana zumbure zumbure, dama kofar gidansu ne saita fita daga cikin mota tareda banging kofa. Tsaki yayi kana yace “Allah ya raka taki gona”

Da daddare ta kirashi tana neman sulhu saboda ta lura ya fita iya shege.

Kwana sunata tafiya babu alamar komawar Deela babu dalilin sa, kwance tashi yanzu satin ta biyu da barin gidan Naufal, tana jin zuwanshi zata bar duk inda take ta koma ɗaki ta rufe kofa.

Haka tana sallar isha’i take kwanciya, babu mai takura mata daga Abba har Anty kullum cikin mata hidima suke. Gashi ta murmure ta kara fresh abinta hankali kwance.

Yau Asabar tun takwas Miemie da Anty Saudah suka tafi islamiyya. Dama Abba a gidan Mama yake, Deela na zaune a falo sai gyangyaɗi ya ɗebeta.

Muryan Naufal taji a kanta, a hankali ta buɗe sannan ta sake rufewa. Murmushi yayi saiya cigaba da magana.

“Fadeela sarauniyar mata, babyna Matana na kaina, kece shugaba a cikin Matana a aljanna..... Haba babyna I’m sorry please”

“Nagane laifina please kizo mu tafi gidan mu, wallahi nayi missing dinki, your smile, jokes, care in fact everything about my sweet Other half”

Buɗe ido tayi domin ta kalleshi, green eyes dinnan Sai sheki sukayi. Kuma kana kallonsa kasan cewa yana cikin damuwa.
Idan baka sanshi ba zakaji tausayinsa amma banda ita, ita yanzu zuciyar indai akan shine toh a bushe yake kamar stock fish, aslima haushin sa takeyi. Dayake mata magana muryanshi kamar narkarkiyan dalma ne a cikin zuciyarta.

Zama tayi sosai ta gyara daga kishingiɗin, kallon up and down tayi ta watsar kana ta cigaba da kollonta. Shikuma yaje dab ta ita zai zauna tareda rike mata hannu.

Da sauri ta mik’e dukda cikin jikinta, yanda tayi kamar an soka mata mashi, a fusace ta soma magana muryanta yana rawa.

“Menene haka zaka taɓa ni? Baka burgeni ba! da sai kaje wajen matar da zaka aura saika taɓa ta”

“Haba babyna ki daina faɗin haka mana, nace am sorry fah”

“ Mai I’m sorry dinka zai kara min a jiki? Bazai kareni da komai ba kuma bazai rage niba. So I don’t need it”

“Nika mara akan wata karuwa da batasan darajar kanta ba balle na wani koh? ai duniyar nan babu wanda yayi min abinda kayi min”

“All the lies, deciet, betrayal for what? Haba Naufal! ban chanchanci haka ba a wajen ka. I thought I meant more than this to you”

Kuka kawai yaci karfinta, shikuma jikinsa yayi sanyi tareda la'asar, saiya matsa wajenta zai taɓa ta, da sauri daja baya harda tuntube. Cikin kuka ta soma magana a hasalce, “karka kuskura ka taɓani, you’re done touching me”

Cak ya tsaya bai iya motsi ba, yasan cewa yayi gaggawan ɗaukan hukunci but ya kamata subar komai a past tunda abin yafi two weeks da faruwa.

Rufe ido tayi tanata masa bala'i babu kakkautawa, yanda kasan ta haɗiye tabarya haka take jin kanta a tsartsaye.

“Wallahi  ban taɓa tunanin haka zai faru dani ba so soon, kaci amanar soyayya Naufal. Idan haka ake soyayya to I don’t want to have anything to do with it”

“Baby please kiyi hakuri nasan na bata maki rai, but I promise to do better”

“Don’t you dare lie to me kana so kace kasan yanda nakeji, you have no idea how I went through all the Loneliness, Kawai ka baka damu ba. Duk abinda nake maka baka taba gani ba”

“Duk rashin mutuncin da kake min ban taɓa nuna bacin raina ba, kullum hakuri nakeyi. Ko ance maka banida zuciya soso ke wajen. Amma na shanye komai saboda hakuri shine zaman aure”
"Shine zaka mareni akan......"

Anan kuka yaci karfinta tayi shiru da magana saidai rasgar kukanta, muryanta ya soma dishewa gashi karfin jikinta yana raguwa. A hankali ya soma magana cikin nadamar halinsa, “please baby I’m sorry, kizo mukoma gidanmu, our home mu haife babyn mu”

Dagowa tayi cikin masifa, “ Home! Wat home? Gidan da bakasan komai a kaiba saboda baka zama kun tafi gantali da Aminu office”

Daga nan ta juya ta wuce tareda barin shi a wajen, da sauri ya sha gabanta.
“Wallahi ka matsa min If not duk me nayi maka kaika ja ma kanka” saita kalle wani golf stick dake gefe, shima yana kallo saiya matsa mata kafin ta illanta shi.

Kawai tunanin gwara yaje ya faɗa ma Mommy gaskiya, a dawo mashi da matarsa. Ita kuma rastashi tayi ta wuce hanyar ɗakinta.

Binta ya cigaba dayi amma tayi burus dashi, tana tafe tana hawaye sanadiyar tuna irin rainin dayayi mata.

Buɗe kofa tayi ta shiga daki, ta juya zata rufe kofa saita ganshi tsaye gaban wajen, fuskarta babu annuri ta harɗe gira kana ta fara magana confidently, “Ni da kai, we are done”
Karab ta rufe kofar ɗakinta tareda saka key.

#NiDaDiyata

*I’m Dedicating this page solely to all the fans of NI Da Diyata, I really appreciate your love and support. Your awesome comments keep me going all the time. Allah ya barmu tare har mugama lafiya Amin*

*Ya kamata Fadeela ta koma, kokuma ta zauna har saita haihu?*

*Waiting for your answers*

*All Rights Reserved*

💥∂ιмρℓεs💥
[13/2 07:02] Dimples: ©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 30 ✨✨✨

On the authority of Abu Hurayrah (may Allah be pleased with him), who said that the Messenger of Allah (peace be upon him) said: When Allah decreed the Creation He pledged Himself by writing in His book which is laid down with Him: My mercy prevails over my wrath. It was related by Muslim (also by al-Bukhari, an-Nasa'i and Ibn Majah).

**********

Kwanaki sai wucewa sukeyi babu alamar komawanta, da kanshi ya tafi gidan Grand Kadi ya faɗa masu abinda ke faruwa.

Mommy ta kirata tayi mata faɗa sosai kuma tace she is disappointed in her, duk tarbiyan da sukayi mata saida ta watsa masu kasa a cikin idanu.
Grand Kadi ne yace ayi mata uzuri  gwara ajita bakinta. Washe gari suka tafi gidan gona inda Fadeela take, Naufal yaci shadda dakarkiya fari ɗinkin babban riga.

Yana tafe yana raha tareda full confidence yau zai tafi da matarsa. Kowa ya taru a falo, Big Daddy, Grand Kadi, Abba, Mommy, Mama sai kuma Anty Saudah.
Sannan saisu Deela da Naufal. Grand Kadi ya buɗe taro da addu’a sannan ya fara faɗin fa’idojin aure.
Daga nan sai Big Daddy ya fara magana akan batun auren su, Fadeela aka tambaya menene ainihin abinda ya faru tsakanin su.
Chapter 32 · 0% Book details