Sashe 34
Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
It was narrated that Wathilah bin Asqa' said "The Messenger of Allah (pbuh) offered the funeral prayer for a man among the Muslims and I heard him say: 'O Allah, so-and-so the son of so-and-so is in Your case and under Your protection. Protect him from the trial of the grave and the torment of the Fire, for You are the One Who keeps the promise and You are the Truth. Forgive him and have mercy on him, for You are the Oft-Forgiving, Most Merciful."
********
Bayan ya gama cin abinci saiya yi masu sallama kana ya tafi gidan Mama inda Abba yake. A varenda ya iske Abba yana sauraron BBC hausa.
Sallama yayi mashi sannan sukayi gaisuwan mutunci. Shima zama yayi gefe suka cigaba daji tare. Bayan minti akalla ashirin ya wuce basuce komai ba.
Naufal shi addu’a yakeyi saboda yanaso Abba ya amsa batunsa babu gargada. Gyara murya yayi sai yayi adjusting zamansa, idonsa na kallon k’asa ya soma magana cikin ɗa’a.
“Dama nazo muyi magana ne” Ya faɗa. Shikuma Abba rage karar radio sa yayi ya mayar da hankalinsa wajen Naufal, baiyi magana ba illa kallonsa yana jiransa.
“Dama batun Yasmeenah ne nakeso aje gidansu domin ayi magana”da kyar ya karasa maganar muryanshi sai rawa yakeyi saboda yanda Abba ke kallonsa kur.
“Bangane ba?”
“Ina Nufin maganar auren mu” ya amsa. Ashe Mama tana jinsu sai tayi karab ta chapke.
“Ban gane ba?Kamar ya kana so ka kara aure? Yaushe yaushe kayi aure ne? Ni duk daukana shiririta ne naku na yaran zamani ashe abin yakai haka. Ko mace ɗaya ka kasa rikewa balle biyu” ta faɗa, kara fitowa tayi varenda ta jingina da bango saita soma magana.
“tuntuni ake fama dakai akan kayi aure amma kakiyi shine kake so a cikin shekara biyu kayi mata biyu koh? Bazai yiwu ba asha fate ranar sallah” ta cigaba da sababi. Abba ne ya tsinke ta tareda faɗin, “Inbaa aure shine za’a aure ki?”
“Ai tunda shi yake son abinsa gwara a kyaleshi, tunda yanada halin da zai rike su. Kawai addu’a za’a bisu dashi Allah ya kauda tsautsayi da fitina”
“Amin summa Amin” Mama tace daganan sai tayi shiru. Naufal yaji daɗi sosai saboda zai shiga sahun manyan mutane watau masu mata biyu.
Abba ya umurce shi akan a gayama iyayen Yasmeenah gobe zasu kai gaisuwan iyaye kuma da sadaki duk za’a haɗa.
Godiya yayi saiya bar gidan ya tafi hanyar gidansu Meenah, murna sosai tayi harda rungumarsa. Daga nan ta soma zuba mashi sabon shagwaba. Bai bar kofar gidansu sai wajen sha daya saura kadan.
Washe gari anyi komai an bada sadakinta a dubu dari biyu, sai kudin gaisuwa dubu hamsin. An sanya biki da tarewa nanda sati shida watau ana kyautata zaton idan Deela ta haihu da sati biyu.
Da Anty Saudah taji maganar ta rasa ta inda zata fara gayama Deela, zaunar da ita tayi ta fara mata nasiha akan hakuri. Ita dai Deela batasan meke faruwa ba amma tasha jinin jikinta.
Da Anty Saudah ta gaya mata an saka auren Naufal ne, wani bakin ciki taji sosai wanda idan tana tsaye ne zata iya faduwa don takaici.
Saisaita kanta tayi saita sunkuyar da kanta kasa saboda hawaye sun fara mamalo mata, “Anty Allah ya sanya alheri” abinda ta iya furtawa kenan.
A hankali ta tashi da niyyar zuwa kitchen saboda danwake take so taci amma yanzu ya fita daga ranta, kawai su Anty zatayi mawa.
Tafe take tana tunanin rashin alkawari irin na ɗa namiji. Sai dai in zama da kishiya ne baya damunta saboda kowa halinsa zai kwaceshi.
Haka taje tayi abinci duk ranta a jagule, tana gamawa ta wuce daki tareda rufe kanta ta soma kuka. Lallai duniya budurwar wawa ne, idan ka saka shi a ranka zai kaika ya baro.
Duk jindadin da kake ciki within seconds idan Allah yaso saiya mayar maka da tashin hankali.
Ita dai tasan cewa kowa da nasa jarabawar kuma tana rok’on Allah ya bata Ikon cin nata. Fatan ta baifi Allah yasa ta sauka lafia ba babu wani complications.
Yasa duk wani abu da Dr tace ta kiyaye daidai gwargwado tanayi. Dadin ta ɗaya shine tayi scanning taga gender ɗin abinda zata haifa. Yadda take da san gayu haka take son ta haifi mace domin ta rinka mata.
Cikin ikon Allah abinda ke cikin cikinta kenan, yanzu duk siyayyar da zatayi ko Naufal ɗin kalar pink ake siyowa kokuma white.
Sun siya su cradle, drawer, kaya daban daban komai dai na tanajin haihuwa. Mama ta saka an sak’a mata showel masu kyan gaske da kuma rigar sanyi na yara.
Ita kuma Anty super ta dinka mata na fitar suna, su kuma su Bilqees, Abla da Amatullah da Miemie anko sukayi wani material purple mai ratsan lemon green.
Shikuma Naufal yayi ma Deela kala uku na fitar suna, sai kuma seti biyu na akwati da kit na faɗar kishiya. Sannan yayi ma kannasa kala ɗaya tareda iyayen sa duka.
Ita kuma Yasmeenah ce masa tayi ya bata kudi ta siya lefenta da kanta tunda ita zata saka abinta, dama zataje Dubai siyan ma kanta kayan dakine. Tana chan tana Siyayya saita rinka kiransa akan kuɗi ya kare ya gaggauta aiko mata.
Idan yayi mata korafi saita soma sababi tana cewa, ‘To keep a classy woman like her is not easy’ idan ta fada irin wannan abu yana mamakin ta sosai kamar ba ita ke rok’on sa ya aureta ba.
Kuma zancen classy da take magana, da zata ga matarshi da batace komai ba. Tun kafin aje Ko’ina har ya fara gajiya da yawan korafin ta.
Ita kuma murna fal ranta ta samu mai kuɗi gashi kyakyawa zata aura. Siyayya takeyi son ranta saboda tanaso bikinta ya jijiga Instagram.
Events kala shida zatayi, za’a buɗe da Fulani day, Korean Day saboda tana bala’in san film dinsu, sannan Kamu, Mother’s Day, Bridal shower da kuma Dinner.
Duk dinkinta a chan tayi, wedding gown dinta fari wanda zata saka ranar dinner Donatella Versace ta ɗinka mata.
Burinta ya cika saboda komai yana zuwa mata yadda take so. Yanzu matsalar ta ɗaya shine yadda zata fitar da matarshi daga cikin gidan.
Wani abin takaici shine ankai mata kaya jere cikin gida sai akace ɗakinta yana downstairs saboda duk na upstairs an cika shi. Abin yayi mata ciwo sosai amma ta kwantar da hankalinta saboda Hostile take over zatayi wa matarsa.
Dole ayi juyin mulki, duk wani abu datake controlling zata daina ne, Karyan iskanci takeyi!
Shikuma Mama ta gargade shi akan kada ya kuskura ya tada Deela daga cikin ɗakunan ta. Dama dakuna uku ke sama, kuma Deela na cikin 2 sai Naufal ɗaya.
A kasa kuma akwai ɗakuna biyu anan Yasmeenah zata zauna, kawai dai dakunan manya ne ba laifi kuma sunada bayinsu.
Batun kitchen kuwa lundary room aka kira carpenter yayi mata su shelves sannan aka kira plumber yayi sink da sauran su.
Dayake d’akin karami ne bazata ji dadin kitchen ɗinba, Komai a marmaste zatayi. Bazata wata ya kamar yadda Deela zata baza tabarma a kasa ba taji dadi.
Dama komai idan ba’a yi dakai ba bazaka ji daɗin abin ba. Dama shi Naufal ya tsara rayuwarsa da mace ɗaya ne yasa zuwan Meenah kamar takura masa ne.
Yasmeenah ta dawo daga Dubai shake da kaya zata kaima dangin mijinta, fitted gown material ta saka Ja da rastin silver wanda ya dame ta. sai tayi wrapping kanta da karamin gyale irin na Arabs.
Hannayenta kuwa wasu kwabɗa kwabɗan zabbai ne da warwazo.
Takalmin nan dai mai tsawo tareda igiyoyi ke kafarta zata gaida In-laws. Su sun saba a turai, soyayya kawai yaro yakeyi da yarinya zai kaita gidansu ta gaishe da iyayen shi amma sam Naufal yaki.
Ita kawai bataso tayi bakin jini wajen su yasa ta siyo masu turare zata kai masu. Bata sha wani wuya wajen gane gidan ba saboda kowa yasan architect.
Ta fara zuwa wajen Mama kafin taje taga Miemie saboda yadda yake maganar ta. Koda akayi mata iso wajen Mama akan tayi bakuwa, mamaki ya kamata da taga yarinya zaune tana jiran ta.
Gaisuwan yan bariki tayi ma Mama Irin,”Sannu Mama, ya kike?” mamaki ya bayyana a fuskar Mama karara wanda ya hanata amsawa.
“Yarinya daga ina?”
Murmushi Meenah tayi kana ta fara magana cikin salo, “Baki ganeni ba koh?”
“Ina zan ganeki baiwar Allah bayan ban sanki ba”
Sosa gemu tayi tana dariya harda makela kafada, ita kuma Mama haushi ya kamata saboda bata Santa ba gashi tazo falon ta tana mata salo.
“Mama nice fah Yasmeenah” ta faɗa tana dariya.
Kallon hadarin kaji Mama tayi mata sai tace, “lafiya kika zo min gida” jikin Meenah yayi sanyi amma ta dake ta soma magana, “Dama nace bari nazo na gaishe Kine, dama nayi tafiya ne shine nace bari na kawo maki wannan”
“toh fah!”Mama tace tana mata wani kallo, irin kallon you’re not welcome. Gyara zama tayi da kyau tana fuskantar saita soma magana idanunta babu wasa a cikin su.
“Mu fah a al’ada tun kaka da kakanni bamu saba budurwa taje gidan saurayi ba gaisuwa. Asali sai an kaita gidanta dangin miji zasu san fuskarta.”
Kara gyara zama tayi ta kalle Meenah da kyau kana ta cigaba da magana fuska a murtuke “koh matar Naufal watau Fadeela bamu sakata a ido ba, bata bi gida gida tana neman fada. Amma kince tsaraba kika kawo min koh? Toh ajiye kan table”
Daga nan sai Mama ta mayar da hankalinta kan SunnaTV dake aiki. Gwiwa babu kwari ta aikata abinda akace saita ce ma Mama “sai anjima”
“Yauwa mu jima da yawa” ta amsa ko kallon gefenta batayi ba. Tunda Yasmeenah take ba’a taba mata wani abu daya taɓa taba kamar yau. Ranta a jagule ta shiga motarta tayi hanyar gidansu kafin taje wajen Anty Saudah ayi mata wanda yafi wannan.
Ita kuma Mama ganin Ikon Allah ta tsaya yi wai budurwar da zai auro kenan, duk fake lashes da fake hair. Gashi sai yauki takeyi kamar danyen kuɓewa.
Naufal ta kira tayi mashi tas, shidai bata hakuri ya rinka yi kuma yayi mata alkawarin Yasmeenah zata canza yanayin shigar ta.
********
Bayan ya gama cin abinci saiya yi masu sallama kana ya tafi gidan Mama inda Abba yake. A varenda ya iske Abba yana sauraron BBC hausa.
Sallama yayi mashi sannan sukayi gaisuwan mutunci. Shima zama yayi gefe suka cigaba daji tare. Bayan minti akalla ashirin ya wuce basuce komai ba.
Naufal shi addu’a yakeyi saboda yanaso Abba ya amsa batunsa babu gargada. Gyara murya yayi sai yayi adjusting zamansa, idonsa na kallon k’asa ya soma magana cikin ɗa’a.
“Dama nazo muyi magana ne” Ya faɗa. Shikuma Abba rage karar radio sa yayi ya mayar da hankalinsa wajen Naufal, baiyi magana ba illa kallonsa yana jiransa.
“Dama batun Yasmeenah ne nakeso aje gidansu domin ayi magana”da kyar ya karasa maganar muryanshi sai rawa yakeyi saboda yanda Abba ke kallonsa kur.
“Bangane ba?”
“Ina Nufin maganar auren mu” ya amsa. Ashe Mama tana jinsu sai tayi karab ta chapke.
“Ban gane ba?Kamar ya kana so ka kara aure? Yaushe yaushe kayi aure ne? Ni duk daukana shiririta ne naku na yaran zamani ashe abin yakai haka. Ko mace ɗaya ka kasa rikewa balle biyu” ta faɗa, kara fitowa tayi varenda ta jingina da bango saita soma magana.
“tuntuni ake fama dakai akan kayi aure amma kakiyi shine kake so a cikin shekara biyu kayi mata biyu koh? Bazai yiwu ba asha fate ranar sallah” ta cigaba da sababi. Abba ne ya tsinke ta tareda faɗin, “Inbaa aure shine za’a aure ki?”
“Ai tunda shi yake son abinsa gwara a kyaleshi, tunda yanada halin da zai rike su. Kawai addu’a za’a bisu dashi Allah ya kauda tsautsayi da fitina”
“Amin summa Amin” Mama tace daganan sai tayi shiru. Naufal yaji daɗi sosai saboda zai shiga sahun manyan mutane watau masu mata biyu.
Abba ya umurce shi akan a gayama iyayen Yasmeenah gobe zasu kai gaisuwan iyaye kuma da sadaki duk za’a haɗa.
Godiya yayi saiya bar gidan ya tafi hanyar gidansu Meenah, murna sosai tayi harda rungumarsa. Daga nan ta soma zuba mashi sabon shagwaba. Bai bar kofar gidansu sai wajen sha daya saura kadan.
Washe gari anyi komai an bada sadakinta a dubu dari biyu, sai kudin gaisuwa dubu hamsin. An sanya biki da tarewa nanda sati shida watau ana kyautata zaton idan Deela ta haihu da sati biyu.
Da Anty Saudah taji maganar ta rasa ta inda zata fara gayama Deela, zaunar da ita tayi ta fara mata nasiha akan hakuri. Ita dai Deela batasan meke faruwa ba amma tasha jinin jikinta.
Da Anty Saudah ta gaya mata an saka auren Naufal ne, wani bakin ciki taji sosai wanda idan tana tsaye ne zata iya faduwa don takaici.
Saisaita kanta tayi saita sunkuyar da kanta kasa saboda hawaye sun fara mamalo mata, “Anty Allah ya sanya alheri” abinda ta iya furtawa kenan.
A hankali ta tashi da niyyar zuwa kitchen saboda danwake take so taci amma yanzu ya fita daga ranta, kawai su Anty zatayi mawa.
Tafe take tana tunanin rashin alkawari irin na ɗa namiji. Sai dai in zama da kishiya ne baya damunta saboda kowa halinsa zai kwaceshi.
Haka taje tayi abinci duk ranta a jagule, tana gamawa ta wuce daki tareda rufe kanta ta soma kuka. Lallai duniya budurwar wawa ne, idan ka saka shi a ranka zai kaika ya baro.
Duk jindadin da kake ciki within seconds idan Allah yaso saiya mayar maka da tashin hankali.
Ita dai tasan cewa kowa da nasa jarabawar kuma tana rok’on Allah ya bata Ikon cin nata. Fatan ta baifi Allah yasa ta sauka lafia ba babu wani complications.
Yasa duk wani abu da Dr tace ta kiyaye daidai gwargwado tanayi. Dadin ta ɗaya shine tayi scanning taga gender ɗin abinda zata haifa. Yadda take da san gayu haka take son ta haifi mace domin ta rinka mata.
Cikin ikon Allah abinda ke cikin cikinta kenan, yanzu duk siyayyar da zatayi ko Naufal ɗin kalar pink ake siyowa kokuma white.
Sun siya su cradle, drawer, kaya daban daban komai dai na tanajin haihuwa. Mama ta saka an sak’a mata showel masu kyan gaske da kuma rigar sanyi na yara.
Ita kuma Anty super ta dinka mata na fitar suna, su kuma su Bilqees, Abla da Amatullah da Miemie anko sukayi wani material purple mai ratsan lemon green.
Shikuma Naufal yayi ma Deela kala uku na fitar suna, sai kuma seti biyu na akwati da kit na faɗar kishiya. Sannan yayi ma kannasa kala ɗaya tareda iyayen sa duka.
Ita kuma Yasmeenah ce masa tayi ya bata kudi ta siya lefenta da kanta tunda ita zata saka abinta, dama zataje Dubai siyan ma kanta kayan dakine. Tana chan tana Siyayya saita rinka kiransa akan kuɗi ya kare ya gaggauta aiko mata.
Idan yayi mata korafi saita soma sababi tana cewa, ‘To keep a classy woman like her is not easy’ idan ta fada irin wannan abu yana mamakin ta sosai kamar ba ita ke rok’on sa ya aureta ba.
Kuma zancen classy da take magana, da zata ga matarshi da batace komai ba. Tun kafin aje Ko’ina har ya fara gajiya da yawan korafin ta.
Ita kuma murna fal ranta ta samu mai kuɗi gashi kyakyawa zata aura. Siyayya takeyi son ranta saboda tanaso bikinta ya jijiga Instagram.
Events kala shida zatayi, za’a buɗe da Fulani day, Korean Day saboda tana bala’in san film dinsu, sannan Kamu, Mother’s Day, Bridal shower da kuma Dinner.
Duk dinkinta a chan tayi, wedding gown dinta fari wanda zata saka ranar dinner Donatella Versace ta ɗinka mata.
Burinta ya cika saboda komai yana zuwa mata yadda take so. Yanzu matsalar ta ɗaya shine yadda zata fitar da matarshi daga cikin gidan.
Wani abin takaici shine ankai mata kaya jere cikin gida sai akace ɗakinta yana downstairs saboda duk na upstairs an cika shi. Abin yayi mata ciwo sosai amma ta kwantar da hankalinta saboda Hostile take over zatayi wa matarsa.
Dole ayi juyin mulki, duk wani abu datake controlling zata daina ne, Karyan iskanci takeyi!
Shikuma Mama ta gargade shi akan kada ya kuskura ya tada Deela daga cikin ɗakunan ta. Dama dakuna uku ke sama, kuma Deela na cikin 2 sai Naufal ɗaya.
A kasa kuma akwai ɗakuna biyu anan Yasmeenah zata zauna, kawai dai dakunan manya ne ba laifi kuma sunada bayinsu.
Batun kitchen kuwa lundary room aka kira carpenter yayi mata su shelves sannan aka kira plumber yayi sink da sauran su.
Dayake d’akin karami ne bazata ji dadin kitchen ɗinba, Komai a marmaste zatayi. Bazata wata ya kamar yadda Deela zata baza tabarma a kasa ba taji dadi.
Dama komai idan ba’a yi dakai ba bazaka ji daɗin abin ba. Dama shi Naufal ya tsara rayuwarsa da mace ɗaya ne yasa zuwan Meenah kamar takura masa ne.
Yasmeenah ta dawo daga Dubai shake da kaya zata kaima dangin mijinta, fitted gown material ta saka Ja da rastin silver wanda ya dame ta. sai tayi wrapping kanta da karamin gyale irin na Arabs.
Hannayenta kuwa wasu kwabɗa kwabɗan zabbai ne da warwazo.
Takalmin nan dai mai tsawo tareda igiyoyi ke kafarta zata gaida In-laws. Su sun saba a turai, soyayya kawai yaro yakeyi da yarinya zai kaita gidansu ta gaishe da iyayen shi amma sam Naufal yaki.
Ita kawai bataso tayi bakin jini wajen su yasa ta siyo masu turare zata kai masu. Bata sha wani wuya wajen gane gidan ba saboda kowa yasan architect.
Ta fara zuwa wajen Mama kafin taje taga Miemie saboda yadda yake maganar ta. Koda akayi mata iso wajen Mama akan tayi bakuwa, mamaki ya kamata da taga yarinya zaune tana jiran ta.
Gaisuwan yan bariki tayi ma Mama Irin,”Sannu Mama, ya kike?” mamaki ya bayyana a fuskar Mama karara wanda ya hanata amsawa.
“Yarinya daga ina?”
Murmushi Meenah tayi kana ta fara magana cikin salo, “Baki ganeni ba koh?”
“Ina zan ganeki baiwar Allah bayan ban sanki ba”
Sosa gemu tayi tana dariya harda makela kafada, ita kuma Mama haushi ya kamata saboda bata Santa ba gashi tazo falon ta tana mata salo.
“Mama nice fah Yasmeenah” ta faɗa tana dariya.
Kallon hadarin kaji Mama tayi mata sai tace, “lafiya kika zo min gida” jikin Meenah yayi sanyi amma ta dake ta soma magana, “Dama nace bari nazo na gaishe Kine, dama nayi tafiya ne shine nace bari na kawo maki wannan”
“toh fah!”Mama tace tana mata wani kallo, irin kallon you’re not welcome. Gyara zama tayi da kyau tana fuskantar saita soma magana idanunta babu wasa a cikin su.
“Mu fah a al’ada tun kaka da kakanni bamu saba budurwa taje gidan saurayi ba gaisuwa. Asali sai an kaita gidanta dangin miji zasu san fuskarta.”
Kara gyara zama tayi ta kalle Meenah da kyau kana ta cigaba da magana fuska a murtuke “koh matar Naufal watau Fadeela bamu sakata a ido ba, bata bi gida gida tana neman fada. Amma kince tsaraba kika kawo min koh? Toh ajiye kan table”
Daga nan sai Mama ta mayar da hankalinta kan SunnaTV dake aiki. Gwiwa babu kwari ta aikata abinda akace saita ce ma Mama “sai anjima”
“Yauwa mu jima da yawa” ta amsa ko kallon gefenta batayi ba. Tunda Yasmeenah take ba’a taba mata wani abu daya taɓa taba kamar yau. Ranta a jagule ta shiga motarta tayi hanyar gidansu kafin taje wajen Anty Saudah ayi mata wanda yafi wannan.
Ita kuma Mama ganin Ikon Allah ta tsaya yi wai budurwar da zai auro kenan, duk fake lashes da fake hair. Gashi sai yauki takeyi kamar danyen kuɓewa.
Naufal ta kira tayi mashi tas, shidai bata hakuri ya rinka yi kuma yayi mata alkawarin Yasmeenah zata canza yanayin shigar ta.