← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 33

Sashe 32

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

       Ta ajje wayarta taji sa'kon text tana dubawa taga Ahmad ne ya turo.

"Your eyes are great, your talks are great I am crazy for you hundred times over
I love you very much,goodnight Azizaty❤"

      A take ta soma blushing ta kasa dena maimaita karanta text d'in,har ta kwanta text d'in yana mata yawa a kai.

   °°°

    Washegari Nasreen ta samu 'kwarin jiki  sosai ,bayan tasha magani ta takura Reyhana ta kira mata Uncle dan ya kira da safe lokacin tana bacci.

     Numbern sa tayi dialing shiru har ta katse beyi picking ba,na biyu ma haka be d'aga ba.

     Ahmad kuwa lokacin suna hanya ze kai Zainab makaranta sannan ya wuce aiki ,ya tsaya a gidan mai be jima da fita daga motar ba sega kiran Reyhana.

     Zainab tana le'kawa ganin "Azizaty❤" ta share kiran koda Ahmad ya dawo bata fad'a masa an kira ba shi kuma be samu ya duba wayar ba suka tafi.

       Reyhana jitai ba dad'i ganin lokaci ya sake ja be ko kira ba,tayi tsammanin kiransa amma taji shiru dan haka itama bata sake kira ba.

      Se wajen 12pm ya lura da missed call d'in,ba 'bata lokaci yayi calling back,se a karo na biyu tayi picking.

       "Assalamu Alaykum".

        " Waalaikumussalam"Ya amsa.

         "Sorry kin kira bana kusa seyanzu naga kiran" Ya fad'a.

        "Tun fa d'azu kusan 3hr baka gani ba?"

         "I am sorry Ummien Nasreen kinji ai min afuwa". Ya fad'a.

        " Ga Nasreen zaku gaisa". Ta fad'a.

        "Toh ai baki ce kin ha'kura ba".

        "Naji toh shikenan". Ta fad'a.

        " Thank you".

        Nasreen tasa wa wayar a kunne"Ga Uncle ". Reyhana ta fad'a.

         " Uncle". Ta kira sunanshi.

           "Nasreen ya jikinki ?" Ya tambaya.

            "Da sau'ki Uncle yaushe zaka zo?" Ta tambaya.

          "Anjima zanzo ,kinsha magani?"

          "Eh". Ta amsa.

            " Yawwa toh mey kike so na kawo maki?"

        "Chocolate". Ta fad'a.

         " Good girl,zan kawo miki kinji ,ina Ummie?"

        "Gata nan". Ta fad'a.

        " Yawwa toh bata wayar".

       Mi'ka mata wayar tayi ,Reyhana ta amsa.Ahmad ya cigaba da janta da surutu.

     •••

   Waya se abinda ya 'karu dan yanzu Reyhana bata 'kin d'aga wayarsa gashi ta dena jin haushin 'kwata-'kwata hira suke yi sosai,da kanta ma kira take ta bawa Nasreen su gaisa bayan nan kuma sesu 'bige da waya.

                   ***

3 weeks later biki yana ta matsowa a yanzun Ahmad ya damu sosai dan ko zama be fiya yi a parlour ba balle Umma tayi masa zancen bikin a yanzu ana maganar lefe ,tun jiya Umma take masa maganar amma ya'ki tsayawa ma suyi maganar.

        Yau da ta gaji ta tare shi har d'aki ta soma yi masa maganar.

        "Kai shikenan kuma dan ance yarinyarnan 'yar uwakka ce kuma seka ke haka? Cha a kai ma auren bazawara ne?"

       "Umma zan fa bada ni kud'i kawai zan bada ba ruwana da wani lefe".Ahmad ya fad'a.

      " Toh har sai yaushe? Kud'in base a bayar da wuri ba".Umma ta fad'a.

      "Kaga yarinyarnan taje gida mey kake so tace da iyayenta? Ko kuwa so kake a d'aga bikin?"

      "Dama ai yakamata a d'aga". Ahmad ya fad'a.

      " Aiko baza'a d'aga ba ,mey make jira ? Gida ne ka gama kuma mey ya rage bazan zama mey baki biyu ba".

     "Amma Umm.." Be 'kare maganar ba ta katse shi.

      "Idan ma abinda kake tunanin gaske neh toh kama dena tuananin haka". Umma ta fad'a.

      " Mey fa?" Ya tambaya.

       "Reyhana, idan tunani kake ka dawo da ita ni bazan hana ka ba amma ba a wannan lokacin ba kaima kasani da farko kenan kuma abu na biyu shine inde Zainab bata son zama gida d'aya da ita ba bazaka had'asu ba".

       Shiru Ahmad yayi yana jin abinda Umma take fad'a shi sam ba haka yake so ba ,baida wacce tafi Reyhana a gunsa ita da Nasreen kawai yake burin yaga sun komo gareshi.

         "Kaji de mey nace maka". Umma ta fad'a.

         Daga haka ta tashi ta barshi yana ta tunane-tunane.

                    ***

  Reyhana a yanzu tana son komawa gidan Ahmad d'inta ,abu biyu ke bata tsoro shine aurensa da Zainab ga Sameer batasan ya zatai dashi ba.

      Yanzun ma tana d'aki tana tsammanin kiransa taji ya Umma zata d'auki abun dan cayai mata ze fad'a wa Umma amma ya kasa.

      A sanyaye ya d'auka waya ya kirata.

      " Assalamu Alaykum".Ta fad'a bayan ta d'aga.

       "Waalaikumussalam". Ya amsa.

       " Kayi magana da Umma".Ta tambaya.

     Shiru yayi bece komai ba tana tunanin ta ze soma bayani.

        "Reyhana..". Be 'karasa ba yayi shiru.

         " Ahmad i understand everything, na fad'a maka wannan ba abune mey sau'ki ba dole nasan Umma bazata ji dad'in haka ba kuma bazan so mu 'bata mata rai ba ,ina ganin kawai mu ha'kura".Ta fad'a.

       "No kidena fad'ar haka ". Cewar Ahmad.

       "Haka ne mana ,idan nayi haka banyi wa Zainab adalci ba d.."

      "Stop talking like this na fad'a maki,baza a kai wannan tsahon lokacin ba tare da kun kasance dani ba".

      " Mey kike tunanin yi?" Ta tambaya.

       "Kafin.."

       "Kafin ka auri Zainab na komo gidanka ? No bazan iya yin haka ba mey kake so Umma ta d'aukeni ? "

        Shiru yayi bece komai ba a zuciyarsa yana ta sa'ke-sa'ke,kowa da abinda yake tunani.Har suka 'kare wayar ba wani solution.

        Tunani ta shiga yi ko kawai ta ha'kura ta auri Sameer a huta.

AR²💖

       Don't forget to comment and vote.love you all💋

Pls share.

Jasko💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

*Last page*

🅿 3⃣5⃣

    *Not edited*

Bayan kwana biyu Zainab ta dawo,jikinta a yanzu ya fara sanyi da auren wannan karan ko fad'a masu batai ba zata dawo kawai ganinta Umma tayi.

Shi Ahmad yana aiki daga nan d'in ma seya biya gidansu Reyhana tukun ze komo gida.Tunda tayi tafiya Zaria befi sau uku sukai waya ba satinta d'aya a can.

°°°
Reyhana tana jin sanda ya shigo parlour amma bata sauka 'kasa ba se Nasreen ce taje.Koda ya kirata 'kin picking tayi har ya tafi bata sakko ba.

Tana zaune Nasreen ta shigo tana murna hannunta ri'ke da leda "Uncle ya bani". Ta fad'a tana nuna mata.

" Toh naji ". Reyhana ta fad'a.

Kayan ciye-ciye ne kala-kala ya siyo mata.

•••

Koda ya koma gida d'akinsa ya shige besan ma Zainab ta dawo ba.

Yana zaune sega kiran Imran." Aboki yane?" Cewar Imran.

"Ya kua". Ahmad ya fad'a.

" Da matsala ne?" Ya tambaya.

"Kaima ka sani ai"Ahmad ya fad'a.

" Reyhanan de?"

"Ehyi ita".Ya amsa.

" Kaima ka bari se bayan wannan auren tukun ".

" For how long?"

"Duk yanda ya kai mana, kai da ka ha'kura da Zainab d'inka ma". Imran ya fad'a.

" Kai baza ka gane ba,tunda mike dake na ta'ba ce maka ina son Zainab? Imran nifa bana son yarinyarnan kawai de saboda Umma shiyasa zan ha'kura". Ahmad ya fad'a.

Zainab duk wannan zancen dayake yi a kunnenta ,tana tsaye jikin 'kofar d'akin sa.Umma ce ta sata kira mata shi ,zuwan da tayi ta riskeshi yana waya kunnenta ya jiyo mata wannan maganar.

Gwiwoyinta sinyi mata li'kis da 'kyar ta iya komawa d'akinta.Kuka mara sauti ta zauna ta shiga yi ba 'ka'k'kautawa.

"For all this long dama Ahmad be ta'ba sonta ba ,so Umma ce tasa ze aureta ashe ? Shiyasa baya nuna damuwa dani ". Abinda take fad'a a ranta kenan.

Umma jin shiru yasa ta biyo sawu ,Zainab na hango tahowar Umma tayi saurin goge hawayen ta.

" Zainab, naji shiru koh baya nan?" Ta tambaya.

"Yana.. yana zuwa". Ta fad'a.

Gid'a kai tayi tukun Umma ta fita ta koma d'akinta. Zainab sake goge fuskarta tayi sannan ta fita taje ta kira shi ,sam bata nuna alamar wani abu ba kuma shima be gano hakan ba.

D'akinta ta koma ta shiga wani sabon kukan ,tana son Ahmad sosai ba 'karamin ciwo abin yai mata ba duk wannan abun da take ashe shirmenta take,bata ga amfanin auren wanda bata so ba.Ta fad'a a ranta.

***
Sameer yau da yamma yazo gidansu Reyhana, da kanta ta kira shi tace tana so siyi magana a ranta ta gama yanke shawarar fad'a masa zata aureshi.

Bayan yazo sun gaisa da Mommy ta tashi ta bar musu parlourn Nasreen dama bata dawo daga school ba.

Bayan sun gaisa Reyhana tayi gyaran murya kafin ta soma magana.

"Ahma..uh..Sameer". Ta kira sunansa shaf ta mance ta kira shi da Ahmad.

" Dama ina so na fad'a maka shawarar da na yanke,uhn..Sameer na..."Be bari ta 'karasa ba ya katse ta.

"Reyhana base kinyi bayani ba na gano abinda kike so kice,na dad'e da fahimtar hakan ni kaina tun sanda naga Ahmad.."

"Sameer ba haka nake nufi ba n.."

"Karki damu kanki ,kada ki manta na fad'a miki duk abinda kike so shi nake so ,Ahmad shi yafi kowa dacewa dake ,ya kamata ku kasance tare".

Shiru tayi ta zama speechless dan bata zaci haka ba daga wajen sa.

"Amma Sameer.."

"Is ok don't worry,Ahmad is the best husband for you I know you still love each other ,you have second chance to be together Reyhana,don't worry about me am really happy for you".

Tausayinsa ne ya kamata sosai Sameer is a very kind person duk wani abu da zatai baya ganin laifinta kuma tasan yana sonta sosai and duk wani abunda take so shi yake so.

" I am so sorry Sameer ". Ta fad'a.

" Don't worry".Ya fad'a.

"Thank you".

" Don't mention". Ya fad'a fuskarsa d'auke da murmushi.

Itama murmushin ta mayar masa tana jin tausayinsa.

***

•°• 4 month later•°•

Reyhana ce zaune a parlour tana ri'ke da wayarta tana chatting da Ikram.

Reyhana: "Ke wannan status d'in fa ? 'boye fuskar mijin naki kike kar wasu siyi miki snatching"

Ikram: " Hhh ,shima haka yake min bara kiga"

Reyhana: "Iyye ,Amaryar Sameer.

Ikram: "Kinji yaya ,kema Amaryar Ahmad"

Reyhana: "Au ramawa zaki"

Ikram:"Toh ku ina naku pic d'in,a turon na gani".

Reyhana: " Kizo har gida tukun"

Ikram: "Nafi kowa son hakan"

Reyhana: "Sorrynki yarinya se nan da 3yrs😝"

Ikram:"Chabb! Nan da wani watan zan duro 9ja"

Reyhana:"Kiyu biyayya se a kawo ki"

Ikram: "Ha ,ina Nasreen 'yan mata?"

Reyhana: "Tana school"

Ikram: "Se ke kad'ai,gaskia ya kamata ayi mata 'kani da wuri"

Reyhana: "Kede mike jira yarinya 😝 da twins zaki duro 9ja"
Chapter 32 · 0% Book details