← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 33

Sashe 19

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

        Bata jira amsarsa ba ta katse wayar,wani haushinsa take ji.Yana shigo bayan sun gaisa ta koma d'aki taja hannun Nasreen da se surutu take masa.

               ***
   Har Sameer ya tafi bata fito ba tana d'aki.Da yamma Aunty Asma'u tazo gidan Mommy.

        " Ya kuwa wannan mutanen har yanzu shiru?" Anty ta tambaya.

       "Hmm har yanzu, duk tsahon shekarunnan da aka shafe shiru koh waya basu sake yi ba". Mommy ta fad'a.

      " Amma wannan basu da mutunci,ace ko kira suji lafiyar 'yarsu bazasi ba balle akai ga ha'k'ko'kinta kuma,wannan akwai mutanan banza,ita Reyhana idan ta kirashi baya amsawa neh?" Anty Asma'u ta tambaya.

      "Toh wayar ta samu tashiga ma tukun,kuma idan ma an sameshi tace masa meh?" Mommy ta 'kare da tambaya.

     "Tuna masa zatai ba dutse bace 'yarsa ,su wannan da wane idon ma zasi kalli yarinyarnan? 'yarda a yanzu idan ance babanta bata sani ba".

     " Ita ajinta kakanta ne Abbanta ai,barsu su cigaba da yanda suke so lokaci zezo zai nemi 'yarsa aikoh".Cewar Mommy tana jinjina kai.

               ***
     2 days later

       Zainab around 9:30pm lokacin tana d'aki Umma ma ta kwanta,wayarta ce a hannunta tana chat a Whatapp.Contact take dubawa idanta ya tsaya kan sunan "Ya Ahmad" kamar yadda tayi saving.

     Tana gwada bud'ewa taganshi online,haka kawai ta tsinci kanta tana son yi masa magana,typing tayi ta tura masa sa'ko kamar haka;

"Assalamu Alaykum,ina yini".

   Seda aka shafe kusan 10min yayi reply dan har ta fita daga profile d'insa.

        Ahmad be kula da message d'in ba da wuri,ganin  "Xynab" kamar yadda yayi saving yayi reply da;   

                   "Wa'alaikumussalam,lafiya lau".

      " Ya kke? Ya school ?"Ta tura.      

    "Alhamdulillah,ya kuke ?" Shima ya tambaya.

"Lafiya lau".Tayi replying.

" Ina Umma koh tayi bacci?" Ya tambaya.

    "Eh". Ta amsa.

      " Ok". Ya amsa.

Yatsa ta sa a baki tana tunanin mey zata kuma cewa ,kusan 2min basu sake magana ba.

    "Kin fara zuwa school d'in?" Ya tambayeta.

Murmushi ta fara yi ganin ya sake mata magana wanda bata zata ba.

   "Se Monday". Ta amsa.

" Ok,wani course?"Ya tambaya.

"Industrial chemistry". Tayi replying.

" Good👍 Allah ya bada sa'a".Yayi sending.

"Ameen, tnx". Tayi replying fuskarta d'auke da murmushi.

  " It's 10pm right? You should have sleep.

"Yaya by 11:00 dae koh". Tayi sending.

" 😱 it's late ,what will you do?"

"Ha! Chatting with you mana". Ta tura.

     " Are you sure? "Yayi sending.

    " Yes mana don't you believe me?"

"I do believe, ok am quitting now".Ya tura.

" Ok,nima yanzu zan kwanta".

"Gudnight ,recite du'a before sleeping".

" Tam night,bye".Ta tura.

Kamar yadda yace tayi addu'a tukun ta kwanta,shima ajje wayar yayi ya dauro alwala ya tada sallah.

AR²💖

     *Comment,share and vote pls.Luv u all😘*

Jasko💕      
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣0⃣

    Alhamdulillah we reach page 20,happy page twenty🎈🎈   Umeeyr tace "Zainab want to snatch our ya Ahmad " 😂
Juma'at Kareem.

     Reyhana kwance a kan gado ,Nasreen na manne da jikinta ta zagaye hannunta a bayanta da hannin damanta na hagunta kuma tana shafa mata gashin kanta,Nasreen da tayi nisa da bacci hankalinta kwance.

       Babu rana da zata wuce Reyhana batayi tunanin Ahmad ba,idan ta tuna shekarun da aka shafe basu sake had'uwa ba kuma ba waya seta ji haushinsa wani 'bangaren zuciyarta kuwa har yanzu da gurbin sa a ciki."Meyasa ze guji 'yarsa? Mey Nasreen tayi masa a duniyannan daya watsar da ita?" Abinda kullum take tambayar kanta wanda amsar hakan ta gagara.

       Bata yi aune ba taji danshi a fuskarta,hannun ta sa da goge hawayen ,the more tana gogewa the more yana sake fitowa dan haka ta dena mah,gam ta sake ri'ke Nasreen a jikinta tare da d'ora ha'barta lightly a goshinta ,idonta ta rufe gam ba jimawa bacci yai gaba da ita.

                 ***

    Zainab 8am ta tashi dan bata fiya bacci dayawa ba bayan subh,kamar kullum a nitse tayi shara ba tare da Umma ta tashi ba,haka toilet ma ta wanke sannan ta koma d'aki.

       8:20am,wayarta dake jone a charge ta zare.Chat da sukai da Ahmad jiya ta shiga dubawa a hankali step by step tana sake karantawa tana murmushin.

       Data tayi switching on ko zata ganshi online,koda ta duba taga be hau ba tun jiyan.

       Tana jiyo fitowar Umma daga d'aki ta ajje wayar ta fita,cikin rissinawa ta gaisheta.

      "Zainab da sassafennan kika tashi harda shara".Cewar Umma.

      Murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba." To sannunki da 'k'o'kari".Umma ta fad'a.

       Har abincin breakfast tare sukai da ita,ko wanke-wanken ma bata bari Umma tayi ba ,haka Umma tayi ta shima ta albarka halin Zainab yana birgeta.

            ***
    Kiran Sameer ne yau ya tashi Reyhana 8:47am taji 'karar wayarta.

      "Hello". Ta fad'a bayan ta d'aga muryarta a cushe.

       " Morning ". Ya fad'a.

       " Morning ". Ta amsa rai a 'bace.

      " Tun d'azu nake jiran 9 yayi sena kira ki amma  I can't even wait,just want to know how you're doing ". Ya fad'a.

      " Am ok". Ta amsa kamar ta sha'ke shi.

     "Nasreen fah is she awake?" Ya tambaya.

      "Ya Allah". Ta furta a ranta dan ta gaji da amsasa ,magana da safe aiki yake mata haka kurum ma balle da Sameer.

       " Bata tashi ba nima bacci nake". Ta fad'a.

      "Oh am sorry na tashe ki,I just can't wait to hear your voice"

        "Uhmm". Ta fad'a.

        " Ok mayi waya anjima,yanzu ki koma bacci kinji bye". Ya fad'a.

         Ko amsasa batai ba tayi hanging taja tsuka.Baccin ma se ha'kura tayi.

      Tun kafin ta 'karasa sakkowa take jin hayaniyar su  Sageer.

        "Ku kuma kun cikawa mutane kunne daga tashi". Ta fad'a bayan ta sakko.

         "Hira muke me dad'i". Cewar Ikram.

         " Ni rufen baki". Ta fad'a tare da nufa kitchen.

     Mommy ta tarar tana had'a breakfast, tama kusa gamawa nan ta taya ta suka gama.

   °Cyprus°

       Yau Ahmad ba class saboda haka shida Imran suk a fita zagayawa bayan sunyi breakfast.

        Imran ya takura Ahmad seyayi pic,kusan seyace be ta'ba gani ya tsaya yin pic ba a hanya.

        "Kawai d'aya zakai,haba ko Umma ai ka turawa taga d'an handsome d'inta". Imran ya fad'a yana dariya.

       " Malam rabi dani". Ahmad ya fad'a yana cigaba da da tafiya.

        Imran daya tsaya daga can baya ya 'kwala masa kira.Shi ya zaci ko wani abune ,yana juyawa yaga flashing camera.

        "Wow! Kaganka kuwa". Cewar Imran yana 'karasowa inda yake.

         Ahmad a jikin pic d'in ya zira  hannunsa d'aya a aljihu hakan ya bada style sosai gashi fuskarsa da d'an murmushi (If u want to see the pic comment with yesss let me see who fall for Ahmad😂).

      "Let me know idan kana son pic d'in kai magana na turo ma,if not senai posting a insta kaga baza a rasa masu so ba". Ya fad'a.

      Ahmad jin ya ambaci insta yasa ya ciro wayarsa ya mi'ka masa.

           " Ha! Better ". Imran ya fad'a.

           Sun d'an zazzaga gari tukun suka komo gida.

       Su Ibrahim kuwa dama jiran dawowarsu suke coz suke da kitchen😂

         " Alhamdulillah gashi ya dawo".Ibrahim ya fad'a.

       Shi Ahmad ma ya manta shaf inba yanzu da sukai magana ba.

       "Maza yau mey za'a dafa mana neh?" Idris ya tambaya.

        "Se abinda kuka gani". Ya amsa.

         "Nikam yau d'an wake nake son ci". Cewar Ibrahim.

          " Nikuma sakwara".Idris ya fad'a shima.

         "Nikam dambu". Imran ya fad'a.

         " Kun dad'e baku ci ba".Cewar Ahmad ya watsa musu harara.

        Dukansu dariya sukai daman salan sashi magana ne.

         D'aki ya shiga ya rage jacket d'in daya d'ora kan kayanshi sannan ya fito zuwa kitchen.Seda yai kusan 5min yana tunanin abinda ze girka, idea ya d'auke yau da gobe ta'ki wasa sun gaji da abinda suke dafawa.

      Fridge ya bud'e yana kalle items d'in ciki,idea neh ya fad'o masa ya d'akko wayarsa yai searching nan ya gano stew na cous cous

       "Butter nut squash and White bean"

     Daya duba yaga suna da items da ake bu'kata,ba tare da 'bata lokaci ba ya fara had'awa.

         Kitchen yayi kaca-kaca everything scattered Maza! anyi girki😂

       1hr later table is complete lunch is ready,Imran shi ya fara serving su Idris da 'kamshi ya bigi hancinsu suma suka d'ibi nasu.Ahmad kallonsu ya tsaya yi yana jira yaga ya taste d'in abincin nasa ze kaya.

       Imran spoon d'aya yakai baki yana tattaunawa still bece komai ba,alama Ahmad yayi masa da gira "yaya?"

        "That's yummy! bro"Imran ya furta yana sake d'iban wani loman.

        " Kai dama kasan da wannan kake barinmu da jollof?" Cewar Idris.

       "Wannan anyi mugun mutum". Ibrahim ya fad'a bakinsa cike da abincin.

       Bece komai ba se murmushi kawai dayake shima yaja plate ya ziba.

       Bayan sun gama ya koma d'aki,in less than 2min sega kiran Xynab.

          " Assalamu Alaykum".Tayi sallama.

         "Waalaykumussalam". Ya amsa.

         " Ina yini".Ta gaishesa.

          "Lafiya".ya amsa.

           " Ga Umma zaku gaisa".Ta fad'a.

           "Bari na kira". Ya fad'a tare da hanging.

       Baya so yai exhausting credit nata tunda alhamdullillah ana basu allowances.

         Umma ce tayi picking bayan ya sake kira,nan suka gaisa sun jima suna hira da ita kafin daga bisani sukai sallama.

                 ***

 Zainab  tun chat da sukai rannan basu sake yiba har ta fara zuwa school kuma yanzun an gyara wayar Mommy dan haka bata sake kiransa ba,shima test da yake dashi kwana biyu yasa baya hawa chat.

       Kusan about 2weeks kenan ,Zainab an 'kwame gaban mirror ana tsara d'auri farar fusakarta tasha make up as always bata fiya zama ba janbaki ba se kwalli shima bata fashin sawa ko ba fita zatai ba.

       Zainab itama tana da nata irin kyan most her exciting lips O shape matsakaicin tsaho gareta and ba siririya bace a murje take but not fat whoo! (Don't ask me about her hair fah,idan nace muku Fulani ce you know kawai!
😁)

       Ko breakfast bata tsaya tayi bama,12:30 sun fito daga class a cafeteria suka tsaya it a da friend tata koda taci abinci wayarta ta d'auko ta bud'e whatapp luckily taga Ahmad online wani farinciki ne ya ziyarceta.

Xynab: "Hello"

" Hi".Yayi replying bayan  1min.

Xynab:"Ya school?"

Ahmad:"Alhamdulillah".

Xynab:  " Ni baka tambayi nawa school en ba". Ta tura bayan kamar 3min.

Ahmad:"Ohh ya school? ".

Xynab:" Seda na ro'ka

Ahmad:"Sorry". .

Xynab:" Is OK".

Xynab:"Toh kai wani course make studying?"

Ahmad:"Computer science".

Xynab:" Nyc".

Ahmad:"Where are you now?"

Xynab:"School".

Ahmad:" At school and you are chatting? "
Chapter 19 · 0% Book details