← Book details Duniya Biyu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 93 OF 104

Sashe 93

Duniya Biyu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ahankali tasauko tazo har gaban Waleed dake kuka sosai kuka bana wasaba tai kneeling har kasa tareda ijiye Arham little agefenta tahade hannayenta cikin kuka tace "Ammi, Dr wlh banda abinda zance, amman na rokeku da girman Allah dakuma darajan Allah kurufamin asiri, Waleed kawa Allah da Annabi kayakuri nasan na cutar dakai dayawa Waleed, please forgive me, Ammi" wani irin kallo Ammi tamata tace "to think I take you as my own daughter Ilham amman kikamin abinda kikayi hmmmm" Ammi ma takasa magana tace "ranan dana fara daura yaron nan a ido naji a jikina ba dan d'ana bane, amman nahana kaina yarda dakaina ina cema kaina tsanan danama Arham yasa yanzu nadena ganin abu ayanda yake, nace ma kaina akanme zan zargi yarinya mai tarbiya irinki, tattara komi nayi na watsar nacire zagin a raina sanan zargi nabata komi Ilham amman ashe inada gaskiya, Ilham danadai kika cuta ko"? Girgiza kai Ilham tayi da sauri tana wani irin kuka, Ammi tasake cewa. "dana dai kika cuta ko Ilham" sake girhixama Ammi kai tayi Ammi tai kwafa tace "tashi kidauki danku yanda ubanshi yabar gidan nan kema kifita kibishi kutafi duk inda zaku, d'ana zai aiko miki da takardan ki har gidan ubanki, keda d'ana har abada, ko mata sun kare Waleed yagama zama dake wlh, ki tashi kirufawa kanki asiri kibar gidan nan sadaf sadaf kafin nasa a fitar dake" ayanda Ammi tai maganan tasan da gaske take tasa ta tashi da sauri tai sama dogon hijabinta kadai ta daura kan towel din jikinta tana kuka sosai tafito ta kinkimi Arham tawuce tafita daga dakin Ammi tabita da kallo sanan ta rungume Waleed sosai ajikinta tana shafashi tace "ya isa Waleed karka jawa kanka ciwon zuciya shi rayuwa yagaji haka daman, ba kowa nakusa dakai bane ke sonka, banda haka da makiyi na kusa gwara na waje, dan makiyin ka nakusa yafi kaika kasa, Waleed inda ace yau nabari ka kashe Arham da still u will never be free, wanan bakin cikin yana tattare dakai kuma hukuma takamaka kaima akasheka bayan kayi shekaru agidan yari, Waleed shi rayuwa dakake gani kome yasame ka kaddara ce anrubuta daman hakan zai faru, sabida halin Arham kuma don't let it discourage you kace bazaka kara taimakon wani ba, aduk lokacin dakake da halin taimako kayi, sanan wanan gidan marayun koda daga baya an baka shi back kayaha kudi kabarshi, Dear Son akwai thousands of abubuwa dazakayi mahaifinka yasami ladan, zaka iya zuwa kauyuka ki gina boholes islamiyu masallatai agaruruwa daban daban yanki daban daban, eradicate almajiran ci, duk wani yaro da aka turo almajiran ci send him back sanan katura kauyen su ataimaka musu agina musu schools, abasu tallafi, settle down Waleed, forget anything Arham and build your life back, tun bayan ya kwace maka gidan marayu lamarinka suka lalace, karufe babin Arham duka arayuwan ka and open a new chapter, ka koma aikin asibitin ka Zenith kokuma ka gina naka asibitin and kadinga duba mutane free, shima charity work ne amman gidan marayu kagama yinshi son, kamanta da Ilham dakomi nata, gidan nan sell it kika kyautar dan banson anything dazai dinga tunamaka dasu, kadage da addu'a, ka gyara tsakanin ka da Allah kaga yanda Allah shima sai tsaya maka, forget everything kana zaune xkaga sakayyan da Allah zai maka cikin gaggawa, is okay babyna kaji" Ammi tamai kiss a kumatu tana sharemai hawayen, kankameta yayi sosai yadaura kanshi kan kirjinta tana shafa bayanshi ahaka yay bacci ajikinta tanajin yanda yake sauke ijiyan zuciyan kuka, mayar da kanshi kan kafarta yayi ta gyaramai kwanciya tana kallonshi itama tabude nabin nata sabon kukan, tai kuka tai kuka tagodema Allah, wanan Jarabta da danta kegani yay yawa tamai addu'a sosai sanan zata sake tsayawa akanshi tsayin daka kar Arham ya kashe mata da. Ahaka har gari yawaye tana zaune yanda taga dare haka taga r'ana kanshi tashafa ahankali, bude idanunshi yayi ya kalli Ammi idanun sun kumbura sosai, murya chan kasa tace "gari yawaye tashi kai alwala kazo kai salla" tashi yayi ahankali yay bayin falon ya shiga itakuma tadauki wayarta text ta turawa Mom akan tazo gidan Waleed this morning, sanan tama Uncle message tasanar dashi komi dake faruwa sanan ta ijiye wayan, sama taje tadauko dadduma tadawo falon ta shimfida nai, fitowa yayi daga bayin yahau kan dadduman itama tawuce bayin ta dauro alwala tafito agefenshi ta tsaya tai salla duk suka idar, tana zaune kan dadduman tana lazimi taji anbude gate Mom ce tashigo gidan da saurinta itada Abdul danshi yatukota sukayo falo tana shigowa idanun Waleed kadai takalla tagane balafiya sabida yanda suka kumbura da sauri Abdul yay kanshi yakai hannunshi kan wuyanshi yace "Ya Waleed bakada lafiya ne meke damunka"? Kafin ma Waleed yace wani abu sukaji ansake bude gate, tashi Mom tayi ta leka ta window tace "Family su Ilham ne wats happening wai" ahankali Ammi ta tashi ta tashi ta zauna kan kujera Mom takoma kan kujeran datake zaune ta zauna Waleed da Abdul kuma na zaune akan dadduman Mahaifin Ilham ya rangada Sallama, Abdul ne ya amsa yatashi yay wajen kofan tareda bude musu kofa suka shigo, Baban ta, sai Mummy su, sai babban yayansu Ibrahima, sai Ya Hassu da Husai dakuma Ilham din da hijabin jiyane ajikinta har kasa idanunta sun kumbura suntum akasa Mummy narike da Arham, anatse Abdul yace "ku shigo" shigowa sukayi aka nennemi waje aka zauna Mummy kuma tai wajen kawarta tace "Ammi meya farune wai jibi idanuwanki" murmushi kawai Ammi takakalo mata batace komiba, gyaran muryan da mahaifin Ilham yay yasa duk akai shiru, yace "Assalamu Alaykum, sanan barkanku kokuma nace barkanmu da safiya gabaki daya, nasan kuna mamakin ganinmuda sassafe hakako" yaydan shiru yace "ayanayin yanda Ilham tashigo gidanmu jiya da daddare kaman wacce aljanu suka buge tana kuka tana ihu hakama dan karamin yaro ta yasa muka shiga damuwa ainun, da tun dare mukaso muzo amman mukace dare yayi a bari da safe saimu kawota muzo muji meya faru dan wlh bata gayamana komiba sai kuka datake yi, yanzu kuma damuka kawota mukaga kuma duk kunanan hakan yakara tabbatar min cewa da abinda ke faruwa, dan Allah kucire my daga duhu Hajiya" murmushi kawai Ammi tasaki sanan tazubama Ilham wasu irin idanu takira sunanta. "Khadija" dagokai ahankali Ilham tayi ta kalli Ammi suka hada ido, babu alamun wasa akan idanunta tace "gayama iyayenki abinda yafaru da abinda kikayi" gyadama Ammi kai tayi ahankali bakinta nawani irin rawa tana shirin fashewa da kuka sanan ta kalli mahaifinta da babban yayansu tace "Baba ummm......jiya Waleed yadawo daga tafiya da daddare, sh......shi.....ne y......ya.....ya kamani da......da...." wani irin mahaukacin tsawa babban yayansu Ya Ibrahim yadaka mata yace "yakamaki dame!" wani irin firgita tayi tasake fashewa da kuka tana komawa baya tace "yakamani da.....da babban aminin shi Baba" tafashe da mugun kuka tashiga komawa baya tai wajen kafafun Mom tarike kafan Mom gam, wani irin mugun kallo mahaifinta yamata yace "mekike nufi da mijinki yakamaki da amininshi Khadijatul Iman"? Baba yamata tambayan babuko digin wasa akan idanunshi, wani irin kuka take tana haki takara damke kafar Mom tace "Baba kuyakuri wlh naci amanar ku, Baba bansan meya shegeni ba, Arham mayaudari ne, maci amana, tun ina Amarya tun muna yankari nabiyemai muka fara tarayya da Arham, Baba kuyakuri ku gafartamin amma Arham little danshi ne bana Mijina ba, Mummy kin tuna ranan dana fita ina gida ina jego nace miki wajen Samira kawata zani, wlh Mummy ba wajenta najeba wajen Arham naje aranan kuma nadauki wanan sabon cikin dake jikina na wata biyu dayan kai, shine jiya Waleed yadawo yakamamu adakinshi akan saman gadonshi tsirara muna saduwa, Baba dan Allah kuyakuri kuyafemin karku tsanani dan girman Allah" tafashe da kuka, duka family ta kallonta suke babu wanda ya iya kwakkwaran motsi cikinsu jin abinda yarsu tafadi da bakinta inda ace wani yafadi zasu iya cewa shairi aka mata amman dagabakinta yake fitowa, Baban Yayansu ne yakasa daurewa sabida Allah yamai bakar zuciya yatashi ya shiga kalle kalle adakin, wayar gaban TV falon yaje baimasan wayan miyeba ya fizgo azuciye yayo kanta kankame kafar Mom tayi tana kuka sosai. "Mom zai kasheni wlh karki bari yadakan karki bari yadakan" fizga daya yamata ya fincikota yashiga zuba mata wayan wutarnan tako ina yasamu ajikinta yana hadamata da hannu gabaki dayan dakin babu wanda yay yunkurin hanashi sai ihunta dayacika ko'ina yana dukanta yace "I can't imagine what bawan Allah nan went through" yanuna Waleed da kanshi ke kasa, yace "I try to put myself in his shoes nakama matata da wani akan gadona agidana tsirara na rantse da Allah bazan bartada raiba, amman bawan Allah nan ko marinki baiyiba Ilham, tarbiyan da Baba da Mummy suka baki kenan, Ilham ki haifi shege sanan kina dauke da wani cikin shegen ajikinki yanzu haka, Innalillahi wa innailaihi raji'un, Ilham wlh kanki kika cuta bamuba" yacigaba da dukanta ganin yana neman kasheta numfashinta har neman daukewa yake yasa Ammi ta yunkura zata tashi riketa Mummy tayi tace "bazakije ba" fizge hannunta tayi ta tashi hannun Ibrahim takama da sauri tace "karka mata rauni Ibrahima ba ita kadai bane" cikin kumfan zuciya Ibrahim yace "Mummy kinsandai kin isa dani ko, tun ina yaro nasanki tareda Mummy mu, yanda na dauki uwata haka na daukeki Mummy ki kyaleni gwala na illatata, ta mutu daga ita har abin cikin nata, Mummy kinji abinda tamuku kuwa, Mummy ta cutar da ke da danki, Ilham taci amanar amintar da kawance da yardan dake tsakanin ki da mahaifiyar mu, Ilham taruguza komi da kukai building tun kafin ahaifo mu" girgixa kai Ammi tayi tace "bata bata komiba, nida mahaifiyar ku will always be aminan juna har duniya tanade, bani wayar wutan nan kaga" karban wayan tayi sanan tajashi tamaidashi kujeran dayake zaune kusada Baba, itakuma Ilham tazube ajikin bango bakinta na jini sosai goshinta ya kumbura fuskarta yay rudu rudu.
Chapter 93 · 0% Book details