← Book details Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 48

Sashe 16

Nida Diyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kawai Miemie ta ankara da inda take saita soma sabon aiki. Daukar kwalba tayi a k’asa ta soma chachaka ma hannun ta, tana kaiwa wajen jijiyanta saita kwala ihu tareda sakin komai. Nan take ta fita hayacinta tareda sumewa.

Anty Saudah ta rusa ihu tareda rugawa wajen ta, Abla ma haka. Shi kuma Naufal mutuwar tsaye yayi saboda duk laifin shi ne.

Saida wasu seconds suka wuce kafin ya dawo hayacinsa, kukan zuci yake wanda yafi na baiyane ciwo.

Daukarta yayi kamar ‘yar tsana yayi waje cikin ruɗewa, ko mota bai shiga ba kawai ya nufa titi yana gudu da ita. Dadin abin Anty Saudah ta iya mota Saita tuka na Naufal ta riske shi a hanya.

“Saika shigo muje tunda ba’a kafa za’a ba” yaji kunya sosai daya lura da abinda yayi amma babu time for that.

Suna kaiwa Asibiti ER aka wuce da ita direct saboda tayi losing jini babu adadi. Kacha Kacha sukayi da jini kuma asibiti ɗin saida yasan da zuwansu.

Anje za’a kara mata jini amma babu match ɗinta saboda haka sai anje blood bank.

Dauke Doctor ɗin da mari Naufal yayi tareda cin kwallarsa, “Dan ubanka meyasa tuntuni baku nema ba dan sakarci sai yanzu?”

Sai kawai ya sake shi ya koma gefe yana kuka, ya tabbata idan suka rasa Miemie shiya kasheta.

Suna zaune aka kawo jinin, nan take aka soma yi mata aiki gadan gadan cikin awa biyu an gama komai.

10:45pm......

Fadeela tana zaune akan Couch tana jiran other half ɗinta babu shi babu dalilinsa kuma su Miemie basu kawo dinner ba, kawai komai yana mata wani iri amma bataso ta kawo mugun zato a ranta.

Har wajen 11:30 bai dawo ba, idanunta ya cika da hawaye tun tana matsewa har saida ta barke da kuka wiwi. Akan 3 seater ta kwanta tayi ma’ishi har barci ya dauketa.

Ita kuma Miemie tana buɗe ido a hankali ta soma magana. Kamar kowane mara Lafiya ruwa yake nema amma banda Miemie, “Khattab” ta furta tana hawaye. Naufal yaji sarai sai ya kyaleta, kwakwal warsa baya aiki abin duniya yayi mashi chunkoso.

Kana ganinta saita baka tausayi, ga jikinta duk bandage ko fuskarta an rufe wajen rabi dashi. Gashi kuma an saka mata oxygen ta hanci saboda numfashi.

Shi baisan yanda zai fara faɗa mata Khattab ya bar Nigeria ba, tunda ya rasa Miemie saiya gudu yabar gidansu, yanzu haka baada tabbacin ga inda yake.

Wasu Doctors su uku suka shigo tareda Nurse guda ɗaya.

“gaskiya zakuyi hakuri bcs alamarinta sai addu’a, yanzu kawai for safety shine za’a rinka k’ulleta saboda idan hannayenta is free saita rinka kokarin nakasa kanta.”

Sai suka fito da handcuff guda biyu, sun gark’e mata hannu ta kowane ɓangaren tareda gado. Itadai kallon kowa takeyi bata masan sunayi ba, “Yaya Khattab” tayita nanatawa.

“Wannan wani irin sone?” Naufal ya tambaya kansa.

#NiDaDiyata

*Fatan alkairi zuwa ga yan group din DIMPLΣS, Allah ya bar zumunci*

*All Rights Reserved*

💥∂ιмρℓεs💥
[8/2 13:23] 💕Ummieekhaleel 💕: ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

💦 Ni Da Diyata 💦

✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Written by DIMPLΣS
Wattpad @Aynarh_dimples

💦Dedicated to Xaynarb B Idreez 💦

✨✨✨Page 17 ✨✨✨

Jabir bin 'Abdullah, may Allah be pleased with them, narrated that Allah's Messenger said: "The key to Paradise is Salat, and the key to Salat is Wudu'." (Hasan)

It was narrated from Abu Hurairah that The Messenger of Allah said: "When it is very hot, then wait for it to cool down before you pray, for intense heat is from the flaring up of the Hell-fire." (Sahih)

**********

Six months later.....

Hakuri shine gishirin zaman duniya, kuma ainun Fadeela tayi exhibiting ɗin wannan abu. Babu abinda Naufal baiyi mata ba na cin zarafi kuma duk ta shanye.

Ko sau ɗaya bata taɓa tunanin zata faɗa ma Mommy ba ko Jawahir, ita kawai tasan nata jarabtan kenan. Sau biyu taje gidansu kuma shima sallah babba da karama ne.

Saidai kuma bai takura mata akan karatu, ya kyaleta ta cigaba amma koda wasa bai taɓa rage mata hanya ba. Idan kuma tanada 8am class toh tun wajen 4am take tashi tayi breakfast and lunch duk ta saka a cooler.

Azumi kuwa na Monday and Thursday baya wuceta Muddin tana cikin lafiya, ma’ana idan tana sallah.

Daga ɗayan ɓangaren ana nan ana fafutukan neman ma Miemie magani, Shidai Khattab har yanzu babu zancensa babu dalilin sa.

Sau da dama idan ciwon Miemie ya tashi Naufal ya rasa tudun dafawa sai kawai yaje gidansu Khattab ko office ɗin babansa ya zauna yayita rusa kuka.

The last time dayaje Sai Abban Khattab ya rantse mashi da girman Alkuran akan baisan inda yaronshi yake ba, shima rabon dasu haɗu tun text msg daya aika mashi akan ya tafi kuma daga nan yayi disconnecting layin, koda akayi tracing ɗakin Khattab ne last location.

Anan fa hankalin Naufal ya tashi sosai saboda ciwon Miemie sai gaba yakeyi. Akwai wani rana haka, Anty Saudah takaita bayan gida domin ta zaga, unfortunately ta cire mata hand cuff sai kawai Miemie ta naushe window da hannunta. Nan take jini ya soma gangaro wa kuma sai ta dauki broken glass tayi slitting wrist ɗinta.

Tashin hankali Anty Saudah ta gani mara misaltuwa saboda nan take Miemie ta sume, sau dama Miemie tayi abubuwa da zai janyo mata asarar ranta.

Akwai wani lokaci tafi One week bata kira sunar Khattab ba, kowa hamdala yakeyi ta fara samun sauki sai Naufal ya cire mata hand cuff ɗinta. Aiko basu suka ganta ba sai bayan kwana biyu.

Shima wajen data fara haduwada Khattab ne, ta zauna a gefen da ake gasa masara tanata rusa kuka, babu wanda yabi ta kanta saboda kana ganinta kasan babu hankali, gashi batada takalmi ga kai a tsefe yayi sama duk kacha kacha.

Tunda daga lokacin sukayi taka tsantsan da ita, yanzu dai basu saka mata Handcuffs akwai wani igiya haka mai yanayin beat. Shi ake saka mata kuma tana wani ɗaki ne wanda babu komai ciki sai carpet.

Wata rana tayita ihu tana buga kanta a kasa amma saboda laushin carpet bata jin ciwo. Wata rana kuma tayita kiran sunan shi a hankali tana hawaye, haka rayuwa ya kasance mata!

Duk Safe da yamma sai Naufal yaje ya dubata, da farko bata san ganinsa. Dayazo ta window inda ake lak’enta saita rinka ihu tana rufe idonta. Kullum kalmar “Ka cuce ni take furtawa”

Ba karamin tashin hankali ya shiga ba, ya kan rufe kanshi sau da dama a ɗaki yayita rusa kuka, tabbas yasan shine sila but yanzu da zai iya maida hannun agogo baya daya yi.

Amma yanzu ta rage mishi haka, tana zuwa har wajen window ta tsaya, Thou bata cewa komai but tana murmushi jefi jefi. Idan kuma time ɗin abinci da magani yayi yana shiga yayi feeding ɗinta.

Ita kuma Fadeela bata wuce One week bataje ta duba taba, abin yana burgeshi sosai amma baya nunawa, kuma ko sau ɗaya bai taɓa tunanin yabar ɗiban albarkan dayake mata ba.

Shi dama yace aurenshi zai zame mata ɓakin canji a rayuwarta, kuma daidai gwargwado yana kokarin ya nuna haka. Dukta susuce tayi fari kamar fatalwa, yasa bataso taje gidansu kafin hankalin Mommy ya tashi.

Ko Jawahir baifi sau biyar taje nata gidan ba kuma shima a gurguje ne. Kullum tana cikin waya da Mommy, “babu abinda kike nema? Lafiyan ki kalau? Me za’a yi maki?” shine tambayar datake mata kuma ko sau ɗaya bata taɓa furta abinda zai jawo ma mijinta kaskanci ba ko bakin jini.

Idan ta gama aikace aikace ɗinta saita je wani empty room haka wanda kayan art work ɗinta suke tayita painting hankali kwance. Shi kaɗai ne abinda takeyi mai kawo mata solace, idan tana yi saita mance da bakin cikin gidan aure.

******

Yau Juma’a kuma kamar kowane sati inada 8am class. Tun wajen 4am alarm ɗina ya tashe ni but ban samu daman saukowa daga kan gado ba sai wajen 4:30am.

A daddafe na sauko inayi ina murje ido bcs barci bai isheni ba. Wajen karfe sha biyu da rabi na kwanta sanadiyar projet dana farayi kasancewar mune final year student.

Kitchen naje na fara kama aiki watau breakfast kuma shima Soyayyar dankali ne wanda tun jiya da daddare na fere na ajiye abina a fridge domin na samu sauki yau.

Daga nan sai nayi jollof Rice na saka ma Naufal abinsa na rana a cooler saboda bazan samu daman dawowa da wuri ba bcs ina Missing Miemie.

Kafin na gama aiki Asbah ta danno kai gadan gadan tunda sai karfe shida akeyi. Pausing girkin nayi na mayar da komai on low heat saina wuce ɗaki.

Alwala na dauro tareda nafilar raka’atanil fijr, ina cikin azkar sai aka kira sallar karshe which nima na tashi nayi. Adduar safe nayi wanda kowane ɗan Adam ya kamata yayi sai kuma na haɗa da neman ma kaina, mijina,iyayena da al’umma baki daya tsari daga sharrin masharranta watau mutum ko aljani.

Kai tsaye kitchen na koma na cigaba daga inda na tsaya, ina ciki naji Ya Naufal ya dawo daga masallaci, murmushi nayi k’arara saboda My other half yasan darajan sallah, at all Baya wasa dashi. Saboda haka ni bana cire ran wata rana zai soni.

Nasan cewa wata rana zai gane nice other half ɗinsa Kuma nasan zaiyi alfahari dani kamar yadda nakeyi dashi. Kwata kwata yanzu bana jin haushin cin kashin dayake mun, I’m not making excuses for his actions but nasan cewa yana cikin damuwa akan ciwon Miemie, fatana kullum Allah ya bata lafiya kila nima na samu lambar zuciyar sa.

12 pm.....

Locacin ne na gama lectures ɗina, kasancewar yau Friday kuma short working day so banyi tunanin zuwa wajen project supervisor ɗina ba.

Tafe nake da Samɗa,Jumaimah da kuma Mansura k’awayena. Muna tafe muna hira hankali kwance. Samɗa ce tayi hanyar parking lot inda motarta yake.

Ihsan Baby ɗin Samɗa na dauka wanda ke tareda mai aikin ta, wasa nakeyi sosai tunda ina san yara, kallona samɗa tayi cikin tuhuma kuma kana ganinta kasan da magana a bakin ta.

“Faɗa karya kasheki” nace ita kuma dariya tayi kafin tace, “Kinsan cewa ke zaki rinka nuna masa salo da zai janyo maki hankalin shi? ”

“Wallahi kin bani dariya, meye banyi ma bawan Allah ɗinnan ba amma banza yake dauka na. Ke ni na gaji wlh”
Chapter 16 · 0% Book details