← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 48

Sashe 20

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Babu wanda baizo gaishe da Fadeela ba including Miemie, saboda tana jin Anty yar gayu batada lafia sai kan ya fara motsawa. Dole aka kawo ta kuma cikin ikon Allah babu handcuffs kuma batayi anything funny ba.

Ita tayi ɗawainiya bata abinci da ruwa, ita abin dariya ya bata saboda ciwon K’afa takeyi ba na hannu ba, kuma ta fara taka kafan kaɗan kaɗan.

Kana ganin ta cikin kwanakin nan kasan cewa yar so ce kuma ba abin wulakanta wa bane. Hatta Big Daddy da iyalansa Ba’a barsu a baya ba, ko Alhaji Sulaiman baban Sadeeq yaje dashi kanshi Sadeeq da matarshi.

Abinci kuwa mai aikin Anty Saudah ke kawo three square meal tareda Mai aikin Mommy. Itama Jawahir duk sanda taje saita kai masu wani abu.

Kwata kwata Naufal baya jin daɗin asibitin idan Anty Saudah da Mama nanan, yafi son idan sun tafi gida ya zauna da Mommy Asha hira.

Bilqees ke kwana da Fadeela thru out. Ni Naufal wajen 6am na isa asibitin kafin su Mama su rigani zuwa asibitin su kama kirana ‘Mugu’ bcs na tsana sunan har cikin raina.

5pm....

An haɗa kayan Fadeela komai da komai ana jiran Doctor ya gama prescribing magani ya sallame su. Itama ta ɗan warware tayi ɗan armashi abinta ba kamar yadda aka kaita ba.

Mama ce tace saidai Fadeela ta wuce wajenta ta k’ara murmurewa saboda tasan halin Wa’e saita kalleshi ta gefen ido. Idan ana sabo da tozarci ya riga ya saba dashi dis past few days saboda sun mayar dashi laughing stuff, mocking ɗinsa anyhow kawai sukeyi.

Saidai ba fault ɗinsu bane, dama komai kayi akwai reckoning ko a duniya ko lahira baki ɗaya. Da bai zubar da girman da Allah ya bashi ba yayi abin tsiya da haka bai faru ba. But he promised to do better.

“Nifa ba inda za’a je min da mata” ya faɗa masu.

Mama ta dubeshi a kaikaice, irin duban hadarin kaji “Toh mara kunya hanamu” ta hayayyakoshi.

“Ai dama da bakice haka ba, wajena zata zauna kinsan sun saba da Miemie” Anty Saudah ta faɗa.

Haka suka rinka jani in jaka shi babu wanda zai tafi mashi da matarsa wani wajen.

Fadeela na daga kwance tana jinsu duk rai a jagule, tsakani da Allah tunda yace he will do better gwara a barta ta koma ɗakin ta. Sai wani zuciya yace mata “Karya yakeyi kawai bauta yake so ta koma tana yimashi”

Kauda tunanin tayi bcs aure ibada ne kuma ladanta yana sama wajen Allah. Indai da aure tsakanin su gwara tayi masa koma menene muddin bazai kare hakkin addini ba.

Kowa yasani Allah yana tareda masu hakuri Besides Hausawa sunce mai hakuri shike dafa dutse har yasha romonta.

Anty Saudah ta dafa mata kafaɗa “ ‘yata! Zaki bini muje gidan gona?” Bata ce mata komai ba illa Sinna kai kasa tana wasada hannunta.

“Sauraron ki nakeyi”

Daga ido tayi saita lura kowa kallonta yakeyi, musamman shi gwaskar ya kafa mata ido babu kiftawa. Sunkuyar da kai tayi tareda cewa, “Anty duk abinda kuka ce shi za’a yi”

Kwafa yayi ranshi ya bala’in ɓaci bcs tunda suna Santa idan tace zata zauna dashi babu mai hanata. “Ko kai bazaka zauna da kanka ba idan an barka” wani siririn murya ya raya mashi.

Ita kuma koda wasa bazata iya cewa tana son zama da mijinta ba bcs rashin kunyarta bai kai haka ba besides suna kwatan mata yancin tane.

Daidai lokacin su Grand Kadi da Mommy suka shigo, Naufal bai bari sun natsa ba ya fara masu k’orafi akan za’a rabashi da matarsa.

Murmushi Grand Kadi yayi, “ karka damu babu mai hanaka tafiya da matarka, kai ka shigo da ita kuma kai zaka fita da ita”

“Woooow!” ya faɗa tareda naushin iska. Ko kunyar kowa baiji ba ya nuna murnarsa a fili. Harda shaking hannun Grand Kadi yana godiya.

Dariya yake masu Anty Saudah domin yaci argument ɗin, ita kuma takaimai dukan wasa a kafaɗa sai shikuma ya kauce tareda saurin barin ɗakin.

Fadeela sinna kai tayi ba tace komai ba but murna fal ranta zata koma wajen Other Half ɗinta.

An tarasu su biyu an masu nasiha akan aure mai shiga jiki, idan kayi shi da kyau ka kuɓuta, if not Zai kaika ga hallaka. Aure ba abin wasa bane kuma yana cikon manyan sunnonin Manzan Allah SAW.

Zo mu zauna dama zo mu saɓa ne, kuma mistakes are what makes you human but Yanda Kayi handling ɗinshi makes u a better person.

Wajen 30 mins kowa na tofa albarkacin bakinsa kafin aka shi masu albarka suka wuce.

Dama da safe Bilqees, Abla harda Miemie sunje gidanta sun gyara mata tsap. Ita Miemie tun sanda ta fara fita wajen Anty yar gayu aka fara gane kanta, tana shan magani akai akai kuma bata gardama.

Thou ba’a barinta alone, sun shirya ma Fadeela komai hardasu laundry aka tayata.

Shikuma ya tsaya Vanilla joints ya siyan masu kayan lashe lashe sai kuma ya siyan masu kaji gasarshe na kan titi.

Shi Bawai Santa yakeyi ba but kawai after everything he put her through, tayi deserving something sweet. Ita tana mota tana mamakin yanda yakeyi kamar ba shiba.

#NiDaDiyata

*Big shout-out to all the fans of this book, Nagode sosai Allah ya bar zumunci. Especially those dana keda direct contact dasu kamar su UmmieeJafar Novels, Xarah Novels, The Queen Bee, Deyart Novels, Hamagee Novels, Billy Galadanci Novels, Marubuci, Rash Kardam Novels, Xoubhie Novels etc*

#TeamNiDaDiyata

#TeamFadeela
#TeamNaufal
#TeamMiemie
#TeamKhattab

*Ni dai TEAM NAUFAL ce*

*All Rights Reserved*

💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 20 ✨✨✨

*Lesson*

‪Patience is when you're able to conquer that angry voice in your head which wants to take revenge on others who hurt you or are mean to you!‬‬‬‬‬‬

Mufti Ismail Menk

Ibn Mas'ud (May Allah be pleased with him) said: The Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "He who says: 'Astaghfir ullah-alladhi la ilaha illa Huwal-Haiyul-Qayyumu, wa atubu ilaihi (I seek the forgiveness of Allah, there is no true god except Allah, the Ever-Living, the Self- Subsisting, and I turn to Him in repentance),' his sins will be forgiven even if he should have run away from the battlefield (while he was engaged in fighting for the Cause of Allah)."[Abu Dawud, At-Tirmidhi and Al-Hakim

**********

CYPRUS

A East ɗin Mediterranean akwai wani Island da ake kira Cyprus, chan daga wajen Arewan garin akwai wani k’aramin gidan gona wanda ya k’unsa ɗakuna biyu da bayi uku tareda da kitchen daya.

A cikin falon akwai dinning area, drinks cabinet da kuma chimney.

Wani matashi ne wanda bazai kai shekara 25 a duniya ba ya shiga cikin gidan, hannunsa shak’e yake da itatuwa kuma ya nufa hanyar fireplace ɗin falon, yana zuwa wajen saiya dire tareda ajiyar zuciya.

Kayan sanyin dake jikinsa ya fara k’okarin ragewa, safar hannu ya cire sai kuma maufler tareda head warmer.

Yanzu fuskarshi ya bayyana sosai wanda da baka ganin komai sai k’wayar idanu. Jacket ɗinsa ya cire tareda ajiye wa akan couch sai ya rige daga shi sai sweat pants tareda T-shirt.

Kai tsaye dinning area ya wuce ya haɗa ma kanshi shayi a wasu fararen Chinese wears. Yana sha yana lumshe ido,Saida ya zuba ma kansa kofi biyu na ruwan bunu kuma ya shanye tas.

Tsam ya mik’e tsaye ya wuce wajen wani calendar haka wanda yayi kacha kacha da rubutu. “Day 190” ya rubuta a bangon saiya wuce hanyar bedroom ɗinsa ya shiga bayi direct.

Kallon kansa ya tsaya yi a mirror ɗin bayin, duk ya canza kamanni ya susuce. Rabon daya aske gashin kansa kona gemunsa tun yana Nigeria. Yanzu Afro yayi tsawo kamar jirgi ya doso gari ga kuma fuskarshi jaɓa jaɓa da gashi.

Mutane biyu kawai yake tausaya mawa, na farko dai Mahaifiyarsa wanda yasan tana cikin matsananci tashin hankali akan rashinsa.

Na biyu kuma Haskensa Miemie, rashinta yayi sanadiyar gudunsa. Shifa bazai iya zama gari ɗaya babu ita yasa kawai ya tafi.

Wanta yayi making ɗinshi clear bazai taɓa bashi ita ba saboda wasu dalilai nashi. Shikuma idan ba Miemie bazai zauna da wata mace a inuwar aure ba.

Babu makawa idan yana gidansu za’a tursasa shi akan ya aure Lili which bazai iya buɗe idonsa ya ganta ba.

Wanka yayi sannan ya shirya cikin Long sleeve da jens wando, ɗayan ɗakin opposite nashi ya wuce tareda shiga. Maidaidacin ɗaki shake da kayan computer kala kala tareda sauran abubuwa daya jibanci haka.

Zama yayi akan wani kujera dayake gaban babban computer. Kunnawa yayi sai wani rubutu ya fito inda aka rubuta NTI TELECOMMUNICATIONS.

Nan ya saka password ya soma aiki gadan gadan, kana ganin yanda yake aiki cikin kwarewa kasan cewa ba sabon hannun bane.

NIGERIA

“Inspector mun samu leads akan shi” wani Sergent ya Shiga office ɗin IG tareda mashi salute.

Ajiye takarda yayi dake hannunsa sannan ya gyara zama tabaransa.

“A Ina ne wajen?”

“Sir Chan Cyprus ne, akwai wani ICT company dayake ma aiki. Toh wani ɗan department ɗinmu dayayi tracking hotonsa a cikin database ɗinsu”

“Innalillahi, tuntuni muna nemasa amma yana chan Cyprus. How true is this information?” IG ya tambaya.

“Anyi kowane bincike kuma an gane Khattab ne”

“Kuma kun tabbata anan yake aiki ba scam bane?”

“Affirmative Sir”

“Okay ku shirya mana Visa muje Cyprus muga gari”

2 days later....

Khattab ne ke cikin Garden ɗinsa yana gyarawa, dayake Miemie ta koya mashi yanda zaiyi shuka da sauran su so bashida matsala wajen yi yanzu.

Saboda yana Missing Miemie in the first place Yasa ya siya gida mai yanayin gidansu watau na gona. Yana cikin gyara sunflowers da kuma Hydrangeas sai kawai yaji an shigo mashi gida, bai yi kokarin dubawa ba saboda mutum ɗaya ya sani watau makwabcin sa Mr Kareem.

Tafiya yaji ta wajen ɓangaren dayake Kuma yasan Mr Kareem bazai zo wajen ba. A hankali ya ɗaga tareda juyawa, fuskar da bazai taɓa manta wa ya gani. IG ne yake tafiya wajen dayake.

Nan take gabansa yayi mumunar faduwa, da sauri ya mike tsaye tareda da sakin shovel ɗin hannunsa. Jikinsa rawa ya somayi baisan mai zaice ba.
Chapter 20 · 0% Book details