← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 48

Sashe 27

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Tsoron me? Kana ganin Mommy ta fara biye ma zigin kawayenta wai bamu jin magana, shine waccan satin Ina bakin varenda ina busa sigari sai kwastam wai karna kara sha a cikin gidanta" Huzaifah ya faɗa duk ranshi a bace, daga nan saiya zuka Wiwi ya hura ta hanci da baki cikin kwarewa.

"Dama nazo na ara lighter ne amma tunda kuma sana'a kukeyi bari na zauna muyi tare" Hilal ya faɗa yana kanne ido.

Haisam ne ya tashi ya saka sakata a kofa, yana juyawa suka kwashe da dariya su uku. Sai Hilal ya fito da hodar iblis.

Tsaki Huzaifah yayi sai yace, "Dalla Meye haka? Sai ka rinka bata kudinka akan wannan abu"

"Mallam ina ruwanka? Kudinka ko nawa? Baka san daɗin abinnan bane saboda idan ka fara baka iya denawa. Ko gidan ka zaka iya sayarwa akan ka siye shi" ya amsa mashi.

"Nidai bazan iya cire kudina in siya wannan yar hodar ba, gwara nayi ta amfani da Wiwi cikin sauki" Haisam yace.

"Shine ai Danuwa" Huzaifah ya amsa yana dariya saiya mika ma Haisam hannu suka sha.

"Ku kuka sani, ni dai yanzu na fara" Hilal ya faɗa tareda buɗe hodar sa. A kasa ya barbaɗa kan tiles ya soma sinsina yanayi yana jan numfashi da karfin tsiya ga idansa jazur.

Saida yayi wajen sau uku sannan ya kishingida yana hutawa kamar wanda yayi aikin karfi. Sai ya soma jero magana mara kan gado.

"Yanzu naga Babe ɗinnan, sa'a taci yau juma'a kuma bana iskanci ranar danayi maganinta"

"wace yarinya?" Haisam yace

"Wanda ta mare Huzaifah mana" saiya faɗa yana babbaka dariya, ihu ya kwarara kafin ya cigaba da magana, "Ba'a haife macen da zata mareni ba, idan na fara dukanta kamar Allah ya aikeni in kasheta"

Daga nan saiya sake ɗukawa ya sinsina hodarsa sau ɗaya kana ya dago kuma akwai wani a hancinsa amma bai goge ba.

"Wallahi gaskiya ake faɗi kafi hankali cikin mu, saboda yanda bakayi mata komai ba" Hilal ya faɗa.

"Ai da nine ta mara wallahi ɗakinta zanje nayi yanda nakeso a jikinta, gobe bazata sake" Haisam ya faɗa.

"Allah yayi maka albarka, nima abinda na faɗa kenan... Amma wancan ya tsaya kamar wani soko" Hilal ya chapke.

Saidai Huzaifah baice komai ba yanata busar Wiwi, Saida ya gama kana ya dauko Shisha ya fara dashi, ahankali ya soma magana, "Gwara ku daina tunanin ta saboda Daddy yace zan aureta"

Ciza yatsa Hilal yayi saboda baiso daya ji labarin ba, dama cikin yan kwanakin nan yakeso ya far mata tareda gwangwaje wa a jikinta saboda indai haduwa ne to tayi.

Dariya Huzaifah yayi yana nuna Hilal kana ya soma magana, "Musamman kai nasan ka iya maita tun wuri nayi maka iyaka da matana"

Sosa k'eya yayi saiya manne tafin hannunsa biyu kana yace, "It's all good, ba matsala na kyaleta. Amma ba haka rai yaso ba, gaskiya anfi sanka à gidan nan"

Haisam ne yace, "toh amma babu tastin?" ya kalle su yana warware idanu. Pillow guda biyu Huzaifah ya wurga mashi suna dariya.

Yasmeenah ta isa wajen aikinsu Naufal ta rasa me zatayi, babban gini ne mai bene da yawa kuma akwai office daban daban. Ta fito daga motarta ta rufe harta soma tafiya ɗaya ɗaya cikin kasaita.

Naufal ta gani yazo wucewa shi baima lura da ita ba, da sauri ta tsayar dashi. "Hello! Baka gane ni bane?"

Saida ya ware ido da kyau kana ya tuna, baiyi murmushi ba kawai ya soma magana. "Ohh! Allah sarki! Sannu"

Murmushi tayi saita taka taje gabansa, "Ina wuni ina gajiya?"

"lafia" ya amsa.

"OMG! Locacin lunch yayi Muje na siyan maka mana saboda na biya taimakon daka min."

"Karki damu dan Allah nayi badan komai ba"

"Noo ni ban yarda ba, I insist please. Karka yi turning ɗina down mana. Just lunch ne Fah" ta faɗa tana kanne ido.

Haka kawai ya hakura yace suje.

Ita kuma Fadeela tayi tuwon shinkafa da miyan egusi wanda yasha ganda da busharshen kifi. Wani mai masu wanki ta kira kana ta bashi dari biyar akan ya kaima Naufal abinci office.

Yana zuwa baiga Naufal ba haka ya maida abincin gida, sai ta gwada wayarsa amma ringing sau uku bai ɗauka ba. Shiru tayi tana tunanin inda yaje, kiran wayar Miemie tayi kuma akace mata baya wajen.

Abinda yake daure mata kai shi ne yau yanada aiki da ko fita daga office bazai iya ba shine tace bari tayi surprising ɗinsa da abinci gashi kuma babu shi babu dalilin sa, wani zuciya ya raya mata kila ya fita da Aminu ne, tabbas taba kanta amsa.

Su Yasmeenah an samu abin so, rufe motarta tayi ta shiga motar Naufal wani Benz yar yayi GLK 350. Sai yauki take masa suna tafiya, shi haushin sa ɗaya abu yazo dauka motarsa gashi wayarsa yana office.

Sun isa Larema zasu ci abinci, shi shinkafa yace akawo mashi duk ya kagu ya bar wajen, ita kuma sai zuba turanci takeyi tana salo. Daga karshe saita ce akawo mata chips da kebab.

Har waiter ɗin ta tafi sai Yasmeenah ta kirawo ta " I like my chips the way I like my men, hot and brown" saita kanne mashi ido.

Wayancewa yayi ya kawar da fuska. Bayan an kawo masu abinci suka ci sukayi nat, Naufal ya tashi ya biya sai Yasmeenah ta fara kukan shagwaba wai ita zata biya gashi yayi mata wayo.

Hakuri ya soma bata amma ta kafe sai buga takalmi takeyi a kasa, ji kakeyi kwas kwas tana taramasa jama'a. Daga nan tace saidai wata rana su sake zuwa ta biya. Dole ya yarda, daga nan juya mashi bayanta ta tafi hanyar mota cikin salon rausaya.

Sun koma office ɗinsa saita ce "Yanzu yaushe zan kara ganinka"

"Yaushe kike so?"

"ko anjima bai dameni ba"

"No saidai within the week"

"Toh babu damuwa, Im Yasmeenah by the way"

Daga nan su kayi exchanging number kana kowa ya tafi, da sauri ya shiga domin yaga wayarsa. Missed call ɗin Fadeela ya gani dama yana kyautata zaton haka.

Da sauri ya bar office yayi hanyar gida, yana isa Fadeela ya gani kwance a kan 3 seater sanye da A shaped atampha ɗinkin gown.

A hankali ya tadata saboda barci ya soma dibanta. Murmushi tayi saita ja masa kumatu, "Baby harka dawo?"

"Eh nayi missing ɗinki yasa na dawo da wuri"

Murmushi tayi tana kokarin tashi, "Muje kaci abinci"

"Sorry baby Yanzu Aminu ya Kaimu muka ci shinkafa"

"Ni gaskiya zan kira Aminu na bashi warning ya daina kai mun miji yawon cin abinci, toh yanzu ya zanyi da wanda na dafa?"

"Baby sai muci anjima bazai baci ba"

Murguda baki tayi ranta baiso ba, suna makale da juna suna tafe zasu ɗaki sai tace "Other half akwai abinda ya faru yau ne?"

Gabansa faduwa yayi, miyan bakinsa ya bushe, da kyar ya saita kansa kafin yace , " Babu abinda ya faru, kinsan bazan ɓoye maki komai ba"

"Other half na sani mana, dama kawai jikina yana min wani iri ne"

"Karki damu Baby babu abinda ya faru kuma babu abinda zai faru. Jira yakeyi sukai daki domin yayi deleting number ɗin Yasmeenah da komai daya jibance ta.

#NiDaDiyata

*All Rights Reserved*

💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 26 ✨✨✨

Narrated Ibn 'Umar, The Messenger of Allah (pbuh) found 'Umar al-Khattab in a caravan while he was swearing by his father. So he said: Allah forbids you to swear by forefathers. If anyone swears, he must swear by Allah or keep silence.

**********

Same day wajen 9:45pm.......

Su Fadeela suna zaune a falo suna kallon 9 O clock news na NTA, shi ya zauna akan 3 seater ita kuma ta kwanta akan cinyarsa anayi ana hira.
Saiga wayarsa ya fara ruri alamun an kirashi, da sauri ya saka silent saboda ya gane wanda ya kirashi. Ita Fadeela bata ma lura da abinda yake ciki ba, duk hankalin ta yana wajen TV dake aikinsa.

Haka wayar ya cigaba da kara a karo na biyu shima ya kuma sakawa a silent, a hankali ya zame kan Fadeela dake jikinsa ya Mike tsaye.

“Baby bari inje bayi na dawo” Ya faɗa kana ya soma tafiya. Hanyan upstairs ya nufa zuciyarshi yana duka saboda bashida gaskiya.

“Ah ahn Other half baga bayi a kasa ba saika je wani upstairs” Ta mashi magana yayin dayake tafiya.

Cak ya tsaya tareda juyawa rai baiso ba, bakinsa yana rawa ya soma magana, “Kanin wanka fa zanyi”

“Ohhh kace babban Harka ne, gwara kaje chan kafin naji wari”

Murmushi yayi saiya juya ya tafi, yana tafe yana rarrabe ido alamun rashin gaskiya. Yana isa ɗaki saiga wayar Yasmeenah ya sake shigowa.

Da zumuɗi ya dauka tareda karawa a kunnen sa, “Hello!”

Ita kuma gyara kwanciya tayi saita makale murya chan kasa, “Hi Mine, ya kake?” shiru yayi dayaji tace mashi mine amma saiya basar ya cigaba da magana.

“Lafia lau, kefa?” “Ni gaskiya I’m not fine, Wai ace baka kira kaji yana kai gida ba koh? Bcs I’m not important to you”

“Ba haka bane, kinsan ina aiki da yawa but I’m sorry” sake mirginawa tayi daga kan gado sannan ta harde kafafu.

“Okay naji Mine, Kaci dinner kuwa? ko nazo na dauke ka mu fita mu ci?”

“Ai ni da wuri nake ci Wallahi”

“Ni gaskiya ban yarda ba, kawai rowa kayi min but It’s all good nima zan rama” ta faɗa muryanta à shagwaɓance.

Daga nan suka cigaba da hira kala kala har sunfi minti talatin suna zantawa. Ita kuma Fadeela tasan Other half ɗinta Baya daɗewa a bayi, saita bishi taji ko lafiya?

Yana kwance yana hira saiya ji zuwan Deela, da sauri ya tashi harda tuntuɓe zai shiga bayi, kafin ta buɗe kofan harya kunna famfo domin taji karar ruwa. Ajiyar zuciya ya rinka yi duk zufa yana keto masa.

Text yayi ma Yasmeenah akan he is busy zasuyi Waya gobe. Saiya dauraye fuskarshi da ruwa sannan ya fito.

Deela yagani zaune tana jiran shi, “Other half lafiya ka dad’e a bayi?”
Chapter 27 · 0% Book details