← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 48

Sashe 15

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Please idan Kinga dama ki rinka yin busy body idan kina abu, mutum sai shegen nawa kamar kunkuru” Ya faɗa yana wani yatsine fuska.
Tana tafe tana gunguni tareda magana ciki ciki, “Bani bace kunkuru saidai......” kafin ta karasa maganar saiga shi agabanta yana huci kamar mayunwacin zaki.

“Saidai wa?.......”  ya tambayeta.

#NiDaDiyata

*Corpers wee! Shout-out to all corpers I know the struggle is hard esp now that dey have not paid our allowee, we will still survive biko! Special shout-out to 2016 Batch B stream 1 most esp Ummunah Bende corpers. If you are reading this you are wrong! Is that clear!*

*All Rights Reserved*

💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 16 ✨✨✨

Abdullah bin 'Amr bin Al-'as (May Allah be pleased with them) reported: A man asked the Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam): "Which act in Islam is the best?" He (Sallallahu 'alaihi wa sallam) replied, "To give food, and to greet everyone, whether you know or you do not."[Al-Bukhari and Muslim].

********

Rufe ido tayi ta kasa haɗawa dashi tareda karkarwa, ji kawai tayi an damk’eta. Ihu ta tsandara saboda rik’on dayayi mata babu sassauci kuma abinka da farar mace babu makawa hannunsa saiya nuna.

Still bata buɗe ido ba kawai hawaye suka soma fitowa kamar a bakin teku.

“Bada ke nake ba? Nace karasa maganar mana. Ashe ke karamar mara kunya ne. Tun ba yau ba nace ki hankaltu dani.”

“Idan nace zan rinka dukan kine kawai kasheki zanyi saboda bakida wani abun duka tunda bakifi loma ɗaya da rabi a haɗiye kiba. Kuchaka kawai!”

“Sai shegen iya rashin kunya ga kuma shegen tsoro kamar farin kura. Da an riskeki sai ki fara kukan munafunci kamar ana kashe ki..... Mts”

Saiya wurga ta k’asa ta faɗi wanwar. Baka jin komai sai Sheshek’ar kukanta kawai tana jan majina a hankali.

“Idan kinso gobe ki kara, Karkiga yanzu na kyale ki” ya cigabada sababi har ya koma wajen couch ya zauna. Kafa ɗaya kan ɗaya ya daura yana kallon TV dake aiki. Wannan karon ESPN ya saka.

Ita kuma a hankali ta tashi jiki babu kwari rai a jagule tayi hanyar dining, karap karap kake ji karar takalmi ta isheshi kuma da gangan takeyi.

Ko cooler da karfin gaske take buɗewa kamar zata karya murfin, haka take amfani da chokali karap karap ita kanta ta damu balle shi. She was just acting clumsy Sai ɓari takeyi ta ishe kowa.

Tsaki yakeyi saboda duk ta cika mashi kunne, a fusace ya juyo rai a bace yana nuna mata ɗan yatsa.

“Ke dalla meye haka ba zakiyi abu a natse ba kin cika min kunne”

Puppy eyes tayi mashi tareda cewa, “Kayi hakuri yaya bansan yana damunka ba”

“Okay yanzu kin sani gwara ki bari kafin na damk’eki”

Bata ce komai ba illa sinna kai tana dariya, tabbas taji daɗin abinda tayi tunda da gangan ne. Cikin ruwan sanyi zata rinka frustrating ɗinshi.

Ta jera mashi abinci wanda multi-colored rice ne da stew ɗin Cat fish. Sai kuma Coslow wanda yasha Macaroni da hanta. Drink kuma coconut ne aka markaɗa da shinkafa na tuwo tareda pineapple.

Karap karap ɗin slippers ya sanar dashi gatanan zuwa, dab dashi taje ta tsaya kamar zata auka mai.

“Yaya ga abincin na zuba maka”

Harda bazai amsata ba sai kuma ya canza ra’ayinsa.

“Sai kin fado jikina zan san kina min magana?” ya tambaya yana mata kallon raini.

“oh sorry!” saita matsa baya

Shiru sukayi for some seconds saitace, “Akwai abinda zanyi maka kuma?”

Bai tanka taba saiya mike tsaye, yanda dunkaro ta idan da batayi saurin matsawa ba daya banke banza.

Hawa yayi dinning ya zauna, yanda ta jera ya k’ara burgeshi. Ita kuma dama ta ɗiba nata yana kitchen. Karap karap takeyi harta wuce ta shiga kitchen, wannan Karon harda juya mai jiki.

Shiru yayi saboda ya shaka matuk’a, “indai jiki ne toh I’ve seen better” ya faɗa a ranshi. Sannu a hankali ya gama cin abinci saiya tashi ya wanke hannu, sink ɗin wajen yayi hooking yaki budewa so dole yaje wani wajen.

Nearest to the dinning area kitchen ne, ranshi baiso ba amma haka ya hakura ya tafi.

Ita kuma ta gama cin abinci har ta fara wanke wanke sai Naufal ya faɗo mata a rai. Dariya ta tuntsire dashi tareda magana a fili, “Wai ace mutum bashida sana’a sai faɗa, dage yafi shi hakuri.... Haba kullum faɗa kamar a Syria aka haife shi”

“Ina jinki” Ya faɗa.

A tsorace ta juyo tareda sakin plate ɗin hannunta, tas kakeji ya fashe. Neman wajen guduwa taso yi amma shike hanya. Tabbas yau kashinta ya bushe saboda saita daku.

Narai narai tayi da ido bakinta na rawa amma babu abinda ke fita. Zufa ya soma yanko mata duk ta fita hayacinta.

Takowa ya somayi tareda smug face, kana ganin shi kasan yana shirin mugunta. Sannu a hankali har ya kai wajen datake ya tsaya.

Da hannu yayi alamar ta matsa mashi, wucewa yayi ya wanke hannunsa saiya bar kitchen ɗin.

Shi abinda yasa baice komai ba saboda yanda ta tsorata, ihu yayi mata zata iya haɗiye ranta ta mutu ta jawo mashi bala’i babu gaira babu dalili.

Amma tabbas maganar datayi ya taɓa shi, wai yau shi ake ce ma dage da kuma yana faɗa kamar haihuwar Syria, lallai!

Ita kuma sororo ta tsaya tana tunanin abinda ya faru few seconds ago, gaskiya ya bata mamaki matuka saboda bata sanshi da hakuri ba, wani zuciya ya raya mata kila tayi Azkar da kyau ne.

“Gaskiya ba mamaki!” ta faɗa a fili saita ɗuka kasa ta fara gyara ɓarnar datayi. Dama wayanta yana gefe sai kawai ta dauka ta kunna wakar Nazeefi Asnanic mai taken Ga Amarya, Haka ta rinka rero wakar kamar ita ta rubuta mashi.

Dakinshi ya koma ya zauna akan gado yana tunani, faɗa Sam sam ba ɗabi’arsa bane kuma kowa ya shedeshi. But tun haɗuwarsu yake wasu shikashikan rashin mutunci babi babi.

“Ka manta Bad luck ɗin dake binta ne ya canza ka” wani zuciya ya raya masa.

“Hakane fah” ya faɗa a fili. Tashi tsaye yayi saiya canza kaya.

Farin Boyel ya saka wanda aka ɗinka jumper da wando. Sai ya haɗashi da coffee Brown hula da takalmi. Turaren Ralph Lauren ya fashe jikinsa dashi har ya fara choking saboda yawansa.

Yaci kwalliya kuma yayi kyau sosai a matsayin shi na kyakyawa, wannan green eyes ɗin yana glimmering. fine guy san kowa, ko makiyan sa basa kushewa. Ni kuma Dimples nace “ Na Fadeela bada kanka a sare!”

Yana tafe taku dai-dai zashi gidansu Fadeela yayi godiya akan karamcin da suka yi mashi. Abba ya gargaɗe shi akan dole saiya je ya gode masu, kuma shima yana so ya daki tsuntsu biyu da dutse daya.

Tunda ya lura Mommy tana sanshi gwara yayi mata shishigi saboda koda ta kai k’ara babu mai gasgata ta.

********

A chan gidan lambu kuwa, Miemie ce ke gyara flowers ɗin datayi planting da kanta. Sun flower ne kuma kullum saita duba su, ta dauki wani flower pot sai kuma ta sake shi k’asa ya faɗi ya fashe.

Bata ko damu ba saima takashi da tayi kurmus. Kana ganinta kasan ‘yan kanta sun motsa.

Tunda baya Naufal ya bar gida take jin kanta wayam, tunanin Khattab kawai takeyi. Ya diran mata kamar kibiya batada wani katabus sai shi.

“Ba Ya Naufal, ba Ya Khattab.... Toh wallahi bazai yiwu ba”

Komawa cikin gida tayi wanda ‘yan biki sun ragu yanzu. Abla ta gani a hanya saita ce mata, “Kinga Yaya Khattab kuwa?"

Harara ta watsa mata kafin tace, “Eh yana buje na” sai tayi wucewarta.

Miemie bata ce komai ba illa wucewa ɗakin Mamanta watau Anty Saudah, “mama ki kaini wajen Yaya Khattab dan Allah”

Shiru Anty Saudah tayi kafin ta fara magana a hankali, “Mamana yau Kinsha magani kuwa?”

“Ni wajen Yaya Khattab zaki kaini....”

“idan Kinsha magani sai muje koh”

“Wallahi ban yarda ba, nasan bazaki kaini ba” Sai kawai ta fashe da kuka. Anty Saudah da sauri ta ɗauko magani domin ta bata atleast su samu saukinta.

Fizgewa tayi daga hannun Mamanta ta zubar dashi ta rinka takawa da kafarta tana yi tana kuka tayi kacha kacha da wajen.

“Bazan shaba” ta faɗa tana rusa kuka a ɗuk’e. Nan take ran Anty Saudah tashi.

Number ɗin Naufal ta soma nema, bugu ɗaya, biyu, uku saiya ɗauka. A gurguje tayi mashi bayanin komai. Nan take ya yi hanyar gidan saboda yabar gidansu Mommy kenan zai koma nashi.

Yana tafe yana tunanin condition ɗin Miemie bcs sun ɗade batayi tuburan ba.

Bai rufe k’ofan motarshi ba da sauri yayi cikin gida, yana isa wajen yagasu Abla anyi charko charko a waje saboda Miemie tace bata san taga kowa.

Tana zaune ko Mommy ɗinta ta kasa zuwa wajenta kafin ta mauje ta, Kiran sunar Miemie yayi a hankali tareda tura kofa.

“karka matso kusa dani”

“Calm down Lil sis,nine fah”

“I hate you” ta faɗa tareda kuka sosai.

“Kace min Yaya Khattab yayi min sallama ne, saboda ka maida ni mahaukaciya koh?”

Shiru Naufal yayi ya rasa me zaice kafin ya faɗa wrong thing tayi losing mind ɗinta hauka yazo gadan gadan.

Ita kuma ta kifa kai akan gwiwa sai kuka takeyi mai tsuma rai. Kawai saita mike tsaye tace, “Muje ka kaini wajen Yaya Khattab”

Zuwa yayi dab da ita ya ce babu inda zata. Wani irin kukan ta somayi kawai saita ruga window ta fara buga kanta dashi, duk da glass ɗin wajen ya fashe sai karfe Still bata daina ba.

Yaya Khattab ta rinka maimaita wa.

Duk yanda Naufal yayi kokarin kwanceta yana so ya gaza mashi. Tausayinta yake matuka saboda yasan zafin so.

Fincikarta yayi ya watsar a Kasa, jini ke fito mata ta hanci ta baki gashi kuma daga kanta yana gangaro wa. Kuka takeyi sosai tana kiran Khattab da muryanta daya fara dishewa, idanunta sunyi jazur kamar garwashi saboda wahala, duk ta galabaita a hankali takeyi.

“Kashe kanki kike so ki yi?”

Ko kallon shi batayi ba kawai tana kuka ne, duk abinda akeyi su Anty Saudah da Abla ana gefe ana kuka. Gashi Abba ya tafi Kano.
Chapter 15 · 0% Book details