Sashe 28
Buzu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To ka gani, shi ba ubanta ba ba ɗan uwanta na jini ba, ba ma kwa tsoron ya lalata rayuwar yarinyar. Ga ku a cikin ƙwaryar birni kamar masu hankali, amma kun yi abu kamar mutanen farko. Duk yadda ake ciki wajibi ne gobe ka wuce gaba, zan bayar da mutum biyu a nan, aje a dawo da yarinyar nan, muddin ba ku dawo da ita ba, to wani abun ku ka aikata kuma sai na rufe ku daga kai har wanda ku ka kai ta" Gaddafi ya jinjina kai tare da yi wa Imran wani mugun kallo.
*****
Nana a É—akin da sarkin baka yake bayar da magani ta tarar da shi, yana ganin wata mata da yaronta.
Ƙafafuwan yaron tamkar lagwani 'yan sirara marasa ƙwari, da hannayensa. Haka kansa ma ɗan mitsitsi da kaɗan ya fi lemon zaƙi fuskarsa tamkar tsoho abin tsoro yaron.
Uwar kuma sai rungume shi take yi cike da so da ƙauna.
Sarkin baka ya ce "Wata rana kin kashe gizo gizo cikin dare, a banɗakin ki, lokacin ki na da ƙaramin cikin yaron nan, ba tare da kin yi bismillah ko addu'a shiga banɗaki ba, an yi haka?"
Ta girgiza kai ta ce "Sarki ba zan iya tunawa ba"
"To an yi, shi ya faÉ—i abin da ki ka yi masa, kin bugawa jaririnsu takalmi, kin nakasa shi, shi suka ajiye a jikin gizo-gizo yana wasa, ki ka dake shi da takalmi, da kin yi addu'a da ya bar jikin gizo-gizon. Dan haka yanzu É—an su suka ajiye a jikin yaron naki, jininsa da sauran sinadaran jikin yaron ki, da za su saka ya girma, su yake sha yana girma, dan haka ko an cire aljanin mutuwa zai yi ba shi da sauran mamora sun gama lalata jikin yaron da garkuwar jikinsa" matar ta fashe da kuka ta ce "Dan Allah sarki ka taimake ni"
Ya girgiza kai ya ce "Magani kawai nake bayarwa, ba ni da ikon kashewa ko rayawa, zan baki magani ki koma gida, Allah ya baki wani"
Nana ta ce "Ya a ka yi ka san aljanin ne a jikinsa, kuma idan ya fita ba zai rayu ba?"
Buɗe ƙwaryar can, ki ɗaukko mini habbatussauda, akwai tazargade a ciki da tsakin kuka, da garin farin muski, duk ɗebo su da kan ki ki zo" babu musu Nana ta harhaɗo kayan da ya ce ta kawo masa.
Ya zira hannu a jakarsa ya ɗaukko garwashi, ya ɗora a kan wata tasa, ya ɗebi haɗin nan ya zuba a kai. Ko sakan goma ba a yi ba, yaron ya mimmiƙe ya din ga tsala uban ihu.
Sarkin baka ya cewa matar "Yaushe rabonsa da kuka, ko ya motsa wata gaɓa ta jikin sa?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya tunawa ba, kullum a kwance kawai yake"
"To tun da ya yi kuka yanzu har da mimmiƙe wa, kin san ba ƙalau ba, baiwar Allah ki je gida, Allah ya baki wani"
Nana a ranta ta ce "Yaro ya ji wannan uban hayaƙin ba dole ya tsala ihun azaba ba".
Ya ce "Kamar har yanzu ba ki yarda da abin da ki ka gani ba ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a na yarda"
" 'yar wace ɗariƙa ce ke ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Ɗariƙa ba ta cikin sharaɗin addini, dan haka ni ba ni da wata ɗariƙa"
Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, kin san kowace ɗariƙa akwai malamin da ta ke yarda da shi, da ki na da ɗariƙa da na ce ki saurari bayanin da wani babban malami ya yi a kan aljanu, amma manta kawai kin tashi lafiya?"
"Lafiya kalau Alhamdilillah" ta buÉ—e baki za ta sake magana ta ga bakin sarkin baka duk jini da sauran gashin zakaran da ya cinye jiya, wanda lokacin da ta shigo ba bu shi a bakinsa.
Zabura ta yi ta ja da ba, dan a zaton ta a mafarki ta ga ya ci zakaran ba a gaske ba, kuma da har ma ta manta ma.
Sarkin baka ya sanya hannu, ya zaro sauran gashin daga bakinsa, ya kalla ya yi murmushi ya ce "Kar ki tsorata Nana, tun a zuwan ki gidan nan da na so cutar da ke, sai na cutar da ke ta in da uban duƙusa ba zai iya ba ki kariya ba.
Har ga Allah bani da niyyar cutar da ke, kuma da gaske na san ba zan iya raba ki da shi ba, amma na rage masa tasiri ta wasu fuskokin daban-daban a tattare da ke.
Tabbas na cinye zakara da ransa, kuma uban duƙusa ne ya zungure ni, sai da na yi a gaban ki, dan ki cire yarda da ni kar ki yarda ki sadaukar mini da shi. Da na mallake shi zan ƙara ƙarfi da ƙarin tasirantuwar magunguna na, kuma zan kerewa sa'a tsakanin mutanenmu.
Ainihina ɗan wanzamai ne, na gaji wanzanci daga nan aka kai ni bara, na samu karatun Alqur'ani daidai gwargwado sai dai babu sauran litattafai na addini. Azabar yunwa ce ta sanya na fara bin matasa daji farauta, daga baya na watsar da allo na bar gurin malamin da aka kai ni gaba ɗaya, duk mahaifiyata 'yar maharba ce, amma na fi ƙarfi ga ɓangaren wanzanci.
Na yi rashin ji, na yi faɗi tashi, na yi wa harkar baka haye, har na so na fi 'yan gado ƙwarewa, hakan ya saka sauran maharba sako ni a gaba, da tsaface-tsaface da ƙoƙarin son kawar da ni. Sun sha haɗa kai domin su kashe ni.
Suka yi mini shiri, na zo ba na iya kama komai idan na fita harbi, ga rashin lafiya, dole na bazama neman magani a nan na haɗu da uban gidana, a masu magani ya bani maita, wadda ita ma wasu baƙaƙen aljanu ne suke tasrifinta, ya ƙara koya mini harkar magani, ga wanda na gada na wanzanci a gida. Ya yi mini girkar aljanu na zo na gawurta, na nemi na fi shi ma ko ma na ce miki na fishi ta kaowace fuska, kawai sai ya fara neman ya kashe ni, saboda hassada. Wataran mun fita farauta tare ya rikiɗe ya koma ƙaton maciji ya yi ƙoƙarin haɗiye ni, ni kuma garin ƙwatar kaina na kashe shi har lahira.
A haƙiƙanin gaskiya, ba na yadda na bawa mutum duk wani abu da zai cuci mutane a kan zalunci. Ina da tarin aljanu kala-kala da nake aiki da su. Na nemi ki sadaukar mini da uban duƙusa ne domin na ƙara ƙarfin tasirina. Rabona da maita har na manta, tana nan a jikina amma bana amfani da ita, na daina ta'amalli da aljanun maita, shi ne jiya ya zunguri maitar ta motsa mini. Yanzu haka sai na je na yi jinya, kuma zan ja dogon lokaci ban yi aiki ba, sai dai yarana su yi. Hatta Salamatu da ki ke gani ba mutum ba ce ba. Ainihin matar ba ta da lafiya sihiri aka yi mata, ba ta iya komai aka kawota nan. Na saka Salamatu a jikinta take yi mini aiki, Salamatu na fita gangar jikin za ta faɗi ta ci gaba da jinya. Shirin a jikin gawa aka yi mata, aka binne gawar ni kuma ba zan iya sakawa a ciro gawa daga makwanci domin karya sihirin ba, hakan tamkar tozarta gawar ne."
Jikin Nana duk ya yi sanyi da jin labarin da sarkin baka ya bata.
"Yarinyata da tana raye da ta kai kamar ke, na tafi farauta abokan adawa ta, su ka kasheta da babarta, tun daga nan ban kuma aure ba,, shiyasa na yi iya ƙoƙarin da zan yi na gagare su. Zan saka a mayar da ke gida, ba sai kin yi makonni biyun ba, domin kuwa jiya an turo mini 'yan aike, ana so a haɗa kai da ni, in bayar da jininki, kuma ina da yadda zan yi na bayar, za ayi mini musaya da wani abu mai tsoka, wanda da na so, zan karɓa na bayar da jinin naki na yi maganin uban duƙusa, amma ina jin tausayin ki, ban san gaibu ba, amma akwai yiwuwar kina daf da buɗe sabon babi na ƙaddara, dan zuwanki gidan nan tuni kin yi wa ƙaddarar mukulli"
Cikin mamaki Nana ta ce "wace irin ƙaddara ce kuma haka?"
"A'a ba ni da damar cewa komai, amma ki tambayi ƙaisar mene ne tarihin kakaninki, za ki ga ta in da zuwanki gidan nan ya buɗe sabon babin ƙaddararki. Babu lallai ki fahimci labarin a take sai a gaba kaɗan za ki fahimta sosai da sosai. Abu ɗaya zan iya gaya miki, nima ina da alaƙa da labarin kakaninki ta wata fuskar"
"To kai ka gaya mini labarin mana"
Ya sauke numfashi ya ce "Ƙarfin hali kawai nake yi, maitar da take cikina ce take ta wahalar da ni, rabona da cin wani abu da sunan maita na fi shekara goma sha, saboda na sha maganin danne ta, kwatsam jiya na ci na san sai na yi jinya"
Nana har da gyara zama ta ce "To ita maitar mece ce? A addini babu maita sai dai kambun baka, to ita a ina ake samun maitar kuma ya ake yin ta"
Sai da ya yi dariya, Nana akwai tambaya ba kasafai take barin kanta ya kulle ba.
"Tabbas babu maita a addini, sai kambun baka. Maita tsafi ce sihiri ce, wani siddabaru ne da aljanu, da yake ƙara tasirin kambun baka. Ya danganta da wadda ka ke da ita. Akwai wadda ka ke iya ganin kurwoyin mutane, a siffofi na dabbobi, akwai wadda muke amfani da ita mu lalata abu. Idan muka kalli abu, ko ba mu tanka ba zai lalace. Mu kan zuba yawunmu idan ta taso mana a cikin abinci mu bawa mutum, sai ya yi ta rashin lafiya. Ina da jar maita ne, mai bala'in fiye da kowacce tare da wani aljani nake sarrafata, shi ne idan ya buƙaci jini yake zuwa kaina, sai na sha sai ya samu nutsuwa ya sake ni. Ina iya sarrafa maitar yadda nake so, ko shi ne Uban duƙusa ya zunguri maitar a cikina"
Nana ta jinjina kai ta ce "To amma ya aka yi ya iya zuwa gurin da ka ke, bayan ka na da magungunan su?"
*****
Nana a É—akin da sarkin baka yake bayar da magani ta tarar da shi, yana ganin wata mata da yaronta.
Ƙafafuwan yaron tamkar lagwani 'yan sirara marasa ƙwari, da hannayensa. Haka kansa ma ɗan mitsitsi da kaɗan ya fi lemon zaƙi fuskarsa tamkar tsoho abin tsoro yaron.
Uwar kuma sai rungume shi take yi cike da so da ƙauna.
Sarkin baka ya ce "Wata rana kin kashe gizo gizo cikin dare, a banɗakin ki, lokacin ki na da ƙaramin cikin yaron nan, ba tare da kin yi bismillah ko addu'a shiga banɗaki ba, an yi haka?"
Ta girgiza kai ta ce "Sarki ba zan iya tunawa ba"
"To an yi, shi ya faÉ—i abin da ki ka yi masa, kin bugawa jaririnsu takalmi, kin nakasa shi, shi suka ajiye a jikin gizo-gizo yana wasa, ki ka dake shi da takalmi, da kin yi addu'a da ya bar jikin gizo-gizon. Dan haka yanzu É—an su suka ajiye a jikin yaron naki, jininsa da sauran sinadaran jikin yaron ki, da za su saka ya girma, su yake sha yana girma, dan haka ko an cire aljanin mutuwa zai yi ba shi da sauran mamora sun gama lalata jikin yaron da garkuwar jikinsa" matar ta fashe da kuka ta ce "Dan Allah sarki ka taimake ni"
Ya girgiza kai ya ce "Magani kawai nake bayarwa, ba ni da ikon kashewa ko rayawa, zan baki magani ki koma gida, Allah ya baki wani"
Nana ta ce "Ya a ka yi ka san aljanin ne a jikinsa, kuma idan ya fita ba zai rayu ba?"
Buɗe ƙwaryar can, ki ɗaukko mini habbatussauda, akwai tazargade a ciki da tsakin kuka, da garin farin muski, duk ɗebo su da kan ki ki zo" babu musu Nana ta harhaɗo kayan da ya ce ta kawo masa.
Ya zira hannu a jakarsa ya ɗaukko garwashi, ya ɗora a kan wata tasa, ya ɗebi haɗin nan ya zuba a kai. Ko sakan goma ba a yi ba, yaron ya mimmiƙe ya din ga tsala uban ihu.
Sarkin baka ya cewa matar "Yaushe rabonsa da kuka, ko ya motsa wata gaɓa ta jikin sa?"
Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya tunawa ba, kullum a kwance kawai yake"
"To tun da ya yi kuka yanzu har da mimmiƙe wa, kin san ba ƙalau ba, baiwar Allah ki je gida, Allah ya baki wani"
Nana a ranta ta ce "Yaro ya ji wannan uban hayaƙin ba dole ya tsala ihun azaba ba".
Ya ce "Kamar har yanzu ba ki yarda da abin da ki ka gani ba ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a na yarda"
" 'yar wace ɗariƙa ce ke ne?"
Ta girgiza kai ta ce "Ɗariƙa ba ta cikin sharaɗin addini, dan haka ni ba ni da wata ɗariƙa"
Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, kin san kowace ɗariƙa akwai malamin da ta ke yarda da shi, da ki na da ɗariƙa da na ce ki saurari bayanin da wani babban malami ya yi a kan aljanu, amma manta kawai kin tashi lafiya?"
"Lafiya kalau Alhamdilillah" ta buÉ—e baki za ta sake magana ta ga bakin sarkin baka duk jini da sauran gashin zakaran da ya cinye jiya, wanda lokacin da ta shigo ba bu shi a bakinsa.
Zabura ta yi ta ja da ba, dan a zaton ta a mafarki ta ga ya ci zakaran ba a gaske ba, kuma da har ma ta manta ma.
Sarkin baka ya sanya hannu, ya zaro sauran gashin daga bakinsa, ya kalla ya yi murmushi ya ce "Kar ki tsorata Nana, tun a zuwan ki gidan nan da na so cutar da ke, sai na cutar da ke ta in da uban duƙusa ba zai iya ba ki kariya ba.
Har ga Allah bani da niyyar cutar da ke, kuma da gaske na san ba zan iya raba ki da shi ba, amma na rage masa tasiri ta wasu fuskokin daban-daban a tattare da ke.
Tabbas na cinye zakara da ransa, kuma uban duƙusa ne ya zungure ni, sai da na yi a gaban ki, dan ki cire yarda da ni kar ki yarda ki sadaukar mini da shi. Da na mallake shi zan ƙara ƙarfi da ƙarin tasirantuwar magunguna na, kuma zan kerewa sa'a tsakanin mutanenmu.
Ainihina ɗan wanzamai ne, na gaji wanzanci daga nan aka kai ni bara, na samu karatun Alqur'ani daidai gwargwado sai dai babu sauran litattafai na addini. Azabar yunwa ce ta sanya na fara bin matasa daji farauta, daga baya na watsar da allo na bar gurin malamin da aka kai ni gaba ɗaya, duk mahaifiyata 'yar maharba ce, amma na fi ƙarfi ga ɓangaren wanzanci.
Na yi rashin ji, na yi faɗi tashi, na yi wa harkar baka haye, har na so na fi 'yan gado ƙwarewa, hakan ya saka sauran maharba sako ni a gaba, da tsaface-tsaface da ƙoƙarin son kawar da ni. Sun sha haɗa kai domin su kashe ni.
Suka yi mini shiri, na zo ba na iya kama komai idan na fita harbi, ga rashin lafiya, dole na bazama neman magani a nan na haɗu da uban gidana, a masu magani ya bani maita, wadda ita ma wasu baƙaƙen aljanu ne suke tasrifinta, ya ƙara koya mini harkar magani, ga wanda na gada na wanzanci a gida. Ya yi mini girkar aljanu na zo na gawurta, na nemi na fi shi ma ko ma na ce miki na fishi ta kaowace fuska, kawai sai ya fara neman ya kashe ni, saboda hassada. Wataran mun fita farauta tare ya rikiɗe ya koma ƙaton maciji ya yi ƙoƙarin haɗiye ni, ni kuma garin ƙwatar kaina na kashe shi har lahira.
A haƙiƙanin gaskiya, ba na yadda na bawa mutum duk wani abu da zai cuci mutane a kan zalunci. Ina da tarin aljanu kala-kala da nake aiki da su. Na nemi ki sadaukar mini da uban duƙusa ne domin na ƙara ƙarfin tasirina. Rabona da maita har na manta, tana nan a jikina amma bana amfani da ita, na daina ta'amalli da aljanun maita, shi ne jiya ya zunguri maitar ta motsa mini. Yanzu haka sai na je na yi jinya, kuma zan ja dogon lokaci ban yi aiki ba, sai dai yarana su yi. Hatta Salamatu da ki ke gani ba mutum ba ce ba. Ainihin matar ba ta da lafiya sihiri aka yi mata, ba ta iya komai aka kawota nan. Na saka Salamatu a jikinta take yi mini aiki, Salamatu na fita gangar jikin za ta faɗi ta ci gaba da jinya. Shirin a jikin gawa aka yi mata, aka binne gawar ni kuma ba zan iya sakawa a ciro gawa daga makwanci domin karya sihirin ba, hakan tamkar tozarta gawar ne."
Jikin Nana duk ya yi sanyi da jin labarin da sarkin baka ya bata.
"Yarinyata da tana raye da ta kai kamar ke, na tafi farauta abokan adawa ta, su ka kasheta da babarta, tun daga nan ban kuma aure ba,, shiyasa na yi iya ƙoƙarin da zan yi na gagare su. Zan saka a mayar da ke gida, ba sai kin yi makonni biyun ba, domin kuwa jiya an turo mini 'yan aike, ana so a haɗa kai da ni, in bayar da jininki, kuma ina da yadda zan yi na bayar, za ayi mini musaya da wani abu mai tsoka, wanda da na so, zan karɓa na bayar da jinin naki na yi maganin uban duƙusa, amma ina jin tausayin ki, ban san gaibu ba, amma akwai yiwuwar kina daf da buɗe sabon babi na ƙaddara, dan zuwanki gidan nan tuni kin yi wa ƙaddarar mukulli"
Cikin mamaki Nana ta ce "wace irin ƙaddara ce kuma haka?"
"A'a ba ni da damar cewa komai, amma ki tambayi ƙaisar mene ne tarihin kakaninki, za ki ga ta in da zuwanki gidan nan ya buɗe sabon babin ƙaddararki. Babu lallai ki fahimci labarin a take sai a gaba kaɗan za ki fahimta sosai da sosai. Abu ɗaya zan iya gaya miki, nima ina da alaƙa da labarin kakaninki ta wata fuskar"
"To kai ka gaya mini labarin mana"
Ya sauke numfashi ya ce "Ƙarfin hali kawai nake yi, maitar da take cikina ce take ta wahalar da ni, rabona da cin wani abu da sunan maita na fi shekara goma sha, saboda na sha maganin danne ta, kwatsam jiya na ci na san sai na yi jinya"
Nana har da gyara zama ta ce "To ita maitar mece ce? A addini babu maita sai dai kambun baka, to ita a ina ake samun maitar kuma ya ake yin ta"
Sai da ya yi dariya, Nana akwai tambaya ba kasafai take barin kanta ya kulle ba.
"Tabbas babu maita a addini, sai kambun baka. Maita tsafi ce sihiri ce, wani siddabaru ne da aljanu, da yake ƙara tasirin kambun baka. Ya danganta da wadda ka ke da ita. Akwai wadda ka ke iya ganin kurwoyin mutane, a siffofi na dabbobi, akwai wadda muke amfani da ita mu lalata abu. Idan muka kalli abu, ko ba mu tanka ba zai lalace. Mu kan zuba yawunmu idan ta taso mana a cikin abinci mu bawa mutum, sai ya yi ta rashin lafiya. Ina da jar maita ne, mai bala'in fiye da kowacce tare da wani aljani nake sarrafata, shi ne idan ya buƙaci jini yake zuwa kaina, sai na sha sai ya samu nutsuwa ya sake ni. Ina iya sarrafa maitar yadda nake so, ko shi ne Uban duƙusa ya zunguri maitar a cikina"
Nana ta jinjina kai ta ce "To amma ya aka yi ya iya zuwa gurin da ka ke, bayan ka na da magungunan su?"