Sashe 16
Ni Da Gidana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tare muka Shiga hada hadar girkin safe da su Khairat, duk da Khairat tayi tayi na bar aikin sayi nak'i. Ta Hak'ure, Sai gashi muna aikin tare cikin armashi, har 'yar hira mu keyi. Ita kuwa Muhibbat baya ga gaisuwa bata sake cemin komai ba. Bayan miskilanci, ma naga tana Fama da jin kai ainun, ko irin yanayin Yayan tane da ita ban Sani ba. Amma shi Ancle sanadin aure ya d'an sauya,tun da har yana 'yar hira dani. Ta yiyu ita ma ta sauya idan an Kwan biyu, amma fa a zatona.
Muhibbat dai tafiyar ta tayi ta barmu da aikin, kuma na lura sanadin zuwa na ne. Khalifa ne ya lek'o kichean d'in ya soma yiwa Khairat Maganar ta dafa masa ruwan wanka idan ta gama.Sai kuma yayi Jim, da ya ganni, in da ya sake bina da mayataccen kallo, Sannan ya Mik'o gaisuwarsa gareni.. Na amsa da sauri na kau da kai na ci gaba da a binda na keyi. Zuciyata bata sak'amin komai ba, game da Khalifa, Kawai banajin dad'in kallon da yake yi min ne, ko santaran nake babu aure. Ban Sani ba, ko shi kuma tasa d'abi'ar Kenan, ko kuma wani k'uduri ne a ransa. Amma yaya zanyi, tun da k'addara ta cilloni gidan'su.
Bayan ya tafi, Khairat tace "Yaya Khalifa ya cika matsawa mutane idan yaga a na aiki. Da da wutar nefa ma Sai na jona masa a Heater ko electric cooker. Amma tunda Yaya Fa'izu ma zaice na dafa masa ruwan wanka,, Sai Kawai na had'a musu wuri guda."
Nace"Bari na d'ora musu a gas cooker d'ina, idan yaso Sai ki d'ebarwa Khalifa nasa, kin San yanzu ruwan sanyi bazai zububa a jiki, dole Sai an d'an dafa, tun da da ragowar sanyi, tun da kuma safiya ce, Kije kiyi shirin makaranta, kar ki makara, naji kina tambayar lokaci, na k'arasa soya dankalin."
Tace "Gaskiya Kam. Kin hutashsheni ma, na gode Anti Sumayya. Dama na kusa latti Wallahi, wannan Yaya Khalifan Zai sake b'atamin lokaci. N'a gode."
Nace"Kai Khairat, Ina a bin godiyar, ai anzama d'aya."
Cikin mintina kafin ta shirya, Na dafa ruwa, ta Mik'awa Khalifa nasa. Ban bata na Ancle Fa'izu ba, nace na a jiye masa, duk da na fahimci ita ke yi masa wannan aiki, ba kuma fasa bata zai yi ba na Sani saboda ni. Ni kuma na Hak'k'ak'e aikin ya dawo hannu na duk runtsi.
Da na gama na zuba komai a mazubin da ya dace. Daga Sama na jiyo muryar Momi, nan nasan ta tashi Kenan.
Na nufi benen domin na gaishe su har Abban. Amma gyaran muryar Abban da naji yana saukowa daga benen na dakata. Saye yake da babbar riga babu ta ciki. Nan nasan iya k'ofar gida zai fita. Na tsuguna na gaisheshi. Cike da farin ciki sosai ya amsa, ya tambayi lafiyata da yarda na kwana."Allah ya shi albarka, ya Baku zaman lafiya 'yata." Ba kad'an ba naji dad'in addu'ar nan tasa. Ko ba 'ace ba,kana ganin sa kaga Mutumin K'warai mai karimci. Fara'a Kam a fuskar sa kamar gonar auduga.
Nasa kai da nufin d'aga labulen mai kauri da ba'a ganin na ciki, na tsinkayi maganganun, kuma farko Sunana naji an kira, shine dalilin da gabana ya fad'i Na kasa Shiga, in da maganganun suka tayi ta tururuwar Shiga kunne na. Muryoyin Khalifa ne da momi.
"Sumayyan ai babu laifi Itama Khalifa.Tana da hankali da nutsuwa ga alamu ga ladabi. Gashi tana karatu, amma banga alamun wayewar banza a tare da ita ba kamar wasu."
Yace
"Momi, bafa a saurin yabon d'an kuturu, Sai ya mutu da yatsu."
Ta karb'eshi
"Haka ne Khalifa Sai ya mutu da yatsu."
Ya sake cewa.
"Momi, nifa tun kafin ma na ganta na tsaneta. Da na ganta Sai nafi tsanarta. Kallon k'urillama nayi tayi mata, domin naga me Yaya Fa'izu ya gani, a jikinta har ya zab"i auren'ta, amma bangani ba. Momi mai kafirin wayoce fa Yarinyar nan, da iya kissa, daga zuwa har ta zama 'yar gida?anya bazata d'auke Miki hankalin d'aba a gaba?
Da bata ce komai ba ya zarce
"Momi amma fa Yaya Fa'iz ya kwafsa, kan a bu kad'an yayi wani auren huce haushi, kodai k'arawa kai haushi, tun da na tabbatar Salima kad'ai yake so a duniya. Laifin mominta ai
bai kamata ya shafeta bako?"
Nan momin tace" Shima ai ba Salimar yayi nufin b'atawa ba, nufin sa na kan mamanta, amma dole ita zata fi kowa jin ciwon hukuncin da ya zartar na yin aure.Nasan labarin bai same ta ba, tun da kaji shiru.Amma dai ya aikewa da iyayenta katin d'aurin aure, ta yiyu bata ji ba.Nima banji dad'in a binda yayi ba na zartar da hukuncin yin aure, a matsayin ramuwa. Nafi son sa da Salimar sau dubu. Babu yarda banyi ba, na hanashi auren nan, amma ya dameni da magiya da lallami, kullum har Sai da na saduda. Ni kunyar had'a ido nake da Salimar ma Wallahi. Yarinyar dake mutuwar son'sa, duk in da d'an uwan sa yake, Sai da ta nemi Sani. Bata gajiya da yi Mana d'awainiya, jikinta bai huta ba, haka ma kud'inta. Amma a ce sakayyarta Kenan? Gaskiya Sai yanzu nake jin ciwon auren ma, bayan anyi. Ko a waya kunyar Mu gaisa nake ji. Kasan Kusan kullum tana bugowa ta gaisheni."
Khalifa yaja dogon tsaki.
"Dole ma Yarinyar nan tabar gidan nan Momi, dole ya sallameta, ko bai shirya ba."
Momin tace"Wani irin furuci kake yi Khalifa? Kai ke auranta, ko kana da wani k'arfin iko ne a kan mai auranta? ai babu Maganar dole, tun da Shima ba sonta yake yi ba, yarda na fuskanta , kama hutar da kanka. Idan d'an koli Yaci kasuwa, ai gida yake komawa ko?"
Khalifa yace "Haka ne Momi. Ni dama babbar damuwata, kar ta ritsa dani. Saboda Salima tace za'ta samomin aiki na acounter a kamfanin babanta. Kinga idan auren ta da Ancle Fa'izu bai yiyu ba, ko taji yayi auren nan, Yaya kike zaton makomata Momi? Ni za'ayiwa buk'ulu fa. Ai dole na shirya munak'isar da zai Saki Yarinyar nan Momi, idan naga bashi da niyyar sallamarta da wuri."
Ban tsaya naji me momin zata ce ba, na juya a hankali na sauko, saboda idan na Shiga za'su tsargu. Idan kuma na ci gaba da tsayuwa, za'su iya fitowa su ganni.
Nayi zaune a d'aki, damuwa duk ta baibayeni. Maganganun Khalifa su sukafi zafafa k'wak'walwa ta. Bansan zan fuskanci Wata matsala ba kuma a gidan, bayan ta b'angaren Mijina da nake tunanin ita kad'aice da zan ji da ita. To A she bayan matsalar da nake da ita ta Mijina, duk gidan ma Ina da matsala da su, babu mai yi dani a she duk sun fison Mijina da Salima. Gaskiya naga Muhibbat Sai wani fizga fizga take min. Momi farin cikin Ancle, Fa'iz tace ta fison Salima sau dubu dani. To ko iya nan matsala ta ta tsaya, ai da aiki gagarimi a gabana. Ancle baya had'a kaunar momin sa da ta kowa. To ni kuwa da wanne zan soma? Ta Ina zan fara? Da yaya zan soma warware matsalolin da suka yi min k"awanya hagu da dama?.
*🏤 NI DA GIDANA 🏤*
*_Littafi na daya_*
*NA*
*ZAINAB ILYAS MAZAWAJE*
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
📱14
______Duk da wad'annan matsaloli dake gabana, amma domin k'arfin hali Wai b'arawo da sallama, Zuciyata Sai rad'amin take da cewa
Sumayya karki kaya, ba"a sanin maci tuwo, Sai miya ta k'are, kuma mai zabarin nema, yana tare da nasara, wataran, musamman mai nagarta.
Ni dai nasan, bawai nacin son Ancle Fa'iz ko ya Soni, shine babbar matsalata ba. A ra'ayina, a tsarina, babu a binda nak'i jini irin a ce nayi aure ya mutu, Sannan a ce ma ban dad'e ba. Sam! ban shiryawa Zaman zawarci ba, ban kuma shiryawa amsa sunan bazawara ba. Domin Muddin wa'adin aure na da Ancle Fa'izu ya cika ya sallameni, ban isa na goge tambarin sunan bazawara a goshins ba.
Nasan samarina ma zasu samu labari, suyi min dariya, musamman Usman, daya da ya tab'a yab'amin magana da Karin magana, yace Wai k'arshen a lewa dai kasa ce, suna nan suna zuba ido kuma, suga k'arshen'ta. Shi zaton'sa wani mai iko sosai na samu na barshi.
Bayan wani lokaci, na koma na gaishe da Momi. Sam Banga wani sauyi a tare da ita ba, Sai ma bangajiya, da tayi min, da cewa, Wai taji nice jigon aikin komai, na Karin kumallon ranar. Khairat dama ita ta kwashe komai, ta kaiwa kowa. Nima har d'aki ta biyo ni dashi. Tace min
"Anti Sumayya, na tafi makaranta. Fuska ta cike da fara'a nace"To, a dawo lafiya, K'anwata." Khairat, ita ce na tabbatar tana k'aunata da zuciya guda. Kuma nima ta Shiga raina, tashi d'aya.
Har lokacin, banga Ancle Fa'iz ba, ya fito daga d'akin'sa ba. Bacci yake ko menene, ban Sani ba. Kamar na Shiga na gaisheshi, na kasa.
Na had'a ruwan wanka mai zafi dai dai dai, nasa turarrurukan wanka, na rufe da murfin babban bokitin wankan,mai kyau.
Sai da na gama shiryawa, na zauna a falo, Ina karyawa, Sannan na jiyo muryar Ancle Fa'iz shida Khalifa a tsakar gida suna magana. Nan nasan a she Khalifa, ba fita yayi ba. Kafin na farga naji sallamar Ancle Fa'iz. Amma daga bakin K'ofa ya coge, muka gaisa. Nace"Ancle ga ruwan wankan ka can fa na kaima bathroom. Kallona naga yayi, Sai yayi d'an Jim, kamar bazai ce min komai ba. Ni kuwa nasan shammatar'sa nayi, shi yasa na sashi a kwanar nazarin yarda zai yi da katsalandan d'in da nayi, na binda bayaso nayi. Wato yi masa d'awainiya ko Wacce iri.
Nace
"Ancle, Fa'iz kajini kuwa?"
Ya shafi, kyakykywar
bak'ar sumar'sa da take a kwance ta soma fesowa, daga askin da yayi mai suna SKIN, da yay masa kyau kuwa sosai.
Yace"Naji ki Sumayya."
Daga haka bai sake cewa komai ba, ya tafi. Nasan da bai a mince ba, zai fad'amin ba ya so, tun da bashi da rufi, ko alkunya.
Muhibbat dai tafiyar ta tayi ta barmu da aikin, kuma na lura sanadin zuwa na ne. Khalifa ne ya lek'o kichean d'in ya soma yiwa Khairat Maganar ta dafa masa ruwan wanka idan ta gama.Sai kuma yayi Jim, da ya ganni, in da ya sake bina da mayataccen kallo, Sannan ya Mik'o gaisuwarsa gareni.. Na amsa da sauri na kau da kai na ci gaba da a binda na keyi. Zuciyata bata sak'amin komai ba, game da Khalifa, Kawai banajin dad'in kallon da yake yi min ne, ko santaran nake babu aure. Ban Sani ba, ko shi kuma tasa d'abi'ar Kenan, ko kuma wani k'uduri ne a ransa. Amma yaya zanyi, tun da k'addara ta cilloni gidan'su.
Bayan ya tafi, Khairat tace "Yaya Khalifa ya cika matsawa mutane idan yaga a na aiki. Da da wutar nefa ma Sai na jona masa a Heater ko electric cooker. Amma tunda Yaya Fa'izu ma zaice na dafa masa ruwan wanka,, Sai Kawai na had'a musu wuri guda."
Nace"Bari na d'ora musu a gas cooker d'ina, idan yaso Sai ki d'ebarwa Khalifa nasa, kin San yanzu ruwan sanyi bazai zububa a jiki, dole Sai an d'an dafa, tun da da ragowar sanyi, tun da kuma safiya ce, Kije kiyi shirin makaranta, kar ki makara, naji kina tambayar lokaci, na k'arasa soya dankalin."
Tace "Gaskiya Kam. Kin hutashsheni ma, na gode Anti Sumayya. Dama na kusa latti Wallahi, wannan Yaya Khalifan Zai sake b'atamin lokaci. N'a gode."
Nace"Kai Khairat, Ina a bin godiyar, ai anzama d'aya."
Cikin mintina kafin ta shirya, Na dafa ruwa, ta Mik'awa Khalifa nasa. Ban bata na Ancle Fa'izu ba, nace na a jiye masa, duk da na fahimci ita ke yi masa wannan aiki, ba kuma fasa bata zai yi ba na Sani saboda ni. Ni kuma na Hak'k'ak'e aikin ya dawo hannu na duk runtsi.
Da na gama na zuba komai a mazubin da ya dace. Daga Sama na jiyo muryar Momi, nan nasan ta tashi Kenan.
Na nufi benen domin na gaishe su har Abban. Amma gyaran muryar Abban da naji yana saukowa daga benen na dakata. Saye yake da babbar riga babu ta ciki. Nan nasan iya k'ofar gida zai fita. Na tsuguna na gaisheshi. Cike da farin ciki sosai ya amsa, ya tambayi lafiyata da yarda na kwana."Allah ya shi albarka, ya Baku zaman lafiya 'yata." Ba kad'an ba naji dad'in addu'ar nan tasa. Ko ba 'ace ba,kana ganin sa kaga Mutumin K'warai mai karimci. Fara'a Kam a fuskar sa kamar gonar auduga.
Nasa kai da nufin d'aga labulen mai kauri da ba'a ganin na ciki, na tsinkayi maganganun, kuma farko Sunana naji an kira, shine dalilin da gabana ya fad'i Na kasa Shiga, in da maganganun suka tayi ta tururuwar Shiga kunne na. Muryoyin Khalifa ne da momi.
"Sumayyan ai babu laifi Itama Khalifa.Tana da hankali da nutsuwa ga alamu ga ladabi. Gashi tana karatu, amma banga alamun wayewar banza a tare da ita ba kamar wasu."
Yace
"Momi, bafa a saurin yabon d'an kuturu, Sai ya mutu da yatsu."
Ta karb'eshi
"Haka ne Khalifa Sai ya mutu da yatsu."
Ya sake cewa.
"Momi, nifa tun kafin ma na ganta na tsaneta. Da na ganta Sai nafi tsanarta. Kallon k'urillama nayi tayi mata, domin naga me Yaya Fa'izu ya gani, a jikinta har ya zab"i auren'ta, amma bangani ba. Momi mai kafirin wayoce fa Yarinyar nan, da iya kissa, daga zuwa har ta zama 'yar gida?anya bazata d'auke Miki hankalin d'aba a gaba?
Da bata ce komai ba ya zarce
"Momi amma fa Yaya Fa'iz ya kwafsa, kan a bu kad'an yayi wani auren huce haushi, kodai k'arawa kai haushi, tun da na tabbatar Salima kad'ai yake so a duniya. Laifin mominta ai
bai kamata ya shafeta bako?"
Nan momin tace" Shima ai ba Salimar yayi nufin b'atawa ba, nufin sa na kan mamanta, amma dole ita zata fi kowa jin ciwon hukuncin da ya zartar na yin aure.Nasan labarin bai same ta ba, tun da kaji shiru.Amma dai ya aikewa da iyayenta katin d'aurin aure, ta yiyu bata ji ba.Nima banji dad'in a binda yayi ba na zartar da hukuncin yin aure, a matsayin ramuwa. Nafi son sa da Salimar sau dubu. Babu yarda banyi ba, na hanashi auren nan, amma ya dameni da magiya da lallami, kullum har Sai da na saduda. Ni kunyar had'a ido nake da Salimar ma Wallahi. Yarinyar dake mutuwar son'sa, duk in da d'an uwan sa yake, Sai da ta nemi Sani. Bata gajiya da yi Mana d'awainiya, jikinta bai huta ba, haka ma kud'inta. Amma a ce sakayyarta Kenan? Gaskiya Sai yanzu nake jin ciwon auren ma, bayan anyi. Ko a waya kunyar Mu gaisa nake ji. Kasan Kusan kullum tana bugowa ta gaisheni."
Khalifa yaja dogon tsaki.
"Dole ma Yarinyar nan tabar gidan nan Momi, dole ya sallameta, ko bai shirya ba."
Momin tace"Wani irin furuci kake yi Khalifa? Kai ke auranta, ko kana da wani k'arfin iko ne a kan mai auranta? ai babu Maganar dole, tun da Shima ba sonta yake yi ba, yarda na fuskanta , kama hutar da kanka. Idan d'an koli Yaci kasuwa, ai gida yake komawa ko?"
Khalifa yace "Haka ne Momi. Ni dama babbar damuwata, kar ta ritsa dani. Saboda Salima tace za'ta samomin aiki na acounter a kamfanin babanta. Kinga idan auren ta da Ancle Fa'izu bai yiyu ba, ko taji yayi auren nan, Yaya kike zaton makomata Momi? Ni za'ayiwa buk'ulu fa. Ai dole na shirya munak'isar da zai Saki Yarinyar nan Momi, idan naga bashi da niyyar sallamarta da wuri."
Ban tsaya naji me momin zata ce ba, na juya a hankali na sauko, saboda idan na Shiga za'su tsargu. Idan kuma na ci gaba da tsayuwa, za'su iya fitowa su ganni.
Nayi zaune a d'aki, damuwa duk ta baibayeni. Maganganun Khalifa su sukafi zafafa k'wak'walwa ta. Bansan zan fuskanci Wata matsala ba kuma a gidan, bayan ta b'angaren Mijina da nake tunanin ita kad'aice da zan ji da ita. To A she bayan matsalar da nake da ita ta Mijina, duk gidan ma Ina da matsala da su, babu mai yi dani a she duk sun fison Mijina da Salima. Gaskiya naga Muhibbat Sai wani fizga fizga take min. Momi farin cikin Ancle, Fa'iz tace ta fison Salima sau dubu dani. To ko iya nan matsala ta ta tsaya, ai da aiki gagarimi a gabana. Ancle baya had'a kaunar momin sa da ta kowa. To ni kuwa da wanne zan soma? Ta Ina zan fara? Da yaya zan soma warware matsalolin da suka yi min k"awanya hagu da dama?.
*🏤 NI DA GIDANA 🏤*
*_Littafi na daya_*
*NA*
*ZAINAB ILYAS MAZAWAJE*
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
📱14
______Duk da wad'annan matsaloli dake gabana, amma domin k'arfin hali Wai b'arawo da sallama, Zuciyata Sai rad'amin take da cewa
Sumayya karki kaya, ba"a sanin maci tuwo, Sai miya ta k'are, kuma mai zabarin nema, yana tare da nasara, wataran, musamman mai nagarta.
Ni dai nasan, bawai nacin son Ancle Fa'iz ko ya Soni, shine babbar matsalata ba. A ra'ayina, a tsarina, babu a binda nak'i jini irin a ce nayi aure ya mutu, Sannan a ce ma ban dad'e ba. Sam! ban shiryawa Zaman zawarci ba, ban kuma shiryawa amsa sunan bazawara ba. Domin Muddin wa'adin aure na da Ancle Fa'izu ya cika ya sallameni, ban isa na goge tambarin sunan bazawara a goshins ba.
Nasan samarina ma zasu samu labari, suyi min dariya, musamman Usman, daya da ya tab'a yab'amin magana da Karin magana, yace Wai k'arshen a lewa dai kasa ce, suna nan suna zuba ido kuma, suga k'arshen'ta. Shi zaton'sa wani mai iko sosai na samu na barshi.
Bayan wani lokaci, na koma na gaishe da Momi. Sam Banga wani sauyi a tare da ita ba, Sai ma bangajiya, da tayi min, da cewa, Wai taji nice jigon aikin komai, na Karin kumallon ranar. Khairat dama ita ta kwashe komai, ta kaiwa kowa. Nima har d'aki ta biyo ni dashi. Tace min
"Anti Sumayya, na tafi makaranta. Fuska ta cike da fara'a nace"To, a dawo lafiya, K'anwata." Khairat, ita ce na tabbatar tana k'aunata da zuciya guda. Kuma nima ta Shiga raina, tashi d'aya.
Har lokacin, banga Ancle Fa'iz ba, ya fito daga d'akin'sa ba. Bacci yake ko menene, ban Sani ba. Kamar na Shiga na gaisheshi, na kasa.
Na had'a ruwan wanka mai zafi dai dai dai, nasa turarrurukan wanka, na rufe da murfin babban bokitin wankan,mai kyau.
Sai da na gama shiryawa, na zauna a falo, Ina karyawa, Sannan na jiyo muryar Ancle Fa'iz shida Khalifa a tsakar gida suna magana. Nan nasan a she Khalifa, ba fita yayi ba. Kafin na farga naji sallamar Ancle Fa'iz. Amma daga bakin K'ofa ya coge, muka gaisa. Nace"Ancle ga ruwan wankan ka can fa na kaima bathroom. Kallona naga yayi, Sai yayi d'an Jim, kamar bazai ce min komai ba. Ni kuwa nasan shammatar'sa nayi, shi yasa na sashi a kwanar nazarin yarda zai yi da katsalandan d'in da nayi, na binda bayaso nayi. Wato yi masa d'awainiya ko Wacce iri.
Nace
"Ancle, Fa'iz kajini kuwa?"
Ya shafi, kyakykywar
bak'ar sumar'sa da take a kwance ta soma fesowa, daga askin da yayi mai suna SKIN, da yay masa kyau kuwa sosai.
Yace"Naji ki Sumayya."
Daga haka bai sake cewa komai ba, ya tafi. Nasan da bai a mince ba, zai fad'amin ba ya so, tun da bashi da rufi, ko alkunya.