Sashe 31
Kishiya Ko Baiwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin muryan lallashi Ahmad yace"kiyi hakuri My Queen kidena wahalar da bakinki akan wannan bakauyiyar yarinyar ni nasan matanki da zan dauka akanta Wanda setayi danasa ni akan abinda ta aikata miki,domin babu wani mahalukin daya isa ya wulakanta ki in kyalesa komai matsayinsa aduniya bare kuma kaskantacciya mara mutunci."Hannu tasanya tashare hawayen dake ambaliya afuskart,cikin dauriya da kafewar zuciya tace"Naji ni kaskantacciya ce awajenka,dama bana neman ka daukakani"daukakar Allah nake bukata bana mutum ba,Maganar danasani kuwa na nawa ya Ahmad!?ai danasani tunda ga ranan dana shigo cikin gidanka, amatsayin matarka nakeyi kuma har gobe bazan dena ba harse ranan da kagyara rayuwar ka, kadawo cikekken namiji mai cike da ikon fada agidan sa Wanda yasan hakkin aure yakuma San hakkin Allah akansa kana yasan halak da haram,hmm ya Ahmad ina mai tausaya maka ranan da ubangiji ze tsaidaka agabansa ya tambayeka hakkin daya baka akan matanka shin maizaka fada masa!?...Cikin wani irin matsanancin fushi da tsanarta yakwasheta da mari.wanda yasanya ta faduwa tabuga kanta ahannun kujeran atake wajen yakumbura.Cikin rashin tausayi yasanya hannunsa yadagota tare da shake wuyanta mari yashiga kifa mata hagu da dama yana cewa Wallahi ko duk duniyar nan gatankine yau sena nunamiki ni basa ankibane,Inaso ko mafarki kikayi kinyi musayar yawu dani inkintashi kirazana bare kuma kiyimin rashin kunya.Kafewa idanunta sukayi asama sekakari take,dakyar ta iya kokarin daga hannunta tarike nasa dan kwatar kanta anma ta kasa danko gezau beyiba,zubawa sarautar Allah ido tayi domin tasan yau karshenta yazo.
Ganin yana kokarin kisa yasa Nadiya saurin karasowa tarike hannunsa,Cike da tsoro tace"Honey sake mata wuya karka kasheta kaja mana bala'i!.kinsaketa yayi sema sake matse ta dayayi ajikin bango da duka karfinsa dan wani irin tsanarta yayi acikin rayuwar sa gwanda yakasheta kowa yahuta.Cikin tashin hankali Nadiya tabuga masa tsawa tare dacewa wai bazaka saketa bane seka kasheta!!??tafada tana janye hannunsa ganin ko motsi Sukainat tadena"Saketa yayi yana wani irin huci afusace yajuya yafice daga dakin.Zubewa Suky tayi sumammiya awajen"Cikin sauri Nadiya tabude Frigg tadauko ruwa me sanyi tasheka mata.Numfashi taja,kana tabude idanunta dasuka kada sukayi jawur dasu"Ganin ta farfado yasa Nadiya tajuya tafice...
Kuka Sukainat tafashe dashi Wanda muryanta befita,se hawaye dake ambaliya akan innocent face dinta.Dakyar ta Iya mikewa tashiga toilet ruwan zafi takunna tagasa jikinta da goshinta dake mata zafi,kafin tafito kan gado tafada"tayi rigingine, sotake bacci yadauketa kozata rage damuwar dake ranta anma Hakan yaki domin idanunta bushewa sukayi ba alamar bacci acikinsu.Rufin
P.O.P dake dakin tazuba wa idanu tana tunanin rayuwa,baki daya bata da sa'a acikin rayuwar ta. Ahmad yazame mata karfen kafa tun daga ranan data shigo cikin gidansa take cikin bakin ciki da takaici Wanda batasan ranan karewar saba
.Lumshe idanunta dake cike da hawaye tayi tana, tuna ranan data fara haduwa da Ahmad acikin rayuwar ta ranan da kaddararta tasauya izuwa kunci da bakin ciki,takuma dawo baiwa.Hawayene suka wanke mata fuska lokacin data tuna ahanyar ta nadawo daga islamiyya tahadu dasi.lokacin da aka tashe a islamiyya yamma yayi sosai kasancewar zasuyi musabaka hakan yasa suka dade,se da tafito taga hadari yahadu bakikkirin yana bada iska alamar daf ruwa yake da saukowa,gashi babu masu abin hawa hawa duk da kasamcewar tsakanin dutsen tanshi da federal Sacateria bawani nisa sosai.Hong dataji yayi yawa abayanta yasa tayi saurin matsawa gefe batare data juyaba domin sauri take ta Isa gida,sake danna mata hong akayi da karfi, hakan yasa tajuya akuma dede lokacin ne ruwan sama ya barke kamar da bakin kwarya.Zuge glass din motar yayi cike da nutsuwa yace"Barka da wannan lokacin kanwata,amsawa tayi da yauwa"tana kokarin barin wajen ganin yanda ruwa kedukanta,cikin kasa da murya yace"kishigo in rage miki hanya karmura yakamaki!,kai ta girgiza masa cikin yanayin sanyinta tace"ngd.sake sassauta murya yayi yace"pls kishigo mana inrage miki hanya"kin amincewa tayi.Duk Magiyan da yaitamata kantashiga yarage mata hanya anma fir taki. tayi tafiyar ta acikin ruwan yayinda shikuma yadinga bin bayanta ahanli har ta Isa Gida batare datasan yana biye da ita ba...
Sukainat kitashi kibamu abinci"Muryan Rufaida yakatse mata tunanin datake"Ahankali tabude kumburarrun idanunta takalle ta,Cikin muryan ta dabaya fita sosai tace"banyi girkiba.Dariyan shekiyanci Rufaida tasheke dashi kafin tace"Meyasa meki haka kofaduwa kikayi ko kuma kinyi fada ne amafarki da wacce tafi karfin ki!?hhhh gardiya tafadi akasa, tana gama fadin haka tafice daga dakin tana dariyar mugunta,dan dama ba yunwa takejiba Nadiya ce tasanya ta zuwa tambayi abinci...
Shiga parlour tayi tana dariyar mugunta hadda rike ciki,Hararanta Hjy kultum tayi tace ke lafiya kike irin wannan dariyar kamar wata zararriya.tsagaita dariyar tayi tace"Wlh grany bakiga fuskar Sukainat bane kamar wacce sukayi kokuwa da kada..Fashewa da dariya Nadiya tayi tace ke banson karya fa"Allah Momy bakarya nakeba dagaske nake..
Tsaki Hjy Kultum taja tace taje can takarata da mugun halinta matsalar tace duk bakin halinta kanta zekare ai,Ina aikar da aka miki tafada tana kallon Rufaida!?cewa tayi batai girki ba"anma bari nakira miku ita sekuga yanda fuskarta tayi, tana gama fadin haka tafice batare datajira jin amsar suba,tana shiga dakin babu sallama tace" Sukainat kawar kada kizo Hjy tazo kugaisa...Da kallo Sukainat tabi bayanta,tana mamakin sunan data kirata dashi wai kawar kada,kawar da tunanin tayi aranta kana tamike ahankali tadauki hijab dinta tafita daga dakin...
Kanta akasa tashiga parlour,bakinta dauke da sallama"Ko kallon ta basyi ba bare tasamu arzikin amsa salamarta.Bata damu da hakan ba domin inda sabo yaci ace tasaba da hallayar su.
Cike da ladabi ta tsugunna kusa da kujeran da Hajiya kultum ke kai tace"Sannu da zuwa Hjy fatan kinzo lafiya!?,Azabure Hjy kultum tamike tana watsa mata kallon tsana tace."Bana bukatar gaisuwarki mara tarbiya,se kizo kina wani sissinne kai kamar mutuniyar arziki!"maza fice kibani waje bana kaunar ganin wannan shedaniyar fuskar taki.Batace komai ba tamike tana kokarin hana kanta hawaye domin bataso suga raunin ta.Haba Sukainat kamata yayi kitsaya kibata hakuri dan Hjy kamar uwa take agareki,bekamata kinuna fushin ki kan tayi miki fada ba,anma yanda kika mike din nan yananu ni da kinfusata da fadar datai miki, takarashe tana satan kallon Hjy kultum dake jijjiga kafa cike da bala'i.
Murmushin takaici tayi,tarasa meta tsarewa Nadiya arayuwarta Wanda bata da burin daya wuce taga ta kuntatawa rayuwar ta."Cikin dashash'shiyar muryan ta da befita sosai tace"Wallahi ko daya banji takaicin kalaman Hjy ba dan yanda zan daraja Ummi na haka itama zan darajata amatsayinta na mahaifiyata...Cikin sauri Hjy kultum tadaga mata hannu tana huci tace"Allah yasauwa ke min in haifi mujiya kamar ke,me bakin jini da mugun hali,kije can kinemi uwarki anma ni bana fata in zama uwarki,dan da nahaifi irinki gwanda inda wama bani da 'da aduniya lalacacciya kawai...Cikin sauri Sukainat tafice daga dakin tana matsar kwalla,dan bazata Iya jure zama suna jifanta da munanan kalamai ba gara tafice tabasu waje.
Bayan fitarta Nadiya takalli Hjy kultum tana tabe baki tace"Hjy Wallahi yarinyar nan ta mugun renaki Sam bata ganin girmanki da kimarki sekace ke basurukar taba ce!,tafi karfin baki hakuri kenan akan lefin data miki gaskiya Hjy sekinyi gaggawar daukar mataki a kanta inba haka ba nan gabama se tayi abinda yafi wannan!?.Kwafa Hjy kultum tayi tace"bar matsiyaciyar yarinya ninasan maganinta dan sena dauki tsatstsauran mataki akanta...
Se bayan sallan la'asar Ahmad yashigo gidan agajiye.Lokacin dayashigo Hjy kultum nashirin tafiya ganin sa yasa takoma tazauna.Kusa da ita yazauna yagaishe ta"amsawa tayi da murmushi afuskarta tana tambayar sa kasuwa?"Dan yamutsa fuska yayi yace"Kasuwa babu dadi dan acikin wata daya nayi asara tafi na milliyan uku baki daya, harkan kasuwanci na Neman tabarbare min nakasa gabe meke damuna!? Se asara naketayi komai se lalace min yake."
Wani irin ka kasa gane abinda ke damunka bayan ga Abu afili,akuma kusa dakai"cewar Nadiya tana jifansa da wani shu'umin kallo"Kamar ya akusa dani My Queen ban fahimci mekike nufi ba yafada yana me kura mata idanu alamar yana son jin Karin bayani.Yanzu kuwa zan fahimtar daku,sede bansan yanda zaku amshi maganata ba. Daga shi har Hjy kultum ido suka zuba mata batare da sunce komai ba,sede da ka kalli fuskokinsu zakasan suna Bukatar Karin bayani....Murmushin samun nasara tayi kafin tace"...
_VOTE COMMENTS AND SHARE._✅
*_ESHAA CE~_*🤙🏻
[3/23, 15:13] ESHA: *KISHIYA KO BAIWA???.*
_(True life story)_
_Na Marubuciya_
*REAL ESHAA ~*
*WATTPAD*
_Realeshaa_
_Like my page on Facebook_👇🏻
https://www.facebook.com/REAL-ESHAA-FANS-114689303720405/
*_Ya Allah kajikan mahaifina ya Allah kagafar tamasa zunubansa ya Allah kakai haske kabarin sa ya Allah kajikan duk kan musulman dasuka rigamu gidan gaskiya ya Allah kasa innamu yazo mucika da imani._*
*PAGE 55&56*🖊️
_________________________📖 Uban me yakawo ki wajena!?Aida sekije kibisa tun yanzu ku kaini wajen hukumar kare hakkin mata bawai Sena sake yi miki komai ba,idan kukayi hakan se intabbatar dacewa kuncika yan halak kuma dagaske kukeyi"!yakarashe afusace dan har cikin ransa yake jin takaicin cin mutunci da mutumin ya masa hakika badan yaci darajan furfura ba daseya tsula masa rashin mutunci da harya mutu baze manta dashi ba...Banza tayi masa dan wani mugun haushi yake bata,batare da ta tanka masa ba ta jingina bayan ta da jikin motar jin kafafunta sungaji da tsayuwar.Akufulace yace"Ke dan Ubanki ni sa'anki ne da zanyi miki magana kina jina kiyi min banza ya fada yana zazzare mata daradaran idanunsa!?Idan motar dake wajen ya amsa to itama ta amsa.
"Wannan shirun datayi bakaramin kona mai zuciya yayi ba hakika yarinyar nan taga gadon baccina bacin haka yaushe ze mata magana tayi banza dashi,afusace yasanyo hannu acikin aljihun wandansa yaciro dari biyar ya wurgama tare dacewa kidauka kibiya kudin transport kiwuce gidan ku inyaso daganan sekiwuce kuje kukaini kara keda sabon Uban naki!.Yana gama fadin haka yashiga motarsa batare daya jira jin abinda zatace ba kana ya buleta da kuran motarsa yabar wajen...Murmushin takaici tayi a lokacin da motarsa ta bace mata koda amafarki bata taba zotan irin Wannan wulakan cin daga wajen Ahmad ba,Dasauri tasanya hannunta tashare hawayen dake kokarin zubo mata.Jiki amace tafara tafiya har tafita daga cikin haraban asibin yayinda zuciyar ta keta yimata sake-sake kan tawuce gidan su,yayinda wata zuciyar ke cewa takoma gidan sa.Cikin ikon Allah tana fitowa tasamu adedeta, taransa tayi tare dasanar masa dacewa bayan driving school ze kaita,kai dan acaban ya jinjina mata tare da fada maya yanda zata biyashi bamusu ta amince da bismillah tashiga shikuma yatayar suka tafi...
Ganin yana kokarin kisa yasa Nadiya saurin karasowa tarike hannunsa,Cike da tsoro tace"Honey sake mata wuya karka kasheta kaja mana bala'i!.kinsaketa yayi sema sake matse ta dayayi ajikin bango da duka karfinsa dan wani irin tsanarta yayi acikin rayuwar sa gwanda yakasheta kowa yahuta.Cikin tashin hankali Nadiya tabuga masa tsawa tare dacewa wai bazaka saketa bane seka kasheta!!??tafada tana janye hannunsa ganin ko motsi Sukainat tadena"Saketa yayi yana wani irin huci afusace yajuya yafice daga dakin.Zubewa Suky tayi sumammiya awajen"Cikin sauri Nadiya tabude Frigg tadauko ruwa me sanyi tasheka mata.Numfashi taja,kana tabude idanunta dasuka kada sukayi jawur dasu"Ganin ta farfado yasa Nadiya tajuya tafice...
Kuka Sukainat tafashe dashi Wanda muryanta befita,se hawaye dake ambaliya akan innocent face dinta.Dakyar ta Iya mikewa tashiga toilet ruwan zafi takunna tagasa jikinta da goshinta dake mata zafi,kafin tafito kan gado tafada"tayi rigingine, sotake bacci yadauketa kozata rage damuwar dake ranta anma Hakan yaki domin idanunta bushewa sukayi ba alamar bacci acikinsu.Rufin
P.O.P dake dakin tazuba wa idanu tana tunanin rayuwa,baki daya bata da sa'a acikin rayuwar ta. Ahmad yazame mata karfen kafa tun daga ranan data shigo cikin gidansa take cikin bakin ciki da takaici Wanda batasan ranan karewar saba
.Lumshe idanunta dake cike da hawaye tayi tana, tuna ranan data fara haduwa da Ahmad acikin rayuwar ta ranan da kaddararta tasauya izuwa kunci da bakin ciki,takuma dawo baiwa.Hawayene suka wanke mata fuska lokacin data tuna ahanyar ta nadawo daga islamiyya tahadu dasi.lokacin da aka tashe a islamiyya yamma yayi sosai kasancewar zasuyi musabaka hakan yasa suka dade,se da tafito taga hadari yahadu bakikkirin yana bada iska alamar daf ruwa yake da saukowa,gashi babu masu abin hawa hawa duk da kasamcewar tsakanin dutsen tanshi da federal Sacateria bawani nisa sosai.Hong dataji yayi yawa abayanta yasa tayi saurin matsawa gefe batare data juyaba domin sauri take ta Isa gida,sake danna mata hong akayi da karfi, hakan yasa tajuya akuma dede lokacin ne ruwan sama ya barke kamar da bakin kwarya.Zuge glass din motar yayi cike da nutsuwa yace"Barka da wannan lokacin kanwata,amsawa tayi da yauwa"tana kokarin barin wajen ganin yanda ruwa kedukanta,cikin kasa da murya yace"kishigo in rage miki hanya karmura yakamaki!,kai ta girgiza masa cikin yanayin sanyinta tace"ngd.sake sassauta murya yayi yace"pls kishigo mana inrage miki hanya"kin amincewa tayi.Duk Magiyan da yaitamata kantashiga yarage mata hanya anma fir taki. tayi tafiyar ta acikin ruwan yayinda shikuma yadinga bin bayanta ahanli har ta Isa Gida batare datasan yana biye da ita ba...
Sukainat kitashi kibamu abinci"Muryan Rufaida yakatse mata tunanin datake"Ahankali tabude kumburarrun idanunta takalle ta,Cikin muryan ta dabaya fita sosai tace"banyi girkiba.Dariyan shekiyanci Rufaida tasheke dashi kafin tace"Meyasa meki haka kofaduwa kikayi ko kuma kinyi fada ne amafarki da wacce tafi karfin ki!?hhhh gardiya tafadi akasa, tana gama fadin haka tafice daga dakin tana dariyar mugunta,dan dama ba yunwa takejiba Nadiya ce tasanya ta zuwa tambayi abinci...
Shiga parlour tayi tana dariyar mugunta hadda rike ciki,Hararanta Hjy kultum tayi tace ke lafiya kike irin wannan dariyar kamar wata zararriya.tsagaita dariyar tayi tace"Wlh grany bakiga fuskar Sukainat bane kamar wacce sukayi kokuwa da kada..Fashewa da dariya Nadiya tayi tace ke banson karya fa"Allah Momy bakarya nakeba dagaske nake..
Tsaki Hjy Kultum taja tace taje can takarata da mugun halinta matsalar tace duk bakin halinta kanta zekare ai,Ina aikar da aka miki tafada tana kallon Rufaida!?cewa tayi batai girki ba"anma bari nakira miku ita sekuga yanda fuskarta tayi, tana gama fadin haka tafice batare datajira jin amsar suba,tana shiga dakin babu sallama tace" Sukainat kawar kada kizo Hjy tazo kugaisa...Da kallo Sukainat tabi bayanta,tana mamakin sunan data kirata dashi wai kawar kada,kawar da tunanin tayi aranta kana tamike ahankali tadauki hijab dinta tafita daga dakin...
Kanta akasa tashiga parlour,bakinta dauke da sallama"Ko kallon ta basyi ba bare tasamu arzikin amsa salamarta.Bata damu da hakan ba domin inda sabo yaci ace tasaba da hallayar su.
Cike da ladabi ta tsugunna kusa da kujeran da Hajiya kultum ke kai tace"Sannu da zuwa Hjy fatan kinzo lafiya!?,Azabure Hjy kultum tamike tana watsa mata kallon tsana tace."Bana bukatar gaisuwarki mara tarbiya,se kizo kina wani sissinne kai kamar mutuniyar arziki!"maza fice kibani waje bana kaunar ganin wannan shedaniyar fuskar taki.Batace komai ba tamike tana kokarin hana kanta hawaye domin bataso suga raunin ta.Haba Sukainat kamata yayi kitsaya kibata hakuri dan Hjy kamar uwa take agareki,bekamata kinuna fushin ki kan tayi miki fada ba,anma yanda kika mike din nan yananu ni da kinfusata da fadar datai miki, takarashe tana satan kallon Hjy kultum dake jijjiga kafa cike da bala'i.
Murmushin takaici tayi,tarasa meta tsarewa Nadiya arayuwarta Wanda bata da burin daya wuce taga ta kuntatawa rayuwar ta."Cikin dashash'shiyar muryan ta da befita sosai tace"Wallahi ko daya banji takaicin kalaman Hjy ba dan yanda zan daraja Ummi na haka itama zan darajata amatsayinta na mahaifiyata...Cikin sauri Hjy kultum tadaga mata hannu tana huci tace"Allah yasauwa ke min in haifi mujiya kamar ke,me bakin jini da mugun hali,kije can kinemi uwarki anma ni bana fata in zama uwarki,dan da nahaifi irinki gwanda inda wama bani da 'da aduniya lalacacciya kawai...Cikin sauri Sukainat tafice daga dakin tana matsar kwalla,dan bazata Iya jure zama suna jifanta da munanan kalamai ba gara tafice tabasu waje.
Bayan fitarta Nadiya takalli Hjy kultum tana tabe baki tace"Hjy Wallahi yarinyar nan ta mugun renaki Sam bata ganin girmanki da kimarki sekace ke basurukar taba ce!,tafi karfin baki hakuri kenan akan lefin data miki gaskiya Hjy sekinyi gaggawar daukar mataki a kanta inba haka ba nan gabama se tayi abinda yafi wannan!?.Kwafa Hjy kultum tayi tace"bar matsiyaciyar yarinya ninasan maganinta dan sena dauki tsatstsauran mataki akanta...
Se bayan sallan la'asar Ahmad yashigo gidan agajiye.Lokacin dayashigo Hjy kultum nashirin tafiya ganin sa yasa takoma tazauna.Kusa da ita yazauna yagaishe ta"amsawa tayi da murmushi afuskarta tana tambayar sa kasuwa?"Dan yamutsa fuska yayi yace"Kasuwa babu dadi dan acikin wata daya nayi asara tafi na milliyan uku baki daya, harkan kasuwanci na Neman tabarbare min nakasa gabe meke damuna!? Se asara naketayi komai se lalace min yake."
Wani irin ka kasa gane abinda ke damunka bayan ga Abu afili,akuma kusa dakai"cewar Nadiya tana jifansa da wani shu'umin kallo"Kamar ya akusa dani My Queen ban fahimci mekike nufi ba yafada yana me kura mata idanu alamar yana son jin Karin bayani.Yanzu kuwa zan fahimtar daku,sede bansan yanda zaku amshi maganata ba. Daga shi har Hjy kultum ido suka zuba mata batare da sunce komai ba,sede da ka kalli fuskokinsu zakasan suna Bukatar Karin bayani....Murmushin samun nasara tayi kafin tace"...
_VOTE COMMENTS AND SHARE._✅
*_ESHAA CE~_*🤙🏻
[3/23, 15:13] ESHA: *KISHIYA KO BAIWA???.*
_(True life story)_
_Na Marubuciya_
*REAL ESHAA ~*
*WATTPAD*
_Realeshaa_
_Like my page on Facebook_👇🏻
https://www.facebook.com/REAL-ESHAA-FANS-114689303720405/
*_Ya Allah kajikan mahaifina ya Allah kagafar tamasa zunubansa ya Allah kakai haske kabarin sa ya Allah kajikan duk kan musulman dasuka rigamu gidan gaskiya ya Allah kasa innamu yazo mucika da imani._*
*PAGE 55&56*🖊️
_________________________📖 Uban me yakawo ki wajena!?Aida sekije kibisa tun yanzu ku kaini wajen hukumar kare hakkin mata bawai Sena sake yi miki komai ba,idan kukayi hakan se intabbatar dacewa kuncika yan halak kuma dagaske kukeyi"!yakarashe afusace dan har cikin ransa yake jin takaicin cin mutunci da mutumin ya masa hakika badan yaci darajan furfura ba daseya tsula masa rashin mutunci da harya mutu baze manta dashi ba...Banza tayi masa dan wani mugun haushi yake bata,batare da ta tanka masa ba ta jingina bayan ta da jikin motar jin kafafunta sungaji da tsayuwar.Akufulace yace"Ke dan Ubanki ni sa'anki ne da zanyi miki magana kina jina kiyi min banza ya fada yana zazzare mata daradaran idanunsa!?Idan motar dake wajen ya amsa to itama ta amsa.
"Wannan shirun datayi bakaramin kona mai zuciya yayi ba hakika yarinyar nan taga gadon baccina bacin haka yaushe ze mata magana tayi banza dashi,afusace yasanyo hannu acikin aljihun wandansa yaciro dari biyar ya wurgama tare dacewa kidauka kibiya kudin transport kiwuce gidan ku inyaso daganan sekiwuce kuje kukaini kara keda sabon Uban naki!.Yana gama fadin haka yashiga motarsa batare daya jira jin abinda zatace ba kana ya buleta da kuran motarsa yabar wajen...Murmushin takaici tayi a lokacin da motarsa ta bace mata koda amafarki bata taba zotan irin Wannan wulakan cin daga wajen Ahmad ba,Dasauri tasanya hannunta tashare hawayen dake kokarin zubo mata.Jiki amace tafara tafiya har tafita daga cikin haraban asibin yayinda zuciyar ta keta yimata sake-sake kan tawuce gidan su,yayinda wata zuciyar ke cewa takoma gidan sa.Cikin ikon Allah tana fitowa tasamu adedeta, taransa tayi tare dasanar masa dacewa bayan driving school ze kaita,kai dan acaban ya jinjina mata tare da fada maya yanda zata biyashi bamusu ta amince da bismillah tashiga shikuma yatayar suka tafi...