← Book details Ni Da Gidana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 31

Sashe 17

Ni Da Gidana Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Ranar nayi bak'i sosai. Baba Talatu da Hajiya mariya suka fara bud'e fage. Da Tsokanar wasa na tarbesu nace
"Ku kuma tsofaffun nan Sai yau za'Ku gamo kai, Ku ringid'o kuzo? Ko Ku lek'oni jiya? Kuma naga duk mazajen nan ku ai naga duk tsofe, babu sabbon jini, sun zama jagwal, ballantana kuce tarairayar'su tasa kuka kasa Samun lokaci."

Hajiya Mariya tayi 'yar dariya tace
"Shak'iyyar wofi. Kwana biyu dai munji kunne, da kika yi gaba, yanzu kyayiwa mijinki kuma."

Baba Talatu, tace"Sa'a ma kika yi muka zo yau. Dama idan dad'i yay wa Mutum yawa, Sai yace Allah kasheni na huta. Da Kawunki Sulaiman cewa yayi, kar muzo, a bari a d'ebi lokaci tukun. Kakan kine, ma yace Sai munzo mun zo mun duba masa ke lallai, duk da dai bake kad'ai bace ma a gidan, ko menene ai da mata 'Yan uwanki ko?

Naji nauyi, na saddakai k'as nace kuma. "Yaya Kawuna yake?
Baba talatu, tace"Dama nasan shine a layin farko. To Lfy Lau yace a gaisheki da kyau." Na yi murmushi kuma nace.

"Allah sarki tsoho mai ran k'arfe, Yaya yake, kina kulamin da shi kuwa? (kakana). Tace

"Tace" Ko ke albarka.Lfy Lau yake, yace na gaisheki."

Hira sosai muka yi, daga bisani, na kaisu wurin Momi. Momi ta karb'esu da daraja Kam, suka yi tama hira, har Hajiya Mariya tace da Momi. Ina Angon yayi, bamu ganshi ba?"
Momi, tace"Sun tafi ziyarce ziyarce, shida Khalifa, d'azu. Tace"Ai nayi zaton jin za muzo ne, ya waske, gudun kar muzo muyi masa d'iban Karan mahaukaciya,saboda ya Samu, Sabuwa, ya ya damu gefe." A kasa dariya, a tare. Hirar barkwanci tsoffin nan sun Shashi da Momi. Hakan yay min dad'I Kam, sosai. Nuriyya tazo a ranar, kuma da ita muka yi ta tarben bak'i har girke girke, duk da momi ta aiko da nata daron tace a bawa bak'i.

****

A Sati na na d'aya a gidan, Ina zaune gaban mudubi Ina taje kaina, Wanda yasha washing da retourching, Yana ta shining ya kwanta lab'am. Ba kuma wani tsawo ne da shi ba can, iya saman kafad'ata yake tsayawa. Ina kuma alfahari da a bina a hakan.
Half vase ce a jikina, da under wear na siket iya gwiwa, domin kwalliya na gama nasa turarurruka na jiki, zan saka kaya na Kenan, naji an banko k'ofa da sauri, an shigo. razana nayi, bawai ga yanayin under wear Kawai dake jikina ba ma, saboda nasan babu mai iya shigomin d'aki kai tsaye haka ba, domin ko Ancle Fa'iz Mijina iya kacin'sa falo, bai tab'a Shiga cikin d'akina ba.

Wanda na yanke tsammanin Zai shigo, shid'in ne ya shigo. Ancle. Sau d'aya ya dubeni, kuma duban sauri da ya shigo ya wuceni ya isa kan gado, ya zauna. Na Samu sauk'in razana, ganin shine. Naja dogon Hijab na sallata nasa, na sake kai duba gareshi, cike da Mamaki. Da ganin'sa kasan daga wanka ya fito. Silk d'in sumarsa da bata taru da yawa ba, jik'e take da ruwa. Zulaika ce gajera a jikin'sa, da towel fari, sol, da ya sak'ala a kafad'a.
Nace"Lafiya kuwa, Ancle?" Kafin yace komai, k'ofar d'akin da take a bud'e ya tashi ya jawo ya rufe. Sannan
Yace

"Mutum, domin ya shigo d'akin matar'sa laifine?"
Na girgiza kai
"Ko kusa, my Ancle. Gani nayi baka tab'a shigowar bane"
Yace"To, yau na shigo, then so what?"
Nayi shiru, Ina kallon'sa.

Ya sake zama kan gadona, ya cire towel d'in da ya sagala a kafad'a ya ajiye gefe

"Sumayya, wani a bune ya faru, nake so, Kije falo ki zauna, ko da Momi ta aiko kirana, kice bananan"
Toh! Wata Sabuwa Inji 'yan caca. Kallon da nayi masa galala, yasan tambayace zan masa na dalili, ya katseni
"Karki tambayeni dalili. Just ki aiwatar, kyaji komai daga baya. Yanzu babu lokaci, kiyi sauri Kije"
Na ja zani zan d'aura, kasan Hijab yace"Kisa kayanki Mana, tun da kin d'ebo. Kiyi sauri amma.

Bani da zab'i face bin umarnin'sa da nasan zai iya jefani matsala babba, idan a kasamu kuskure a ka gane gaskiya. Amma k'arya kuma ba'halin Ancle Fa'iz bace, ko mai amfani ce. Tun da yau yayi kuwa, nasan da akwai babban dalili, ba kuma k'arami ba.

Na Shiga kici kicin cire Hijab domin saka Kayan da sauri, duk da nauyin'sa da yake zaune a d'akin yasa nake komai a sanyaye kuma. Sai naga shi d'in ma juyar da kan'sa gefe yayi ya jawo wani littafi irin na ma'aurata zalla da Nuriyya ta sayomin yana dubawa.
Ban gama d'aura d'an kwali bama na fito, na jawo k'ofar d'akin na barshi a ciki.

Na fara da kunna kallo, domin Samun Nutsuwar yin basaja.Amma, zuciya ta cike da tararrabi take, na me yake faruwa. Fatana dai ko maye, kar ya ritsa da ni, wurin yiwa Ancle Fa!iz Mijina biyayya. Ko minti biyar kuwa, ban cika da zama ba, Sai ga Muhibbat ta d'aga labulen k'ofata tana daga tsaye k'erere, da jin isar nan da fad"in rai tace "Yayan Yana nan?"
Nace
"A'a bai shigo ba ai ."
Ta tsuke fuska" To, Ina zai Shiga Kenan?"
Nayi tsai, Ina kallon'ta Sai kuma nace

"Kin duba, d'akinsa baya nan?" Bata amsamin ba, illa tsaki da taja, ta Saki labulena ta tafi. Na d'an ji ciwon hakan. A binda na kasa tantancewa, ni take yiwa tsakin, ko kuwa rashin ganin Yayan nata.
Bayan mintuna da fitarta na Shiga d'akin, na sameshi, a kwance ma yake a binsa. Nace"Muhibbat tazo nace mata baka nan, Wai don Allah me ya faru ne?"
Yace
"Zan fad'a Miki, Jeki d'akina ki d'auko min Kaya marasa nauyi, shirt da jins, ko T. Shirt da troser da takalmi, da under's, a Kwai sababbi da ban bud'e ba under's, su za'ki d'ebo." Nace" Tom."

Da na fito a d'arare, nayi sa'a duk suna saman Momi, Ina jiyo hayaniya kuma. Na Shiga d'akin Ancle, a karo na farko. Gado ne Kawai da kwabar zuba Kaya,set, da kujerar zama. Na bud'e kwabar, duk na d'auko Kayan da ya sa na d'ebo. Wasu Kayan duk a hargitse, bayan da gogaggu a ciki. Nafi zaton wurin neman wani abu ya hargitsa.
Da na kawo masa, na d'ebo mayuka da turarurruka na jiki da na Kaya, da comb nawa. Domin ban d'auko nasa ba. Yace"Sumayya kwashe Turaren nan, banasa turare mai k'arfi, Sai mai sent, cool, irin nawa. Nace "To" kuwa na kwashe.
Na fito na barshi yana shiryawa. Da na fuskanci ya gama na kai masa Karin kumallo d'akin. Tea da soyayyan plantain ne da k'wai da Khairat ta kawomin.
Ya juyo Yana mai gyara botton d'in riga yace"Ke me zaki ci, da kika kwaso Break fast d'inki kika kawomin?"
Nace"Ancle, ai yayi min yawa dama, na Mutum biyu Khairat ta kawo."
Yace "Duk da haka, Kije ki karya, idan yayi Miki yawa kikai kichean a ba mabuk'aci. Ni a waje zan karya ma."
Ba haka na so ba, na maze amma, saboda na soma karantarsa, idan yace Bazai yi a buba, to fa rabu da shi Kawai. Na kwashe Kayan da ya cire da nufin wankewa ko ba lokacin ba. Na zauna a falo. Ya fito yace"Zan fita, ki rufemin d'akina an jima, mukullan suna kan tebur d'in ward robe." "Nace"To, Ancle"

Sai da ya lek'a tsakar gidan, yaga babu kowa Sannan yay wuf ya arce.
Nayi masa a dawo Lfy, Bayan ya Fice, bai amsa ba, shi yasa nasan bai ji bane.
Bansan me yake faruwa ba, amma Ina ta jiyo hayaniya a Saman Momi, da a lamu bak'ine.
K'arfe takwas na dare, Ancle Fa'iz ya dawo. Dama yakan lek'Oni, kafin ya wuce wurin Momi, idan ya dawo. Daga bakin k'ofar yace"Bari naje wurin Momi, naga yarda zamu kwashe da ita,Sai nazo na fad'a Miki kome ya faru, nasan kin zak'u. "

Yafi a wa d'ya, kafin ya dawo. Na d'ebo turare cikin show glass ya shigo. Kan kujera two seater ya zauna. Nima Sai nazo kusa da shi dab, na zauna. Nace"Nayi zaton kamanta fa"
Yace
"Yaya zan manta, Bayan ninace zan fad'a Miki. Ya kwantar da kan'sa jikin tudun kujera ta baya, cikin galabaitacciyar murya yace"Don Allah Sumayya ki daina saka wannan turaren d'akin mai k'arfi. Wanda kike sawa ma na jiki sent d'insa is high. Turare mai k'arfi har kaina yake hawa."
Na danne, ba dad'in da naji nace"To my Ancle, zan daina sawa na samu air freashner Kawai mai sanyin k'amshi na d'aki. Na jiki kuma zan saka iya body spray sansanya.
Chapter 17 · 0% Book details