Sashe 27
Ni Da Gidana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dai dai k'arfe uku na dare, Khalifa ya sad'ad'o ya shigo min d'aki, bisa ga tsautsayi na sabon da nayi na rashin rufe k'ofata da mukulli daga ciki, Sai dai na tura ta Kawai, ga kuma fahimtar da Khalifa yayi, Ancle Fa'iz baya kwana a wurina. Wannan shi yasa ya samu nasarar yin a binda ya k'udurta a sauk'ak'e. Fitila ya fara kunnawa da ya shigo, haske ya gauraye d'akin Sannan ya ta sheni, ta hankar bubbuga filon da na d'ora kaina a kai. A tsorace na tashi. Na sake tsorata sosai da ganin Khalifa a kaina ya zubomin idanu. Na bazama na jawo softcotton blanket da na a jiye gefena, saboda irin Kayan baccin dake jikina na shan iska ne, saboda zafin da ake yi, a tsukun.
"Lafiya? Khalifa me ya kawoka d'akina cikin dare? Cikin hankalinka kuwa kake?
Ya zaro min idanu, irin na tsoratarwa.
"Na fikima wadatar hankali Sumayya. Ramuwa ce Kawai ta kawoni d'akin nan, saboda wai saboda ke Yaya Fa'iz ya cimin mutunci, cin mutuncin da ba'bu mahaluk'in da yayi min irin'sa. Nasan kuma ke kika zugoshi, to Wallahi kinyi kuskure babba,domin ni ba a takani a Sha!."
Wani irin tsoro ya kamani sosai, domin zatona Wata illar zai min, ko ya hallakani. Muryata na rawa nace.
"Khalifa, amma Sai cikin dare za'ka yi ramuwar? idan gari ya waye Kayi min komenene, amma don Allah banda yanzu."
Yace "Ina! ai Wallahi baki isa ba, yanzu zan rama. Ramuwar gayya tafi ta gayya ciwo. Ciwon da naji a zuciyata Sai na ninninka miki irin'sa. Ki bani had'in kai, na 'yan mintina ne zan idar da nufina na tafi, idan kuma ba haka ba, zan k'ulla miki sharrin da babu mahaluk'in da zai iya wankeki a duniya? sai kowa ya tsaneki, ni da yaya Fa'iz Kawai kika had'ani, ni kuma Sai na had'aki da kowa kin zama a bar k'ya mata."
Tuni na d'au hasken me Khalifa yake nufi,na kuma girgiza da mummunar manufar'sa, da ya rik'a a matsayin ramuwa. Nace
"Wallahi Khalifa bazan aikata aikin ashsha ba, ban aikata ma a baya ba, Sai yanzu da nake da nauyin hak'k'in aure a wuyana? ni ba halina bane. Na yarda Kayi min kowani hukunci idan kalmar hak'uri bazata ceceni ba, amma banda wannan manufar taka"
Yace "Ai ban baki zab'i ba. Kuma ramuwa fa nace zanyi, kuma ramuwar mugunta ai a binda Mutum kasan yafi k'i shi za'ka yi masa ka huce. Kuma nasan mijinki ma, duk da baya sonki, zai tsaneki ya sakeki take, idan ya sa ni." Yana fad'in haka naga ya nufoni.
Nayi zallo gefe a zabure.
"Wallahi zan fasa K'ara na tara Maka jama'a".
Yace
"Haka na fiso ai ki tara Mana ma mutane." Ya nufoni gadan gadan.
Na kuwa daddage na fasa Wata irin k'ara cikin kad'aitaccen daren. Na kuma fasa ta biyu da tafi ta farko sauti. Sai naga Khalifa ya tsaya cak.!
Ancle Fa'iz ne kuwa farkon shigowa, saboda d'akin'sa yana dab da nawa, dole yafi kowa ji. Da Khalifa bakin k'ofa yaje ya tare, domin kar na fita, Amma ganin shigowar Ancle, Sai yaja gefe guda, ni kuma jin Ancle ya kira Sunana yana shigowa falon da sauri, na antayo daga d'aki, bayan naja wani mayafina dake jikin hunger na lullub'e k'irjina. Yarda na taho karta na nufo Ancle Fa'iz Sai a zaci jikin'sa zan fad'a, Amma Ina zuwa Sai na tsugune k'as a gaban'sa Ina kuka. Ancle naga ya Shiga wani irin rud'u da yaga Khalifa, ya juyo da kan'sa ya dubeni. Ya zuba Mana idanu Kawai, ya dubeni, Sai ya dubi Khalifa kuma. Can yasa hannu ya d'agoni daga durk'uson.
"Ihun me kike yi? Me ya faru? Me yasa naga Khalifa a d'akin'ki?
Kafin na iya amsawa Sai ga Muhibbat,da khairat sun shigo, ai Sai na sake Shiga d'imuwar rasa ta Ina zan fara, saboda kunyar Jama'ar da suka soma taruwa, kuma duk Jinin Khalifa.lokaci guda naga idanun Ancle sun sauya kala, sun yi jawur, Sai a zaci ba'ainihin kalar su fari fat bane, masu bada launin shud'i shud'i.Khalifa kuma Kawai yake kallo cikin sauyayyen Jan idanun.
Cikin tsawa yace masa.
"Me ya kawoka d'akin Sumayya? giya kasha, ko wiwi, ko kuma hodar iblis, fad'amin."
A dake ya amsa."Sumul nake. Kuma idan Ina shan d'ayan su, ai kaine shaidar farko, Yaya Fa'iz."
"Karka fad'amin Maganar banza, idan ka tashi shan, Sani zanyi? Fad'amin a binda ya kawo ka d'akinta, ko nayi Maka illar da bazaka moruba Wallahi."
Bud'ar bakin Khalifa.
"Gayyatoni tayi da kanta. Kuma batun yau ta soma gayyatata ta ba, saboda tace wai baka sauraronta, baka bata lokacinta, irin na mace da Miji yau ma bore nayi mata, nace zan fallasa komai, shine tayi ihu, domin reshe ya juye da mujiya."
Muhibbat ta d'au salati, amma wani sakaran kallo da Ancle ya jefa mata, Sai ta d'inke bakin. Khairat dai bata ce komai ba, illa tagumi na tsantsar damuwa. Da k'yar na samu wani k'ololon a bu ya fad'amin da ya tsayamin a k'ahon zuci, saboda Shiga firgicin jin sharrin da Khalifa ya kallafamin.
"Wallahi Ancle K'arya yakemin. Ina kwance na ganshi a tsaye a kaina....
Khalifa ya katse da sauri.
"Ta d'an a dam za'kiyi min? Saboda kina tsoron hukuncin da zaki fuskanta?
Na sake fashewa da kuka. "Kaji tsoron Allah Khalifa...."
Ya sake katseni."To, tsoronki zanji idan banji tsoron Allah ba? ai tsoron Allan yasa na zab'I na Toni a Siri komai yazo k'arshe."
Shigowar Momi dai dai nan yasa na sake firgicewa, domin nasan al'amari ma ya gama lalacewa. Ga Khalifa ya hanani nayi bayani sosai har Momi ta shigo.K'arin d'imaucewar tawa ma, da na kasa gane gaskiyar sirrin zuciyar Ancle Fa'iz na yarda ko rashin yarda, game da mummunan sharrin da Khalifa ya k'ullamin, domin har Momi ta shigo ta soma magana baice komai ba. Da alamu bayan rud'ani, kansa ya d'auki zafi, b'ararraka caji Kawai yake tayi. Momi ta dubemu Mu duka tace
"Wai me yake faruwa a nan.? Ihu da surutai sun tsoratani da k'yar na iya fitowa, zatona ko b'arayi suka shigo ma, Sai da na tabbatar da muryoyi."
Kafin ma ta rufe baki Muhibbat ta zayyano, Khalifa ya karb'a ya k'arashe har da k'ari. Mugun
Kallon da Momi tayi min banyi zaton zan tsira daga shan maruka ba, hagu da dama, ko kuma saukar mahaukacin duka, irin na kawo wuk'a.
"Biri yayi kama da Mutum, kuma alamu a lamun somin hauka zub da miyau.Tuni na tsinke da al'amarinki dama Sumayya, zaki iya fiye da haka. Wato bayan kin tarwatsamin Zaman lafiyar yara, yanzu kuma kinzo kin gurb'atamin tarbiyyar yarona da na d'ebi shekaru Ina tarbiyya. To Wallahi hukuncin da zan d'auka a kan'ki ba iya ke kad'ai zai tsaya ba, har iyayenki, ko da yake baki ma dasu Sai kakanni, to har tsufansu bazan tausaya ba."
Cikin Kukan da da k'Yar yake fita saboda tashin hankali nace "Momi, Wallahi sharrin Khalifa ne, shine......"
Ta dakamin tsawa."Rufemin baki Munafukar banza,mai bak'ar a niya, da mugun hali, da mugun usuli."
Nan naga Ancle Fa'iz ya dubi Momi a hargitse, da alamun Furucinta ya Sosa masa rai sosai, Kawai ta tsira ne, saboda itan mahaifiyar sace.
Kuka na ya k'ara d'agawa, jin dad'in komai ya tafi yarda Khalifa keso, Shima ya dakamin tsawa.
"Rufemana baki, shaid'aniyar Kawai, haka kurum kin jefani halin halaka."
Ai kafin ya rufe baki, Ancle ya kwasheshi da wani irin wawan mari.Ai bansan Sanda na tsaida kuka na ba. Momi ma baki bud'e tayi tana kallon Fa'iz, haka ma Muhibbat ta wani zaro ido na Mamaki, haka Khairat. Shi kuwa Wanda aka Mara d'in dafe kunci yayi Yana kallon Yayan sa ido yayi tulu tulu, kamar zai rama, saboda k'uncin zuci
A zafafe Ancle yace "Matar tawa kake zagi kana dakawa tsawa? a gabana kuma? Lallai ka Isa tabbataccen Mara kunya, kuma Wallahi Sai na koya Maka hankali"
Nan Momi ta karb'a a fusace "Fa'iz, d'an uwanka Kaci zarafi ka tozarta a kan wannan 'yar iskar matar taka? to me yayi mata ma?ai kome yayi mata bai biyani ba. Wato Sam baka duba ma ga ta'asar da tayi, kai ta anzageta shine damuwarka ko?
Ya aro nutsuwa, da tausar zuciyarsa Sannan ya soma magana.
"Momi idan sumayya shaid'ani yace Khalifa ma shine, domin kuwa k'arfe d'aya baya amo, Sai da a bokin yin sa. Kuma in dai hukunci na gaskiya za'ayi to su duka za'a tuhuma, kuma a hukunta. Kuma in dai har an yarda Sumayya ita ta fara neman Khalifa, to kuma laifin'sa yafi girma, kuma yafi fitowa fili, domin kuwa d'akin Sumayya aka ganshi, ba ita aka gani a d'akin sa ba."
*🏤 NI DA GIDANA 🏤*
*_Littafi na daya_*
*NA*
*ZAINAB ILYAS MAZAWAJE*
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
📱22
________ Ga Wanda duk ya dubi Momi, zai ga alamun maganganun Ancle Fa'iz sun Shiga sun zauna Zuciyarta, amma saboda zafina da take ji, da tsana Sai ta sake tasowa Ancle Fa'iz da fad'a da bantab'a ganin shi tana yi masa ba cikin 'ya'yan'ta. Ina ganin kuma Muhibbat tana yiwa Momin rad'a a kunne da Ancle Fa'iz ya kau da kai. Tace a zuciye.
"Kar na sake jin ka dangantawa d'ana laifi irin na wannan banzar matar taka, rore roren tsiya. Yaro na Khalifa kin tsatstsene ita ta yaudareshi, idan ba haka ba me yasa da bai yi ba.? gaba d'aya ma Fa'iz ka fa canza daga d'an da na Sani, mai kishin 'yan uwan'sa da son su da tsananin son Momin'sa."
Ya dubi momin, cikin sanyaya murya.
"Ina nan Momi a sanin da kika yi min, fahimtata dai kika kasa yi." Ta girgiza kai.
"Lafiya? Khalifa me ya kawoka d'akina cikin dare? Cikin hankalinka kuwa kake?
Ya zaro min idanu, irin na tsoratarwa.
"Na fikima wadatar hankali Sumayya. Ramuwa ce Kawai ta kawoni d'akin nan, saboda wai saboda ke Yaya Fa'iz ya cimin mutunci, cin mutuncin da ba'bu mahaluk'in da yayi min irin'sa. Nasan kuma ke kika zugoshi, to Wallahi kinyi kuskure babba,domin ni ba a takani a Sha!."
Wani irin tsoro ya kamani sosai, domin zatona Wata illar zai min, ko ya hallakani. Muryata na rawa nace.
"Khalifa, amma Sai cikin dare za'ka yi ramuwar? idan gari ya waye Kayi min komenene, amma don Allah banda yanzu."
Yace "Ina! ai Wallahi baki isa ba, yanzu zan rama. Ramuwar gayya tafi ta gayya ciwo. Ciwon da naji a zuciyata Sai na ninninka miki irin'sa. Ki bani had'in kai, na 'yan mintina ne zan idar da nufina na tafi, idan kuma ba haka ba, zan k'ulla miki sharrin da babu mahaluk'in da zai iya wankeki a duniya? sai kowa ya tsaneki, ni da yaya Fa'iz Kawai kika had'ani, ni kuma Sai na had'aki da kowa kin zama a bar k'ya mata."
Tuni na d'au hasken me Khalifa yake nufi,na kuma girgiza da mummunar manufar'sa, da ya rik'a a matsayin ramuwa. Nace
"Wallahi Khalifa bazan aikata aikin ashsha ba, ban aikata ma a baya ba, Sai yanzu da nake da nauyin hak'k'in aure a wuyana? ni ba halina bane. Na yarda Kayi min kowani hukunci idan kalmar hak'uri bazata ceceni ba, amma banda wannan manufar taka"
Yace "Ai ban baki zab'i ba. Kuma ramuwa fa nace zanyi, kuma ramuwar mugunta ai a binda Mutum kasan yafi k'i shi za'ka yi masa ka huce. Kuma nasan mijinki ma, duk da baya sonki, zai tsaneki ya sakeki take, idan ya sa ni." Yana fad'in haka naga ya nufoni.
Nayi zallo gefe a zabure.
"Wallahi zan fasa K'ara na tara Maka jama'a".
Yace
"Haka na fiso ai ki tara Mana ma mutane." Ya nufoni gadan gadan.
Na kuwa daddage na fasa Wata irin k'ara cikin kad'aitaccen daren. Na kuma fasa ta biyu da tafi ta farko sauti. Sai naga Khalifa ya tsaya cak.!
Ancle Fa'iz ne kuwa farkon shigowa, saboda d'akin'sa yana dab da nawa, dole yafi kowa ji. Da Khalifa bakin k'ofa yaje ya tare, domin kar na fita, Amma ganin shigowar Ancle, Sai yaja gefe guda, ni kuma jin Ancle ya kira Sunana yana shigowa falon da sauri, na antayo daga d'aki, bayan naja wani mayafina dake jikin hunger na lullub'e k'irjina. Yarda na taho karta na nufo Ancle Fa'iz Sai a zaci jikin'sa zan fad'a, Amma Ina zuwa Sai na tsugune k'as a gaban'sa Ina kuka. Ancle naga ya Shiga wani irin rud'u da yaga Khalifa, ya juyo da kan'sa ya dubeni. Ya zuba Mana idanu Kawai, ya dubeni, Sai ya dubi Khalifa kuma. Can yasa hannu ya d'agoni daga durk'uson.
"Ihun me kike yi? Me ya faru? Me yasa naga Khalifa a d'akin'ki?
Kafin na iya amsawa Sai ga Muhibbat,da khairat sun shigo, ai Sai na sake Shiga d'imuwar rasa ta Ina zan fara, saboda kunyar Jama'ar da suka soma taruwa, kuma duk Jinin Khalifa.lokaci guda naga idanun Ancle sun sauya kala, sun yi jawur, Sai a zaci ba'ainihin kalar su fari fat bane, masu bada launin shud'i shud'i.Khalifa kuma Kawai yake kallo cikin sauyayyen Jan idanun.
Cikin tsawa yace masa.
"Me ya kawoka d'akin Sumayya? giya kasha, ko wiwi, ko kuma hodar iblis, fad'amin."
A dake ya amsa."Sumul nake. Kuma idan Ina shan d'ayan su, ai kaine shaidar farko, Yaya Fa'iz."
"Karka fad'amin Maganar banza, idan ka tashi shan, Sani zanyi? Fad'amin a binda ya kawo ka d'akinta, ko nayi Maka illar da bazaka moruba Wallahi."
Bud'ar bakin Khalifa.
"Gayyatoni tayi da kanta. Kuma batun yau ta soma gayyatata ta ba, saboda tace wai baka sauraronta, baka bata lokacinta, irin na mace da Miji yau ma bore nayi mata, nace zan fallasa komai, shine tayi ihu, domin reshe ya juye da mujiya."
Muhibbat ta d'au salati, amma wani sakaran kallo da Ancle ya jefa mata, Sai ta d'inke bakin. Khairat dai bata ce komai ba, illa tagumi na tsantsar damuwa. Da k'yar na samu wani k'ololon a bu ya fad'amin da ya tsayamin a k'ahon zuci, saboda Shiga firgicin jin sharrin da Khalifa ya kallafamin.
"Wallahi Ancle K'arya yakemin. Ina kwance na ganshi a tsaye a kaina....
Khalifa ya katse da sauri.
"Ta d'an a dam za'kiyi min? Saboda kina tsoron hukuncin da zaki fuskanta?
Na sake fashewa da kuka. "Kaji tsoron Allah Khalifa...."
Ya sake katseni."To, tsoronki zanji idan banji tsoron Allah ba? ai tsoron Allan yasa na zab'I na Toni a Siri komai yazo k'arshe."
Shigowar Momi dai dai nan yasa na sake firgicewa, domin nasan al'amari ma ya gama lalacewa. Ga Khalifa ya hanani nayi bayani sosai har Momi ta shigo.K'arin d'imaucewar tawa ma, da na kasa gane gaskiyar sirrin zuciyar Ancle Fa'iz na yarda ko rashin yarda, game da mummunan sharrin da Khalifa ya k'ullamin, domin har Momi ta shigo ta soma magana baice komai ba. Da alamu bayan rud'ani, kansa ya d'auki zafi, b'ararraka caji Kawai yake tayi. Momi ta dubemu Mu duka tace
"Wai me yake faruwa a nan.? Ihu da surutai sun tsoratani da k'yar na iya fitowa, zatona ko b'arayi suka shigo ma, Sai da na tabbatar da muryoyi."
Kafin ma ta rufe baki Muhibbat ta zayyano, Khalifa ya karb'a ya k'arashe har da k'ari. Mugun
Kallon da Momi tayi min banyi zaton zan tsira daga shan maruka ba, hagu da dama, ko kuma saukar mahaukacin duka, irin na kawo wuk'a.
"Biri yayi kama da Mutum, kuma alamu a lamun somin hauka zub da miyau.Tuni na tsinke da al'amarinki dama Sumayya, zaki iya fiye da haka. Wato bayan kin tarwatsamin Zaman lafiyar yara, yanzu kuma kinzo kin gurb'atamin tarbiyyar yarona da na d'ebi shekaru Ina tarbiyya. To Wallahi hukuncin da zan d'auka a kan'ki ba iya ke kad'ai zai tsaya ba, har iyayenki, ko da yake baki ma dasu Sai kakanni, to har tsufansu bazan tausaya ba."
Cikin Kukan da da k'Yar yake fita saboda tashin hankali nace "Momi, Wallahi sharrin Khalifa ne, shine......"
Ta dakamin tsawa."Rufemin baki Munafukar banza,mai bak'ar a niya, da mugun hali, da mugun usuli."
Nan naga Ancle Fa'iz ya dubi Momi a hargitse, da alamun Furucinta ya Sosa masa rai sosai, Kawai ta tsira ne, saboda itan mahaifiyar sace.
Kuka na ya k'ara d'agawa, jin dad'in komai ya tafi yarda Khalifa keso, Shima ya dakamin tsawa.
"Rufemana baki, shaid'aniyar Kawai, haka kurum kin jefani halin halaka."
Ai kafin ya rufe baki, Ancle ya kwasheshi da wani irin wawan mari.Ai bansan Sanda na tsaida kuka na ba. Momi ma baki bud'e tayi tana kallon Fa'iz, haka ma Muhibbat ta wani zaro ido na Mamaki, haka Khairat. Shi kuwa Wanda aka Mara d'in dafe kunci yayi Yana kallon Yayan sa ido yayi tulu tulu, kamar zai rama, saboda k'uncin zuci
A zafafe Ancle yace "Matar tawa kake zagi kana dakawa tsawa? a gabana kuma? Lallai ka Isa tabbataccen Mara kunya, kuma Wallahi Sai na koya Maka hankali"
Nan Momi ta karb'a a fusace "Fa'iz, d'an uwanka Kaci zarafi ka tozarta a kan wannan 'yar iskar matar taka? to me yayi mata ma?ai kome yayi mata bai biyani ba. Wato Sam baka duba ma ga ta'asar da tayi, kai ta anzageta shine damuwarka ko?
Ya aro nutsuwa, da tausar zuciyarsa Sannan ya soma magana.
"Momi idan sumayya shaid'ani yace Khalifa ma shine, domin kuwa k'arfe d'aya baya amo, Sai da a bokin yin sa. Kuma in dai hukunci na gaskiya za'ayi to su duka za'a tuhuma, kuma a hukunta. Kuma in dai har an yarda Sumayya ita ta fara neman Khalifa, to kuma laifin'sa yafi girma, kuma yafi fitowa fili, domin kuwa d'akin Sumayya aka ganshi, ba ita aka gani a d'akin sa ba."
*🏤 NI DA GIDANA 🏤*
*_Littafi na daya_*
*NA*
*ZAINAB ILYAS MAZAWAJE*
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
📱22
________ Ga Wanda duk ya dubi Momi, zai ga alamun maganganun Ancle Fa'iz sun Shiga sun zauna Zuciyarta, amma saboda zafina da take ji, da tsana Sai ta sake tasowa Ancle Fa'iz da fad'a da bantab'a ganin shi tana yi masa ba cikin 'ya'yan'ta. Ina ganin kuma Muhibbat tana yiwa Momin rad'a a kunne da Ancle Fa'iz ya kau da kai. Tace a zuciye.
"Kar na sake jin ka dangantawa d'ana laifi irin na wannan banzar matar taka, rore roren tsiya. Yaro na Khalifa kin tsatstsene ita ta yaudareshi, idan ba haka ba me yasa da bai yi ba.? gaba d'aya ma Fa'iz ka fa canza daga d'an da na Sani, mai kishin 'yan uwan'sa da son su da tsananin son Momin'sa."
Ya dubi momin, cikin sanyaya murya.
"Ina nan Momi a sanin da kika yi min, fahimtata dai kika kasa yi." Ta girgiza kai.