Sashe 11
Dabaibayi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bin ta munu tayi suka tafi a hankali suka karkata suka shige gidan sad’af sad’af yacce baza a ji takunsu ba falon farko suka shiga ba kowa nan suka lelleqa ko ina ba alamun mutum d’akin amir suka fad’a jin kamar takun mutum, can suka jiyo wata murya na waya
“It’s cleared ma!”
Daga cikin wayar suka jiyo ance “I am very sure zasu dawo ko ba dad’e ko ba jima just don’t forget to keep an eye”
“Yes ma! Amma ya batun samira fa?”
Dariya aka kyakyace da ita “wannan ka barta har zuwa lokacin da zata mallaki hankalinta shine take me amfani, yanzu ita da hoto basu da maraba”
Firgici me sunan firgici ya kama Sam da munu suka ruqunqume juna har basu sani ba suka bigi wani flower vase ya fad’i qasa ai a guje suka maqale jikin bango se dai jinginar su ke da wuya bango ya juya dasu se gasu cikin wani tamfatsetsen closet wanda yasa lokaci d’aya Sam ta kurma wani uban ihu me tada hankali
Munu dake a firgice tayi saurin d’ora hannunta a bakin Sam “shii shii...k...iy..I shi..ru kar ..a ji mu Sam”
Ta fashe da kuka qasa qasa, hannun da Sam ke pointing tabi da ido bata san lokacin da ta fad’a baya ba har ta bige da bango,
“Shish..shine...”
Yawu munu ta had’iye da qyar idanunta kafe kan fuskar zakin dake kallo su, numfashi ta shiga saukewa a hankali ta taka a hankula zuwa wurin fuskar ta yaye saurin ja baya tayi ganin hoton ya habiibii,
Saurin kallon juna sukayi cike da mamaki Sam cikin raunanniyar murya tace “dama shi..ne “ munu ta matsa kusa da ita tare da jan hannunta suka nufi wata qofa a hankali suka murd’a key d’in jiki se gasu a waje,wajen ma dai dai layin gidan gwaggo fita sukayi da sauri ba kowa se tsirarun mutane juyawa sukayi suna kallon qofar data rufe bazaka ta’ba cewa akwai wata qofa a wurin ba a kid’ime suka shiga zabga sauri zasu shiga gida kenan su mu’allim bello suka iso.
A tsakar gida suka tarar da gwaggo suka fad’a mata suna kuka, duk suka rikita ta, menene? Me ya faru? Me ya same ku? Amma shiru ba wanda ya kulata, sallamar su Anwar ce ta sa su sassautawa
“Yawwa ai gara da kuka zo, kun gansu sun tisa ni gaba se tambayar su nake ba wanda ya kulani, dan Allah kuntayani tambayar su, oh ni haulatu”
Mu’allim bello yace “Sam, munu what’s wrong? Meke damunku?” Nan ma shiru ba amsa carpet d’in dake ajiye a gefe ya shimfid’a yana me kallon Anwar.
Anwar da duk suka qular dashi jin yanda ake faman tambayar su basu amsa ba ya ce “Idan baku had’iye kukan nan ba, ni da ku ne” cikin kakausar murya,
‘Dif kake ji wai malam yaci shirwa, ashe wargi ma wuri ya samo “ku samu wuri” sum sum sum suka zauna kusa da gwaggo yaci gaba before the count of 3 ku fad’i abinda ke damun ku.
Tar tar tar suka zayyano abinda ya faru hawaye na biyo baya tun bare Sam, hankali tashe gwaggo ta rinqa salati tana sallallami fad’i take “shikenan zaman mu a garin nan ya qare oh ni Allah ka bani ikon cin jarabawar nan taka, yanzu ace habibii ne dama ke qoqarin lalata miki rayuwa, kai duniya ina zaki damu” ta fashe da wani marayan kuka ta rungumo su jikinta
“Ba kuka zaki yi ba gwaggo”
“Me kake so nayi, bani da kowa bani da komai d’an uwana ya gujeni wannan yaran kawai nake gani naji dad’i to suma ana neman fara farautar su ina zanso kaina ni haulatu”
Qwallar data ciko idanunsa ya share “gwaggo ku tashi mu tafi”
Bello yayi saurin kallonsa, “ina?”
Gidan mu “zaman su a nan ya qare”
Ta girgiza kai “um um d’an nan wahalar se tayi yawa, ka bari zuwa gobe se mu koma can garin mu, inda muka fi wayo”
“Gwaggo dan darajar Allah ki tashi mu tafi in yaso Mayi deciding step to take next”
Kallonshi tayi ido a kod’e “kuj’e d’aki ku d’auko mana hijabai”
Qulle gidan su kayi, suka d’unguma zuwa kwairanga road.
©️Kdeey😊
DABAIBAYI👄
©️Khadija Ahmad (Kdeey😊)
WATTPAD @Deejaht ahmad
®️Haske writers association 💡
(Home of expert and perfect writers)
(17)
Tun daga nesa ya hango motar rannan a qofar gida, daga can baya ya tsayar da motar had’e da sauke wani gauron numfashi , “ya dai?” Bello ya tambaye shi, “ku sauka ku bi ta gate d’in baya” bello ya maida idonsa inda yaga Anwar d’in na kallo, wata baqar mota ya gani a qofar gidan wani mutumi jingine jikinta bayansa a juye, jikinsa ne ya bashi cewa ba lafiya ba, “su waye wad’ancan?” Ya furta a hankali, “abinda nake son sani kenan, har yanzu ba wani feedback daga wurin bashari ne ?”, “a a nasan da ya kira” girgiza kai Anwar yayi ya kalli su Sam ta cikin mirror had’e da sauke ajiyar zuciya a hankali yace “shiga dasu, zan bi bayan motar can” d’aga kai bello yayi ya juya baya “gwaggo bismillah muje mun iso ”
Hanci taja, ta kama hannuwansu suka bi bayansa, tsawon mintuna sha biyar sannan mutumin ya matsa ya shige gida, motar taja.
Ta wata kwana ya bi ya cimma motar a hankali yake binsu har zuwa commissioner road cikin wani tafkeken gida aka shiga, waige waige yayi unguwar shiru ba’a ji komai se kukan tsuntsaye, daga can baya kad’an ya hango wani me trader zaune yana quqqulla leda, parking yayi ya sauka zuwa wurin mutumin,
Sallama yayi had’e da fad’in “Washh Allah baya na, na gaji” buzun dattijo ya d’ago da kanshi da hausa shi da bata fita dakyau yace “sannu bawan Allah”
“Yawwa baba, dan Allah taimaka min da ruwa mana tun safiyar yau bansa komai a ciki na ba”
“Kash se de fa kayi sa’a duk masu zafi ne “ ya miqa masa sachet d’in pure water
Dariya Anwar yayi “nagode, amma baba daman talaka na samun abu me sanyi ne, rabo na da ganin ko qanqara na manta”
Kallon sama da qasa mutumin ya mishi, “kai kuwa daga ina kake haka dan shigar ka da kamanninka sun nuna kai d’in babban mutum ne”
Baki ya bud’e har da riqe ha’ba “wa d’in ni, tab lallai kace oga yayi aiki”
“Kamar yaya ban fahimce ka ba”
Gyara zama yayi, “ni sunana lawali nazo ne daga qaramar hukumar ajingi”
“To to ko kai ne sabon direban hajiya”
Jimm yayi zuwa can yace”..eh nine”
Kallon da tsohon ya masa yasa shi shan ruwan jikinsa, “...amma..”
“Uhm...riqe maganar ka inde gidannan ne wata biyu na baka zaka gudu kaima da qafarka”
Ido ya waro waje “ko zan san meyasa kace haka?”
“..kaje ka gani..” ya miqe tsaye bari na kewaya
Binsa yayi da ido yana juya maganar, tashi yayi da zummar barin wurin ya hango wani ya leqo daga cikin gidan da motar nan ta shiga , bayan wata bishiyar darbejiya ya la’be, bisa mamaki sa se ganin wannan tsohon yayi ya fito shima yana waige waige har yana d’aga wa mutumin hannu
Cikin d’aga murya mutumin yace “ina yake?”
Dattijon dake leqe leqen neman Anwar yace “yanzu na barshi anan fa, wataqila gudu yayi”
Cikin d’aga murya mutumin yace “dalla ware, ni dama nasan duk qarya ka shirya son shigowa kake, To hajiya tace ka cire wannan tsimman ka shigo ciki”
Cikin d’aga murya dattijon yace “Kai dalla malam kasan yacce zaka rinqa min magana, ni ba sa’an ka bane” ya ja tsaki, hannu yasa ya cisge farin gashin bakin sa da na jikin gashin girar sa,
“Ahhh yau tun a nan zaka tu’be, lallai kana had’uwar ka da hajiya ba zata yi kyau ba” saurayin da ada yake dattijo ya ja tsaki
ya miqe tsaye tangar tamkar ba tsohon nan ba dake dunqufe se da ya kuma wawwaigawa gefe da gefe sannan yayi wuf ya fad’a gidan suka rufe.
“Innalillahi wa inna’ilaihir raji’un” ya furta out of his breath, su wane wad’annan mutanen?, kuma wacece wannan hajiyar? Sad’ad’awa yayi ya fad’a mota ya tafi jiki a mace
***
“Gwaggo ba wai uncle ze raba ki da su bane, kina ganin dai abinda ke faruwa boarding school d’in ita tafi dacewa da su”
“Amma..”
“Kar ki damu hajiya yaran nan tamkar yaran cikina suke, saboda gudun haka yasa na yanke hukuncin tura su can UK inda Iyalina suke tare da Anwar dan qarasa karatun su, Allah barshi ke kuma se ki zauna a nan tare da bello da kuma ni har Allah yasa mu warware wannan dabaibayin se mu koma can baki d’aya”
Baki bud’e tace “barrister kaine?...”
Ya murmusa “Ni ne gwaggo, na dawo da qarfina dan nemawa Samira haqqinta da ake qoqarin qwace mata”
Gwaggo ta fashe da kuka “barrister ina cikin wani hali, a yanzu yaran nan sune kad’ai nake gani naji sanyi, idan sukayi nisa da ni ya...”
“Gwaggo nima d’anki ne, Insha’Allah bazaki ta’ba maraicin rashin su ba” cewar bello
Murmushi uncle yayi yace “nayi miki alqawari duk hutu zasu rinqa zuwar miki”
Numfashi ta sauke “shikenan na amince nasan ba zaka ta’ba cutar damu ba, you are my last hope”
Jinjina kai yayi, ta share hawayen fuskarta “Amma meye had’inka da su bello”
Kafad’ar bello ya rungumo “ya’yan wa nane marigayi”
“Allah sarki ‘yan albarka, Allah ya jiqan mahaifan ku”
“Amen gwaggo”
“kukan ya isa haka” suka jiyo muryar shi daga bakin qofa
Kallon shi sukayi duka, gyara tsayuwarsa yayi tare da takowa jiki a mace ya zube saman kujera idonsa saman nasu Sam, “ku tashi ku bamu wuri, ya nuna musu qofar d’aki
Bayan sun shige ya gyara zama had’e da tallafo fukarsa da hannayenshi,
“Anwar lafiya” cewar uncle, girgiza kai yayi tare da miqewa ya rurrufe qofa da windows, suna binshi da ido kafin ya zauna ya zayyane musu duk abinda yafaru tun ganinsa na farko da motar,
Cikin qunar rai uncle yace “yanzu kana nufin cikin yaran gidannan akwai wanda ke bada information a kanmu”
“Yeah, akwai yaron su cikin mu”
Bello ya kalli uncle “I think gara bro A ya tafi da yaran nan abuja gobe idan yaso suyi passport da visa kawai su wuce daga can”
“It’s cleared ma!”
Daga cikin wayar suka jiyo ance “I am very sure zasu dawo ko ba dad’e ko ba jima just don’t forget to keep an eye”
“Yes ma! Amma ya batun samira fa?”
Dariya aka kyakyace da ita “wannan ka barta har zuwa lokacin da zata mallaki hankalinta shine take me amfani, yanzu ita da hoto basu da maraba”
Firgici me sunan firgici ya kama Sam da munu suka ruqunqume juna har basu sani ba suka bigi wani flower vase ya fad’i qasa ai a guje suka maqale jikin bango se dai jinginar su ke da wuya bango ya juya dasu se gasu cikin wani tamfatsetsen closet wanda yasa lokaci d’aya Sam ta kurma wani uban ihu me tada hankali
Munu dake a firgice tayi saurin d’ora hannunta a bakin Sam “shii shii...k...iy..I shi..ru kar ..a ji mu Sam”
Ta fashe da kuka qasa qasa, hannun da Sam ke pointing tabi da ido bata san lokacin da ta fad’a baya ba har ta bige da bango,
“Shish..shine...”
Yawu munu ta had’iye da qyar idanunta kafe kan fuskar zakin dake kallo su, numfashi ta shiga saukewa a hankali ta taka a hankula zuwa wurin fuskar ta yaye saurin ja baya tayi ganin hoton ya habiibii,
Saurin kallon juna sukayi cike da mamaki Sam cikin raunanniyar murya tace “dama shi..ne “ munu ta matsa kusa da ita tare da jan hannunta suka nufi wata qofa a hankali suka murd’a key d’in jiki se gasu a waje,wajen ma dai dai layin gidan gwaggo fita sukayi da sauri ba kowa se tsirarun mutane juyawa sukayi suna kallon qofar data rufe bazaka ta’ba cewa akwai wata qofa a wurin ba a kid’ime suka shiga zabga sauri zasu shiga gida kenan su mu’allim bello suka iso.
A tsakar gida suka tarar da gwaggo suka fad’a mata suna kuka, duk suka rikita ta, menene? Me ya faru? Me ya same ku? Amma shiru ba wanda ya kulata, sallamar su Anwar ce ta sa su sassautawa
“Yawwa ai gara da kuka zo, kun gansu sun tisa ni gaba se tambayar su nake ba wanda ya kulani, dan Allah kuntayani tambayar su, oh ni haulatu”
Mu’allim bello yace “Sam, munu what’s wrong? Meke damunku?” Nan ma shiru ba amsa carpet d’in dake ajiye a gefe ya shimfid’a yana me kallon Anwar.
Anwar da duk suka qular dashi jin yanda ake faman tambayar su basu amsa ba ya ce “Idan baku had’iye kukan nan ba, ni da ku ne” cikin kakausar murya,
‘Dif kake ji wai malam yaci shirwa, ashe wargi ma wuri ya samo “ku samu wuri” sum sum sum suka zauna kusa da gwaggo yaci gaba before the count of 3 ku fad’i abinda ke damun ku.
Tar tar tar suka zayyano abinda ya faru hawaye na biyo baya tun bare Sam, hankali tashe gwaggo ta rinqa salati tana sallallami fad’i take “shikenan zaman mu a garin nan ya qare oh ni Allah ka bani ikon cin jarabawar nan taka, yanzu ace habibii ne dama ke qoqarin lalata miki rayuwa, kai duniya ina zaki damu” ta fashe da wani marayan kuka ta rungumo su jikinta
“Ba kuka zaki yi ba gwaggo”
“Me kake so nayi, bani da kowa bani da komai d’an uwana ya gujeni wannan yaran kawai nake gani naji dad’i to suma ana neman fara farautar su ina zanso kaina ni haulatu”
Qwallar data ciko idanunsa ya share “gwaggo ku tashi mu tafi”
Bello yayi saurin kallonsa, “ina?”
Gidan mu “zaman su a nan ya qare”
Ta girgiza kai “um um d’an nan wahalar se tayi yawa, ka bari zuwa gobe se mu koma can garin mu, inda muka fi wayo”
“Gwaggo dan darajar Allah ki tashi mu tafi in yaso Mayi deciding step to take next”
Kallonshi tayi ido a kod’e “kuj’e d’aki ku d’auko mana hijabai”
Qulle gidan su kayi, suka d’unguma zuwa kwairanga road.
©️Kdeey😊
DABAIBAYI👄
©️Khadija Ahmad (Kdeey😊)
WATTPAD @Deejaht ahmad
®️Haske writers association 💡
(Home of expert and perfect writers)
(17)
Tun daga nesa ya hango motar rannan a qofar gida, daga can baya ya tsayar da motar had’e da sauke wani gauron numfashi , “ya dai?” Bello ya tambaye shi, “ku sauka ku bi ta gate d’in baya” bello ya maida idonsa inda yaga Anwar d’in na kallo, wata baqar mota ya gani a qofar gidan wani mutumi jingine jikinta bayansa a juye, jikinsa ne ya bashi cewa ba lafiya ba, “su waye wad’ancan?” Ya furta a hankali, “abinda nake son sani kenan, har yanzu ba wani feedback daga wurin bashari ne ?”, “a a nasan da ya kira” girgiza kai Anwar yayi ya kalli su Sam ta cikin mirror had’e da sauke ajiyar zuciya a hankali yace “shiga dasu, zan bi bayan motar can” d’aga kai bello yayi ya juya baya “gwaggo bismillah muje mun iso ”
Hanci taja, ta kama hannuwansu suka bi bayansa, tsawon mintuna sha biyar sannan mutumin ya matsa ya shige gida, motar taja.
Ta wata kwana ya bi ya cimma motar a hankali yake binsu har zuwa commissioner road cikin wani tafkeken gida aka shiga, waige waige yayi unguwar shiru ba’a ji komai se kukan tsuntsaye, daga can baya kad’an ya hango wani me trader zaune yana quqqulla leda, parking yayi ya sauka zuwa wurin mutumin,
Sallama yayi had’e da fad’in “Washh Allah baya na, na gaji” buzun dattijo ya d’ago da kanshi da hausa shi da bata fita dakyau yace “sannu bawan Allah”
“Yawwa baba, dan Allah taimaka min da ruwa mana tun safiyar yau bansa komai a ciki na ba”
“Kash se de fa kayi sa’a duk masu zafi ne “ ya miqa masa sachet d’in pure water
Dariya Anwar yayi “nagode, amma baba daman talaka na samun abu me sanyi ne, rabo na da ganin ko qanqara na manta”
Kallon sama da qasa mutumin ya mishi, “kai kuwa daga ina kake haka dan shigar ka da kamanninka sun nuna kai d’in babban mutum ne”
Baki ya bud’e har da riqe ha’ba “wa d’in ni, tab lallai kace oga yayi aiki”
“Kamar yaya ban fahimce ka ba”
Gyara zama yayi, “ni sunana lawali nazo ne daga qaramar hukumar ajingi”
“To to ko kai ne sabon direban hajiya”
Jimm yayi zuwa can yace”..eh nine”
Kallon da tsohon ya masa yasa shi shan ruwan jikinsa, “...amma..”
“Uhm...riqe maganar ka inde gidannan ne wata biyu na baka zaka gudu kaima da qafarka”
Ido ya waro waje “ko zan san meyasa kace haka?”
“..kaje ka gani..” ya miqe tsaye bari na kewaya
Binsa yayi da ido yana juya maganar, tashi yayi da zummar barin wurin ya hango wani ya leqo daga cikin gidan da motar nan ta shiga , bayan wata bishiyar darbejiya ya la’be, bisa mamaki sa se ganin wannan tsohon yayi ya fito shima yana waige waige har yana d’aga wa mutumin hannu
Cikin d’aga murya mutumin yace “ina yake?”
Dattijon dake leqe leqen neman Anwar yace “yanzu na barshi anan fa, wataqila gudu yayi”
Cikin d’aga murya mutumin yace “dalla ware, ni dama nasan duk qarya ka shirya son shigowa kake, To hajiya tace ka cire wannan tsimman ka shigo ciki”
Cikin d’aga murya dattijon yace “Kai dalla malam kasan yacce zaka rinqa min magana, ni ba sa’an ka bane” ya ja tsaki, hannu yasa ya cisge farin gashin bakin sa da na jikin gashin girar sa,
“Ahhh yau tun a nan zaka tu’be, lallai kana had’uwar ka da hajiya ba zata yi kyau ba” saurayin da ada yake dattijo ya ja tsaki
ya miqe tsaye tangar tamkar ba tsohon nan ba dake dunqufe se da ya kuma wawwaigawa gefe da gefe sannan yayi wuf ya fad’a gidan suka rufe.
“Innalillahi wa inna’ilaihir raji’un” ya furta out of his breath, su wane wad’annan mutanen?, kuma wacece wannan hajiyar? Sad’ad’awa yayi ya fad’a mota ya tafi jiki a mace
***
“Gwaggo ba wai uncle ze raba ki da su bane, kina ganin dai abinda ke faruwa boarding school d’in ita tafi dacewa da su”
“Amma..”
“Kar ki damu hajiya yaran nan tamkar yaran cikina suke, saboda gudun haka yasa na yanke hukuncin tura su can UK inda Iyalina suke tare da Anwar dan qarasa karatun su, Allah barshi ke kuma se ki zauna a nan tare da bello da kuma ni har Allah yasa mu warware wannan dabaibayin se mu koma can baki d’aya”
Baki bud’e tace “barrister kaine?...”
Ya murmusa “Ni ne gwaggo, na dawo da qarfina dan nemawa Samira haqqinta da ake qoqarin qwace mata”
Gwaggo ta fashe da kuka “barrister ina cikin wani hali, a yanzu yaran nan sune kad’ai nake gani naji sanyi, idan sukayi nisa da ni ya...”
“Gwaggo nima d’anki ne, Insha’Allah bazaki ta’ba maraicin rashin su ba” cewar bello
Murmushi uncle yayi yace “nayi miki alqawari duk hutu zasu rinqa zuwar miki”
Numfashi ta sauke “shikenan na amince nasan ba zaka ta’ba cutar damu ba, you are my last hope”
Jinjina kai yayi, ta share hawayen fuskarta “Amma meye had’inka da su bello”
Kafad’ar bello ya rungumo “ya’yan wa nane marigayi”
“Allah sarki ‘yan albarka, Allah ya jiqan mahaifan ku”
“Amen gwaggo”
“kukan ya isa haka” suka jiyo muryar shi daga bakin qofa
Kallon shi sukayi duka, gyara tsayuwarsa yayi tare da takowa jiki a mace ya zube saman kujera idonsa saman nasu Sam, “ku tashi ku bamu wuri, ya nuna musu qofar d’aki
Bayan sun shige ya gyara zama had’e da tallafo fukarsa da hannayenshi,
“Anwar lafiya” cewar uncle, girgiza kai yayi tare da miqewa ya rurrufe qofa da windows, suna binshi da ido kafin ya zauna ya zayyane musu duk abinda yafaru tun ganinsa na farko da motar,
Cikin qunar rai uncle yace “yanzu kana nufin cikin yaran gidannan akwai wanda ke bada information a kanmu”
“Yeah, akwai yaron su cikin mu”
Bello ya kalli uncle “I think gara bro A ya tafi da yaran nan abuja gobe idan yaso suyi passport da visa kawai su wuce daga can”