Sashe 36
Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ga kuma peppersoup din kayan ciki a gefe yana jiranta, sai kuma kunun kanwa mai zafin gaske wanda yasha kayan kamshi. Kafewa tayi wai yayi mata yawa saboda idan taci zatayi katon ciki.
Mommy ta zare mata ido dolenta taci tana tura baki, shima Naufal yana daga wajen garden yan cin nashi abinci. Jefi jefi yake aikawa akai masa ɗiyar sa.
Son duniya ya daura mata da Mamanta. Shi ya tabbata yanzu Deela itace soulmate dinshi, burinsa bai wuce Deela ta yarda ta koma suyi rainon babyn tare cikin kwanciyar hankali babu mai takura masu.
Kuma gashi har yanzu baiyi mata magana ido da ido ba, Waya ne ya kira kuma batayi wani cooperating ba. Bayan ya tambaye ta karfin jikinta saita amsa bata sake ce abinda yafi ‘uhm ko uhm uhm ba’
Shi dai yaketa watsa mata kalamai yana faɗin irin kewarta dayake yi. Da taga zancen sa bashida niyyar karewa sai tace yan barka sunzo zatayi attending masu, daga nan saita kashe wayar.
Ita kuma Yasmeenah ya kirata ya gaya mata sau ɗaya zasu rinka waya kuma da daddare ne saboda yanzu his family needs him. Abin yayi mata ciwo sosai amma saita danne.
Congratulations tayi mashi tace ya tura mata pictures,ko sau ɗaya baiyi crossing ranta akan taje barka ba. Laila kawarta ta kitsa mata akan taje kafin Deela ta kullaceta.
Tunda bikinsu bai wuce saura sati biyu ba so itama family ce, ita Laila abinda yasa tace haka bai fi yanda take mutuwar san yara ba.
Yasmeenah taje stores ta ciko leda wajen uku da kaya na yara da niyyar kaiwa ranar suna.
********
Nurse Anisa takan zo duk safe kafin ta wuce aiki domin ta duba lafiyan Deela dana baby. Ko ranar daya kamata ayi ma jaririya allura ita tazo ta dauketa sukaje tareda Miemie suka dawo.
Matar mutunci kowa na yaba yadda takeda halin kwarai, yanzu kawance ya kullu sosai tsakaninta da Deela.
Wajen taran dare jajibarin suna, gida ya cika da yan suna daga Ko’ina duk anzo tayasu murna. Ga raguna manya manya wanda suka amsa sunarsu guda biyu sai kuka sukeyi.
Abinci kuwa, Mommy ta dauki nauyin girka komai daga catering company ɗinta. Shi tuntuni ya saka ma yarinya suna saboda masu printing su Memo da paper bags. Saidai bai faɗi ba.
Ita kuma Deela ta goge sosai tayi fresh kamar ta rinka haihuwa koda yaushe. Tana wanka da ruwan zafi sau biyu yadda ya dace kuma an fara koya mata yanda zata rinka ma kanta.
A nesa yake ganinta kuma yana kallon ta yana hadiye miyau, ya lura hankalinta kwance bata ko missn ɗinshi, ba kamar yadda yake kwad’ayi su zauna tare ba.
Gashi tana shan kunun kanwa sosai yasa kirjinta ya cika da dukiyar fulani. yarinyar ta bata rasa abinci, ci takeyi sosai saita ture. Itama tayi murmur tayi yar kiba, very chubby ga kuma fara’a. Sannan dimples dinta waje biyu sun lotsa sosai, gata kuma da gashi tunda ta biyo babanta.
Tana zaune a bakin gado tana shayar da yarinyar ta, yanda yarinyar keshan Mama yana karasa ma Deela taji sonta cikin ranta. Murmushi kawai take yi saboda soyayyarta ya mamaye mata rai.
Ita yanzu batada wani farin ciki daya wuce ɗiyarta, duk wani san duniya ta daura mata. Tana ganin tafi Maman sharukhan a Kabbi Khushi Kabbi Gham san yaro. Dukda ita wancan daga gate tana jin alamar shigowarsa.
Tana cikin haka sai ga Naufal ya shigo, sallama yayi tareda saukar mata murmushi. Fuskanta babu yabo babu fallasa ta amsa mashi.
Jawo kujerar mirror yayi saiya zauna dab da ita ya watsa mata ido kur. Sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da ɗiyarta.
“Baby Yanzu kin dena kallona” ya faɗa. Ita kuma bata amsa ba saboda bama tada niyyar magana.
Mika mata hannu alamar ta mik’a masa yarsa. Babu musu ta bashi, ita jaririyar harta soma barci dama abinda takeyi kenan all the time.
“Yarinya mai kamada the gorgeous Fadeela” ya faɗa yana kallon ta. Murmushi tayi kadan saita kauda fuskarta.shima murmushi yayi wanda ya bayyana kwarjininsa da kyau.
Riko hannun Deela yayi sai tayi kokarin kwacewa amma ta kasa, “Baby kiyi hakuri da abinda nayi maki, nasan ban kyauta ba amma inaso ki yafe min. Rabon kwado baya wuce cikin ruwa, Allah ya kaddara min auren nan tun kafin nazo duniya, please inaso mu runguma kaddara mu mance da differences dinmu”
Gyara zama yayi sosai saiya tallabo ma Deela gemu kana ya cigaba da magana. “Haba uwargidan Naufal, uwar gida zuciyar miji, uwar gida sarautar mata,uwar gida lantarkin gida, uwar gida babu kamar ki”
“I know you are a strong woman, Koda yaushe kina kokarin ki ɓoye damuwar ki koda yana cin maki rai. Kuma nasan cewa deep down you don’t hate me, kawai you miss me ne.”
“Nima wallahi i miss you, gashi yanzu babyn mu tazo. Ko ba zakiyi don ni ba Please kiyi saboda Pha’eexah”
Daga ido tayi tareda murmushi saboda yanzu taji sunar yarinyar, Daga mata gira yayi yana dariya. “Eh na saka mata Pha’eexah, please ki dawo mu raineta tare cikin gidan mu, Baby i love you so much”
Matse mata hannu yayi cikin kulawa yana mata wani irin kallo mai rikitarwa, gashi idanunsa sun canza kamanni, kana gani kasan yana cikin tashin hankali ne, “Baby Karki Bari kishi ya raba mu, kinsan cewa kece kika fara nuna min asalin soyayya, kece farkon matana a duniya kuma in sha Allah harda aljanna”
“Gashi kuma kin haifar min wannan Beautiful Angel mai kamada ke, please i need my family back. Baki lura you are my first everything bane, Komai dazai faru dani second ne saboda kin riga kinyi min komai and I will forever cherish you for that. Baby bakiga Allah ya riga ya karrama kiba tareda baki girma, girma fah baiwa ce! Please i will do anything Dan Allah ki yarda kawai ki dawo wajena”
“Banaso kuyi min nisa keda Pha’eexah, kinason na canza maki motane ko kayan daki? Just name it baby please”
Ita kuma a dikilce tace, “I like my furnitures and my car, thanks” saita juya fuskanta.
Dukawa kasa yayi saiya daura kanshi akan cinyarta, “Baby please ki dawo wajena, ina shan wahalar rashin ki, please gobe ko jibi sai ki dawo koh?” saiya duba yaga yanayinta.
“Okay zan yi tunani” ta faɗa
Da sauri ya dago tareda rungumota, ingijeshi tayi saita ce, “Sakeni Mallam, baka lura jego nakeyi ba halan”
Suna cikin haka sai ga Miemie tazo rike da pillow tana hamma daga alamu barci takeso tayi. Dama tun haihuwar Pha’eexah take kwana tareda su.
Patting bayan Deela yayi saiya sumbace yarsa a goshi kana ya tafi, yana tafe yana annashuwa bcs he is hopeful nanda Kwana biyu zata dawo.
Ita kuma Deela tana tunani gwara ta koma, ko babu komai yanzu akwai rabo tsakanin Su. Bazata yarda wata yar bariki ba ta rainan mata yarinya.
Kuma bazata bari azo a kwace Naufal haka kurum ba, ta gama taming dinshi, ta nuna mashi yadda ake Soyayya shine za’a rabata dashi.
Zata koma ɗakinta kuma zata zauna, zata nuna mashi ta fita daban cikin sauran mata.
#NiDaDiyata
*All Rights Reserved*
~Yarinya Mai Dimples~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 33 ✨✨✨
~LESSON~
Life comes with both happiness and sadness. Learn to be patient when sad and be grateful when happy. Allah will reward you and elevate your status.
It was narrated from Hafsah, the wife of the Prophet (pbuh) that The Prophet (pbuh) said: "Going to jumu'ah is obligatory for everyone who has reached the age of puberty.'" (Sahih)
**********
Ranar Suna...
Tun wajen karfe hudu na asuba as usual aka daura garwan ruwan wanka, wajen biyar da yankai ruwan yayi tausa uku aka sauke ma Deela.
Anty Saudah ta tada ta locacin data tashi sallar asuba, as usual Miemie ne mai rike Pha’eexah idan Deela ta shiga wanka har saita fito. Yau da kanta tayi wanka yasa saida ta dauki lokaci, abinda akeyi na minti talatin saida tayi wajen awa daya, tana fitowa little one tayi kuka ta gaji tanaso taci abinci.
Zama tayi gefen gado ta soma shayar da ita, tana tunanin sun kusa komawa inda ya dace watau asalin gidansu. Jawahir kawai take jira ta iso saita faɗa mata cewa gobe takeson komawa tunda Mommy bazata zo gidan suna ba irin yadda al’adan Mallam Bahaushe yake.
Shikuma yayi radin sunar Pha’eexah a masallaci tareda gayyata walima karfe biyun rana. Kowa yayi masa fatan alheri tareda addu’a, yaji daɗi sosai yanda aka nuna masa kulawa saboda limamin masjid ɗin yayi alkawarin zuwa.
Wasu tun daga nan suka soma kiransa da Abu_Pha’eexah kuma yaji daɗin abin sosai. Kiran Deela yayi after that ya faɗa mata, itama sanya alheri tayi kana suka cigaba da magana.
Yau tayi mashi magana daidai gwargwado, kuma shima abin ya burgeshi sosai domin har cemata yayi suyi breakfast tare.
Babu musu wajen 7am ta saka aka kai kayan abinci ɗakin Abba saita kirashi a waya yazo suci.
Kunun kanwa ta zuba masu da kosai, shi bawai yana san abin bane amma tunda Deela tanaci kuma bata mutu ba toh shima zai sha.
Bata wani sha sosai ba dama batasan cin abinci tun asalinta. Yayi mata magana saita ce masa ta koshi ne, wasa da hannun Pha’eexah takeyi while ita tana tsotso.
Wayar Anty Saudah suka gani akan ya saka Deela taci abinci kokuma Deelan ta fito haka an fasa breakfast ɗin tare. Mika ma Deela kokon yayi amma taki karba.
Asalima murguda masa baki tayi saita kawar da fuskanta gefe, rok’o yakeyi amma ta kafe akan bazata shaba. Haka ya hakura saiya sha harda nata kason saboda idan Anty ta riske abinci cikin kwano zata saɓa masu.
Shi bai damu idan anyi mashi faɗa ba, kawai ya daukin ma kansa alkawari ne akan Fadeela ta daina zubar da hawayen takaici saina farin ciki.
Yanaci yana zaro ido gashi ko rabi bai shanye ba, tun Deela tana matse dariya bata san sanda ta bushe tayi a bayyane ba. Kallon ta yakeyi yana jin dadin yadda take nishaɗi.
Mommy ta zare mata ido dolenta taci tana tura baki, shima Naufal yana daga wajen garden yan cin nashi abinci. Jefi jefi yake aikawa akai masa ɗiyar sa.
Son duniya ya daura mata da Mamanta. Shi ya tabbata yanzu Deela itace soulmate dinshi, burinsa bai wuce Deela ta yarda ta koma suyi rainon babyn tare cikin kwanciyar hankali babu mai takura masu.
Kuma gashi har yanzu baiyi mata magana ido da ido ba, Waya ne ya kira kuma batayi wani cooperating ba. Bayan ya tambaye ta karfin jikinta saita amsa bata sake ce abinda yafi ‘uhm ko uhm uhm ba’
Shi dai yaketa watsa mata kalamai yana faɗin irin kewarta dayake yi. Da taga zancen sa bashida niyyar karewa sai tace yan barka sunzo zatayi attending masu, daga nan saita kashe wayar.
Ita kuma Yasmeenah ya kirata ya gaya mata sau ɗaya zasu rinka waya kuma da daddare ne saboda yanzu his family needs him. Abin yayi mata ciwo sosai amma saita danne.
Congratulations tayi mashi tace ya tura mata pictures,ko sau ɗaya baiyi crossing ranta akan taje barka ba. Laila kawarta ta kitsa mata akan taje kafin Deela ta kullaceta.
Tunda bikinsu bai wuce saura sati biyu ba so itama family ce, ita Laila abinda yasa tace haka bai fi yanda take mutuwar san yara ba.
Yasmeenah taje stores ta ciko leda wajen uku da kaya na yara da niyyar kaiwa ranar suna.
********
Nurse Anisa takan zo duk safe kafin ta wuce aiki domin ta duba lafiyan Deela dana baby. Ko ranar daya kamata ayi ma jaririya allura ita tazo ta dauketa sukaje tareda Miemie suka dawo.
Matar mutunci kowa na yaba yadda takeda halin kwarai, yanzu kawance ya kullu sosai tsakaninta da Deela.
Wajen taran dare jajibarin suna, gida ya cika da yan suna daga Ko’ina duk anzo tayasu murna. Ga raguna manya manya wanda suka amsa sunarsu guda biyu sai kuka sukeyi.
Abinci kuwa, Mommy ta dauki nauyin girka komai daga catering company ɗinta. Shi tuntuni ya saka ma yarinya suna saboda masu printing su Memo da paper bags. Saidai bai faɗi ba.
Ita kuma Deela ta goge sosai tayi fresh kamar ta rinka haihuwa koda yaushe. Tana wanka da ruwan zafi sau biyu yadda ya dace kuma an fara koya mata yanda zata rinka ma kanta.
A nesa yake ganinta kuma yana kallon ta yana hadiye miyau, ya lura hankalinta kwance bata ko missn ɗinshi, ba kamar yadda yake kwad’ayi su zauna tare ba.
Gashi tana shan kunun kanwa sosai yasa kirjinta ya cika da dukiyar fulani. yarinyar ta bata rasa abinci, ci takeyi sosai saita ture. Itama tayi murmur tayi yar kiba, very chubby ga kuma fara’a. Sannan dimples dinta waje biyu sun lotsa sosai, gata kuma da gashi tunda ta biyo babanta.
Tana zaune a bakin gado tana shayar da yarinyar ta, yanda yarinyar keshan Mama yana karasa ma Deela taji sonta cikin ranta. Murmushi kawai take yi saboda soyayyarta ya mamaye mata rai.
Ita yanzu batada wani farin ciki daya wuce ɗiyarta, duk wani san duniya ta daura mata. Tana ganin tafi Maman sharukhan a Kabbi Khushi Kabbi Gham san yaro. Dukda ita wancan daga gate tana jin alamar shigowarsa.
Tana cikin haka sai ga Naufal ya shigo, sallama yayi tareda saukar mata murmushi. Fuskanta babu yabo babu fallasa ta amsa mashi.
Jawo kujerar mirror yayi saiya zauna dab da ita ya watsa mata ido kur. Sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da ɗiyarta.
“Baby Yanzu kin dena kallona” ya faɗa. Ita kuma bata amsa ba saboda bama tada niyyar magana.
Mika mata hannu alamar ta mik’a masa yarsa. Babu musu ta bashi, ita jaririyar harta soma barci dama abinda takeyi kenan all the time.
“Yarinya mai kamada the gorgeous Fadeela” ya faɗa yana kallon ta. Murmushi tayi kadan saita kauda fuskarta.shima murmushi yayi wanda ya bayyana kwarjininsa da kyau.
Riko hannun Deela yayi sai tayi kokarin kwacewa amma ta kasa, “Baby kiyi hakuri da abinda nayi maki, nasan ban kyauta ba amma inaso ki yafe min. Rabon kwado baya wuce cikin ruwa, Allah ya kaddara min auren nan tun kafin nazo duniya, please inaso mu runguma kaddara mu mance da differences dinmu”
Gyara zama yayi sosai saiya tallabo ma Deela gemu kana ya cigaba da magana. “Haba uwargidan Naufal, uwar gida zuciyar miji, uwar gida sarautar mata,uwar gida lantarkin gida, uwar gida babu kamar ki”
“I know you are a strong woman, Koda yaushe kina kokarin ki ɓoye damuwar ki koda yana cin maki rai. Kuma nasan cewa deep down you don’t hate me, kawai you miss me ne.”
“Nima wallahi i miss you, gashi yanzu babyn mu tazo. Ko ba zakiyi don ni ba Please kiyi saboda Pha’eexah”
Daga ido tayi tareda murmushi saboda yanzu taji sunar yarinyar, Daga mata gira yayi yana dariya. “Eh na saka mata Pha’eexah, please ki dawo mu raineta tare cikin gidan mu, Baby i love you so much”
Matse mata hannu yayi cikin kulawa yana mata wani irin kallo mai rikitarwa, gashi idanunsa sun canza kamanni, kana gani kasan yana cikin tashin hankali ne, “Baby Karki Bari kishi ya raba mu, kinsan cewa kece kika fara nuna min asalin soyayya, kece farkon matana a duniya kuma in sha Allah harda aljanna”
“Gashi kuma kin haifar min wannan Beautiful Angel mai kamada ke, please i need my family back. Baki lura you are my first everything bane, Komai dazai faru dani second ne saboda kin riga kinyi min komai and I will forever cherish you for that. Baby bakiga Allah ya riga ya karrama kiba tareda baki girma, girma fah baiwa ce! Please i will do anything Dan Allah ki yarda kawai ki dawo wajena”
“Banaso kuyi min nisa keda Pha’eexah, kinason na canza maki motane ko kayan daki? Just name it baby please”
Ita kuma a dikilce tace, “I like my furnitures and my car, thanks” saita juya fuskanta.
Dukawa kasa yayi saiya daura kanshi akan cinyarta, “Baby please ki dawo wajena, ina shan wahalar rashin ki, please gobe ko jibi sai ki dawo koh?” saiya duba yaga yanayinta.
“Okay zan yi tunani” ta faɗa
Da sauri ya dago tareda rungumota, ingijeshi tayi saita ce, “Sakeni Mallam, baka lura jego nakeyi ba halan”
Suna cikin haka sai ga Miemie tazo rike da pillow tana hamma daga alamu barci takeso tayi. Dama tun haihuwar Pha’eexah take kwana tareda su.
Patting bayan Deela yayi saiya sumbace yarsa a goshi kana ya tafi, yana tafe yana annashuwa bcs he is hopeful nanda Kwana biyu zata dawo.
Ita kuma Deela tana tunani gwara ta koma, ko babu komai yanzu akwai rabo tsakanin Su. Bazata yarda wata yar bariki ba ta rainan mata yarinya.
Kuma bazata bari azo a kwace Naufal haka kurum ba, ta gama taming dinshi, ta nuna mashi yadda ake Soyayya shine za’a rabata dashi.
Zata koma ɗakinta kuma zata zauna, zata nuna mashi ta fita daban cikin sauran mata.
#NiDaDiyata
*All Rights Reserved*
~Yarinya Mai Dimples~©Exquisite Online Writers
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
💦 Ni Da Diyata 💦
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples
💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦
✨✨✨Page 33 ✨✨✨
~LESSON~
Life comes with both happiness and sadness. Learn to be patient when sad and be grateful when happy. Allah will reward you and elevate your status.
It was narrated from Hafsah, the wife of the Prophet (pbuh) that The Prophet (pbuh) said: "Going to jumu'ah is obligatory for everyone who has reached the age of puberty.'" (Sahih)
**********
Ranar Suna...
Tun wajen karfe hudu na asuba as usual aka daura garwan ruwan wanka, wajen biyar da yankai ruwan yayi tausa uku aka sauke ma Deela.
Anty Saudah ta tada ta locacin data tashi sallar asuba, as usual Miemie ne mai rike Pha’eexah idan Deela ta shiga wanka har saita fito. Yau da kanta tayi wanka yasa saida ta dauki lokaci, abinda akeyi na minti talatin saida tayi wajen awa daya, tana fitowa little one tayi kuka ta gaji tanaso taci abinci.
Zama tayi gefen gado ta soma shayar da ita, tana tunanin sun kusa komawa inda ya dace watau asalin gidansu. Jawahir kawai take jira ta iso saita faɗa mata cewa gobe takeson komawa tunda Mommy bazata zo gidan suna ba irin yadda al’adan Mallam Bahaushe yake.
Shikuma yayi radin sunar Pha’eexah a masallaci tareda gayyata walima karfe biyun rana. Kowa yayi masa fatan alheri tareda addu’a, yaji daɗi sosai yanda aka nuna masa kulawa saboda limamin masjid ɗin yayi alkawarin zuwa.
Wasu tun daga nan suka soma kiransa da Abu_Pha’eexah kuma yaji daɗin abin sosai. Kiran Deela yayi after that ya faɗa mata, itama sanya alheri tayi kana suka cigaba da magana.
Yau tayi mashi magana daidai gwargwado, kuma shima abin ya burgeshi sosai domin har cemata yayi suyi breakfast tare.
Babu musu wajen 7am ta saka aka kai kayan abinci ɗakin Abba saita kirashi a waya yazo suci.
Kunun kanwa ta zuba masu da kosai, shi bawai yana san abin bane amma tunda Deela tanaci kuma bata mutu ba toh shima zai sha.
Bata wani sha sosai ba dama batasan cin abinci tun asalinta. Yayi mata magana saita ce masa ta koshi ne, wasa da hannun Pha’eexah takeyi while ita tana tsotso.
Wayar Anty Saudah suka gani akan ya saka Deela taci abinci kokuma Deelan ta fito haka an fasa breakfast ɗin tare. Mika ma Deela kokon yayi amma taki karba.
Asalima murguda masa baki tayi saita kawar da fuskanta gefe, rok’o yakeyi amma ta kafe akan bazata shaba. Haka ya hakura saiya sha harda nata kason saboda idan Anty ta riske abinci cikin kwano zata saɓa masu.
Shi bai damu idan anyi mashi faɗa ba, kawai ya daukin ma kansa alkawari ne akan Fadeela ta daina zubar da hawayen takaici saina farin ciki.
Yanaci yana zaro ido gashi ko rabi bai shanye ba, tun Deela tana matse dariya bata san sanda ta bushe tayi a bayyane ba. Kallon ta yakeyi yana jin dadin yadda take nishaɗi.