← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 48

Sashe 28

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Mts gaskiya kamar cikina ba lafiya ne” saiya zauna yana ajiyar zuciya.
Dukda yanda jikinta ke mata ciwo bai hanata sauka downstairs ba wajen First Aid box domin ta dauko masa Lemotin.

Tana taka matakalan karshe saida ta huta, a hankali ta karasa ɗakinsa domin ta bashi. Inda ta barshi anan ta iske shi, bare masa tayi kana taje bedside fridge ta dauko masa ruwa.

“Ungo karbi ko zaka ji dama dama”

Amsa yayi saiya yi kamar ya saka a baki amma ɓoyewa yayi a tsakiyar hannunsa, ruwan kawai yasha sai yayi wayo ya saka a aljihun wandon sa.

Ita kuma shafa masa kai take tayi tana masa sannu, ranar kwana tayi tana jinyarsa, ta kwantar dashi saita rufe shi da duvet. Saida ta tabbata yayi barci kana ta koma downstairs dukda tana ganin jiri Idan ta fiye bin wajen.

Kayan kallo ta kashe tareda kulle kofa da kyau, komawa tayi wajen Other half ɗinta duk tausayinshi ya mamaye ta. Ji takeyi kamar ta dauki ciwon ta daura ma kanta, fatan ta daya shine gobe kada ya farka dashi. Nima dai DIMPLΣS nace Amin ya rabb.

Washe gari misalin biyar da rabi na asuba suka tashi, sannu tayi mashi sannan ta koma dakinta. Shi kuma bayan ta tafi saiya dauki wayarsa wanda ke cikin bedside drawer.

Text msg ɗin Yasmeenah ya gani tayi mashi reply kamar haka, “Okay Mine, can’t wait to see you. Goodnight and chocolate dreams” Murmushi yayi wanda baisan yanayi ba.

Nan take yayi saving sunarta as ‘Aminu Office’ saboda kada Deela ta zarge shi dukda bawani abu yakeyi ba.
Ita kuma Deela tana idar da sallah ta wuce kitchen kasancewa yau talata kuma zata awo asibiti. Strawberry pancake tayi masa mai honey saita haɗa da sap ɗin Acha.

Yau da ciwon kai ta tashi saboda a daddafe take aiki ko ganin gabarta batayi, shiru tayi bata faɗa ma Naufal ba kasancewar shima yanaji da jikinsa.

Wajen karfe takwas ya ajiyeta a haraban asibitin Al madina saiya koma office idan ta gama saiya je ya dauketa.

Tana cikin asibiti tabi layin ganin Doctor, Dr Hadiza Pate tana ganin Deela saita mata murmushi.
“Bagashi Allah ya nufa fah” ta faɗa yayin da Deela take kokarin zama.

Daga nan aka duba yadda take tareda kwanakin cikin a jikinta. Anan ne aka gano satinshi goma sha daya.

Duk wani protocol daya kamata masu ciki subi duk tayi, ba ita ta gama ba sai wajen 11 ɗaya da wasu kananan mintuna.

Ta bala’in gajiya saita kira Naufal amma taji call waiting alamun Yana waya. Kashewa tayi tana jiran ya gama saiya kirata.

Shikuma daga ɗayan ɓangaren waya yakeyi da Yasmeenah sai Deela ta kira. Dayake ear piece yake amfani yana kallo yake ringing amma baiyi gigin dauka ba harya tsinke.

Shi yana so ya gama da Yasmeenah ne kafin ya kira Deela saboda yana kyautata zaton ta gama daga asibiti ne.

Ita kuma Yasmeenah sai zuba takeyi wai bata karya kumallo ba tana so ya raka ta. Yanata nokewa amma taki yarda wai saiya rakata koda baci zaiyi ba.

Suna cikin gardama saiga Aminu yazo da wani drawing yana so Naufal ya duba masa.
Da hannu yayi masa alama ya kashe wayar, sallama yake ma Yasmeenah saiya ajiye. Anan ya soma dubawa shaf ya mance zai kira Deela. Suna cikin haka 30 mins later sai Yasmeenah ta kira wai tana Larema tana jiran sa.

Nan take yayi ma Aminu sallama saiya tafi, Aminu shikuma ya ɗaga masa k’afa ne saboda yaji yace, “okay gani nan zuwa” duk zatonsa Deela ce ke ɗayan ɓangaren.

Sanye take da Swiss Lace mint green Wanda akayi mashi ɗinkin peplum. Ya ɗameta dakyar take numfashi balle tafiya.

Gwawaro style ta daura kawai amma bata saka mayafi ba kasancewa ita ba ma’abociyar sa bane. Chewing gum ta saka a bakinta tana tauna kas kas tareda wulla idanu.

Sannan gashi ta fashe kanta da turaren Unbreakable Bond. Tana cikin motarta kirar kia picanto tana jiran isowar Naufal. Tunanin irin salon da zatayi mashi ne yau saboda ta lura yanada zafin kai.

Shikuma yana isa Larema ya fito daga cikin motarsa, harya kulle saiya tunada Fadeela. Nan take yaji babu daɗi tareda haushin kansa.

Wayarsa ya dauko domin ya kirata, itakuma ta kulu tayi fam kamar ta fashe, a parking lot zaune take duk rana ita kaɗai kamar mayya. Taso tayi zuciya ta tafi amma kawai ta hakura kila yana wani abune, saisaita kanta tayi tana faɗin Allah yana tareda mai hakuri.

Sunansa tagani baro baro ‘other half’ murmushi tayi saita dauka, shikuma bugu ɗaya, biyu, na uku yaji ta dauka tareda faɗin, “ My Other half”
Bai kai ga amsa mata ba sai Yasmeenah tayi karab ta kwace wayan tareda kashewa.

Kallonta yayi a fusace ya rasa me zaice, “Meye haka? Bani wayana mana” Ya faɗa a sanyaye.

Murguɗa masa baki tayi cikin wasa tana jijiga jikinta komai nata yana rawa, “Bazan bada ba, lunch zamuci so no phones allowed” saita fara rausaya ta tafi ciki.

“idan kana so kazo ka karba” ta nuna masa wayan sannan ta zura cikin jakarta. Ranshi a bace ya bita ciki duk fargaban yanda Fadeela zatayi yake.

Ita kuma ta rinka Hello! Hello!! Amma taji Shiru. Sake kira tayi sai kawai taji an kashe, “kambu” ta ce saboda bata san sanda tayi ashar ba.

Da karfin tsiya ta fige jakarta, dama gidansu Anty Saudah zata saboda rana ya bigeta gashi jiri yana fizgarta.
Napep ta tare tayi gidanta tunda bata tambaye shiba, tana isa locacin azahar yayi. Bayi ta shiga ta watsa ma kanta ruwan zafi sai tayi alwala.
Sallolinta tayi tareda addu’a, bata bar kan sallaya ɗinba mirginawa kawai tayi ta soma barci. Gashi yunwa ya soma addabarta amma bazata iya tashiba saita huta.

Yasmeenah ta zauna wannan Karon a wajen VIP tana jiran Naufal, sannu a hankali ya taka wajen datake zaune. Murmushi ta sakar masa Shikuma fuskarshi babu yabo babu fallasa.

Duk ya kagu daya bar wajen saboda ya lura da abin iya shege ne. Kawai ordering jollof yayi baima ciba tsakura yayi.

Ita kuma Shawarma aka kawo mata da Non alcoholic wine.
Tana Ci tana mashi salon turanci kamar zata karya harshe, bai biye mata ba illa uhm da kuma uhm uhm dayake amsawa. Jira yakeyi su gama ci ya karɓi wayarsa domin ya kira Fadeela saboda yasan tana jiransa.

Bayan nan saita ce wai suje Vanilla joints shan Ice cream, wani mugun kallo ya watsa mata kana yace, “Halan bakisan inada aikin yi bane?”

“Oh na mance, muje na rakaka office I promise bazan dame kaba” saita ɗaga hannunta sama alamar rantsuwa.

Baiko kalleta ba ya buɗe motarsa.
“Maybe some other time” Yace sannan ya shiga ciki.

“Okay ba matsala” tace saita ɗaga masa hannu.

Yana tafe yana Zura gudu saboda yasan bai kyauta ma Fadeela ba, duk tausayinta ya kamashi kuma yayi mata alkawarin bazai sake ba.

Yana isa asibiti babu alamar Fadeela babu dalilinta, masu gadi ya tambaya sai suka ce masa ta kusa awa daya da tafiya. Dafa kansa yayi yana salati saboda yasan yanzu hankalinta ya tashi.

Wayanta ya kira amma bata ɗauka ba, dama yana kyautata zaton zatayi haka. Ita kuma wayar ta barshi cikin jakarta kuma yana downstairs saboda bazata iya jigilarsa ba.

Yasmeenah gidansu Laila ta wuce kai tsaye domin ta bata labarin abinda tayi kwana biyu. Anan ne Laila ke fada mata indai Architect Naufal ne to fah yanada mata, Amatullah kawar cousin dinta itace kanwarsa.

Cizon yatsa tayi tana jin haushin labarin, sai kuma kawai tayi fuska. Ita zata aureshi koda mata ɗari gareshi ballantana kwara ɗaya karamin alhaki.

Zata zama amarya sa uwar gida hauka tareda maida uwar gida ta zama bora. Koma waye matarsa kawai tayi hakuri ta bar mata Naufal salin alin kafin ta samata bakin ciki ya kasheta.

Kowa yasan Yasmeenah bata iya kishi ba, ba’a cin nasara akanta. Kawai a ganta a kyaleta!

Yana isa gida yaga jakar Deela a falo amma bata wajen, hankalin sa ya ɗan kwanta saboda ya buɗe yaga Wayanta ciki.

Dakinta ya nufa saiya ganta kwance a kasa, yayi nadaman abinda yayi mata ainun. A hankali yaje inda take saiya tallabota.

Mistike ido tayi sai tayi murmushi kamar babu abinda ya faru, dama ita bata iya mita ba. Shine domin borin kunya ya fara jero mata zance.

“Babyna kiyi hakuri, dazu da kika kirani muna conference call dasu Mr Sutter, muna gamawa shine na kiraki saiga wani ogan mu yazo yasa na kashe wayar”

“please I’m really sorry my love, in sha Allah bazan kara ba” kakalo murmushi tayi saita sumbace kumatunsa, “Babu komai, ya wuce saboda nasan baza kayi da gangan ba”

Daga nan ta tashi zata wuce kitchen, rakata yayi domin suyi tare Thou kawai mika mata abu yakeyi. Jollof din Cous Cous ne sukayi sai suka wuce dinning domin yunwa yana damun Deela, shi kuma karfin hali kawai yakeyi saboda ya riga yayi nat tareda Yasmeenah.

#NiDaDiyata

*All Rights Reserved*

💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 27 ✨✨✨

On the authority of Al-Numan bin Basheer, who said : I heared the messenger of Allah say : "That which is lawful is plain and that which is unlawful is plain and between the two of them are doubtful matters about which not many people know. Thus he who avoids doubtful matters clears himself in regard to his religion and his honor, but he who falls into doubtful matters falls into that which is unlawful, like the shepherd who pastures around a sanctuary, all but grazing therein. Truly every king has a sanctuary, and truly Allah's sanctuary is His prohibitions. Truly in the body there is a morsel of flesh which, if it be whole, all the body is whole and which, if it be diseased, all of it is diseased. Truly it is the heart." Narrated by Bukhari and Muslim.

*********

Yasmeenah Yusuf(YY) kokuma Meenah yanda friends ɗinta suke ce mata. Ita bafillatana ce yar asalin garin Shandam dake jihar Jos.
Chapter 28 · 0% Book details