← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 33

Sashe 18

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

       Dede lokacin Mommy ta shigo,baki wangalau ta saki ganin irin yafen da Reyhana tayi.

       " Reyhana mayafinne zaki sa'kala haka  a kafad'a?" Mommy ta fad'a.

       "Dinner fa akace". Ta fad'a tana kallon mudubi.

        " Toh ita wannan fa?" Mommy ta tambaya tana kallon Reyhana.

         "Tana tare daku mana Mommy". Cewar Reyhana.

           "Ikram mije,bye baby girl". Cewar Reyhana tare da shafa kumatunta ta d'auka key d'in motarta.

            Ko jira abinda Mommy zata ce basi ba suka fice,take Nasreen ta rusa ihu,Mommy kanta ta dawo tana rarrashinta" Atoh babarki ta ya dake".Mommy ta fad'a.

        Galleliyar farar Accord Abba ya siya mata bata fi shekara d'aya ba.

        Da sauri ta zugesu suka bar gidan gudun kar Abba ya dawo yace dare yayi tunda 9pm ya shige.

         Ba jimawa suka isa wajen bikin, sakin baki sukai dukansu ganin Sageer a wajen shida wata beb suna zaune.

          "Ikram kinga yarannan koh?" Reyhana ta fad'a disbelievingly.

          "Yes,na ganshi". Ikram ta amsa tana kad'a kai still bata d'auke idonta a kansu ba.

        " Ina cayai mana baze samu zuwa ba kansa ciwo yake,amma kin ganshi".Reyhana ta fad'a harda nuni da hannu.

       "Ai bama wannan ba kalli jibgegiyar da yake kulawa wannan ai seta zaune shi". Ikram ta fad'a.

      Dariya suka hau yi ganin de abin bana 'kare bane suka 'karasa ciki ba tare daya kula dasu ba,dan yayi nisa se tsarata yake, ita kuwa madam d'in ta hakince se blushing take.

       Sageer bade 'yan mata ba,number 1 ne wajen kula bebs,ga tsaurin ido as age d'insa 24 da 'yan kai se a gansa da 'yan 25 zuwa 26 ma,duk wannan abin da ake Mommy bata da labari dan ita a ganinta Sageer har yanzu yaro neh.

       Reyhana tunda tayi pic da Bride ta samu seat ta hakimce,Ikii ta bari can itada sauran sa'anninta suna ta shoshalewa.

        Kamar daga sama taji muryar namiji.

        " Assalamu Alaikum".

    Tana d'ago kanta taga Sameer(D'an yayan Mommy).

            "Sarkin naci". Ta fad'a a ranta.

             A ciki -ciki ta amsa sallamar,take ta d'aure fuska.

            " Toh waye ya fad'a masa ina nan?" Ta tambayi kanta,wata zuciyarce tace"Ikram".

       "Munafuka!" Ta furta.

       "Na'am?" Cewar Sameer.

        "No bance komai ba".Ta wayance ,batai tunanin yajita ba.

         " Surprise, right?"Ya tambaya yana d'age gira .

     Hakan yana d'aya daga cikin abinda yasa take jin haushinsa,iyayin tsiya.

        "Surprise d'in mey kuma?" Ta fad'a cikeda 'kosawa.

         "Ehman,I know zaki mamakin ganina anan tunda baki sanar mini ba". Ya fad'a.

          " May i sit?"Ya tambaya.

          "Uhmm". Ta fad'a.

      Ji take kamar ta kurma ihu,hirarsa tamkar kukan sauro haka take ji.

      " Thanks". Ya fad'a.

     Thanks d'in ma cikin wani murya da bata so ya fad'a.

       Dinner d'in ma seda tayi regretting zuwa saboda Sameer,ya cika ta da surutu iya kaci tace "Eh ko a'a.

       10:39pm na bugawa ta kira Ikram suga tafi,kafin su tafi a wajen ma seda ya isheta.

     A hanya tayi ta balbale Ikram da masifa har suka is a gida ,Nasreen tuni tayi bacci da sand'a suka shiga d'akunansu kar Abba ya jiyo su.

       Sameer tun kafin tayi aure yake son Reyhana ,amma fafur ta'ki shi.Bata dad'e da aure ba ya tafi America ,befi shekara  d'aya da dawowa ba yaji labarin mutuwar auren Reyhana shine ya sake komowa har yanzu beyi aure ba ,yana da shekara 32 a yanzu.Ba fari bane chan yana da kyau shima kuma dogo ne,ba 'karamin son Reyhana yake ba gashi duk yadda takai ga shunning d'insa baya ha'kura.

    Cyprus***

         Zaune kan kujera a falo,su Imran sun d'an fita.Ahmad yanzu sun zama 'yan gari sun saba da abubuwa ,Imran dashi sun zama abokai sosai shi kad'ai yasan ya ta'ba yin aure,hakan ma wani lokaci ne daya ga pics na Nasreen a wayarsa kuma yana yawan ji yana maganarta a waya idan sunyi waya da Umma.

        Babu wani chanji sosai gameda shi na shekaru sede fatarsa data 'kara yin haske, ga gashin kansa ma da yanzu ba sosai ya fiya askeshi duka ba ,yananan luf-luf hakan yana daga cikin amsarsa da weather d'in 'kasar tayi.

       Kiran daya shigo wayarsa ne yasa ya ajje cup d'in tea dake hannunsa.

    Number ne daga Nigeria ya gani amma besan mey shiba.

            "Assalamu Alaykum". Ya fad'a bayan yayi picking.

            " Waalaikumussalm". Yaji muryar mace ta amsa.

   AR²💖

         *Toh! Readers guess who?*

   Jasko💕

       *Comment,share and vote, luv u all😘*

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣9⃣

        "Ya Ahmad ina kwana".Aka fad'a daga d'ayan 'bangaren.

         " Lafiya lau".Ya amsa yana so yayi recognizing muryar me magana.

            "Zainab ce". Ta fad'a.

             " Oh! Zainab, ban d'auki muryar ba ya gida?" Ya tamabaya.

              "Lafiya lau,ya karatu?" Ta tamabaya.

              "Alhamdulillah". Ya amsa.

              " Ina gidan Umma fah".Ta sanar masa.

             "Ok ,kuna hutu ne??" Ya tambaya.

              "Uhh ai mun kammala ma". Ta amsasa.

        " Good,Allah yasa albarka". Ya fad'a.

           "Ameen,ga Umma zakui magana". Ta fad'a.

         " Ok bani ita".

        Umma da take kusa da ita ta mi'ka mata.

        "Ahmad kaji wayata shiru koh?" Cewar Umma bayan ta ma'kala a kunnenta.

        "Eh na kira bana saminki". Ya amsa.

         " Wayar ce ta samu matsala shine nasa Zainab ta kira ka ,tazo nan gida dayake ta samu admission a B.U.K  zata fara zuwa".Umma ta fad'a.

     "Ok,yanzu take fad'a mini sunyi graduation ashe har ta samu admission". Cewar Ahmad.

      " Ehh,na sami mey taya ni zama".Umma ta fad'a.

        "Gaskiya kam,zan kira sadiq seya kai maki gyaran wayar taki".

        Hira kad'an suka ta'ba sannan sukai sallama.

                ***
     Ta 'bangaren su Reyhana kuwa Inno ta tafi garinsu anyi rasuwa,yau kowa daya tashi seya nufo dining yaga wayam.

        " Mommy kuwa ta fito?" Reyhana ta tambayi bassam da yake falo shida Walida suna kallo.

       Bassam a shekaru ukunnan ya 'kara girma sosai dan ya kere Reyhana a tsaho yana 18yrs a yanzu,Walida ma ta 'kara tsaho se siranta kamar a 'balla ta😂

       "A'a". Suka amsata.

       " Tohh! 9am fah,kace yau za'a sha yunwa kuwa".Reyhana ta fad'a tare da shiga kitchen d'in.

      Ruwan tea ta d'ora a tea pot ta komo falo tai joining d'insu.

     Ba jimawa Mommy ta sakko."Ina kwana ".Suka gaisheta a tare.

      " Lafiya".Ta amsa had'e da yin hamma.

     "Bade baku d'ora wani abu ba?" Mommy ta tambaya.

      "Ina fa,yanzu kowa yake tashi". Reyhana ta amsa.

      " Aiko yau kowa ya d'and'ana inno kunsan bata nan nima yau hutawa zanyi kwasan yadda kukai".Mommy ta fad'a.

    "Nide na d'ora tea,Ikram da Walida kuyi saura". Reyhana ta fad'a.

      Ikram tana bacci Walida ta taso ta se turo baki take ita batason aiki.

       Sageer yana fitowa daga d'akinsa yaji kiran Reyhana, sasu tayi a gaba har bassam suka shiga kitchen Mommy tai zamanta a falo.

      " Oya jeki d'ebo dankali keda Walida zaku fere"Reyhana ta fad'a.

      Sageer shi dariya ma abin ya bashi saurayi dashi wai za'a had'a da girki.Gefe guda ya tsaya ya nad'e hannunsa  yana kallan ikon Allah ,jira yake yaga shi kuma nashi aikin.

      "Toh su Sageeru se'ai blending pepper da onion". Reyhana ta fad'a tare da dire kayan miyan data d'ebo a bowl.

      Wani dariya ya fashe da ita harda ri'ke ciki." Haba kema da wasa kike ki dubi kamar ni kice nayi wani blending sekace cooku".

     "Kana mamaki koh,karkayi yaro in kasan wata bakasan wata ba".Ta fad'a tare da d'an matsowa kusa dashi ta rad'a masa yadda  su Walida baza suji ba.

       "Koh kayi ko kuma na fad'a wa Abba da Mommy d'ansu ya girma har Beb yana da ita".

         Sageer da sauri ya zaro ido yana mamakin yadda akai ta sani,what if da gaske zata fad'a ? Ya tambayi kansa.

     " Naji".Ya fad'a.

    Murmushin da yake ma ya koma ciki,turn d'in Reyhana ne se murmushin mugunta take.Su Ikram da suke jira suga zeyi ko baze ba take suka hau 'kunshe dariyarsu.

     Bassam kuma aka had'ashi da 'bare spices da za a had'a sauce d'in.

      Kowa aikinsa yayi facing Ikram se masifa take wa Walida wai tana fallatsa mata ruwa idan zata saka dankalin a ruwa.

     Sageer wai dan yayi sauri se wani cakumar attarugu yake yana cire 'ya'yan attarugun da hannu yana cillawa a blender d'in.

     Bassam mey spices har ya gama yana shirin fita ta tsayar dashi."D'an albarka  a soya wa 'yata indomie da 'kwai mana".Ta fad'a tana masa winking eye.

     Buga 'kafa yayi ya dawo se 'kun'kuni yake.

       Sageer bayan ya gama blending har ze fita yaji saman idonsa na 'kai'kayi, yatsansa ya d'ora ya sosa wheui!

    Lokaci guda ya fara dancing a tsakar kitchen d'in, Reyhana da ta d'ora kaskon suya taji 'kara.

     Kallone ya dawo kansa,Mommy da take falo ma seda ta jiyo ta shigo kitchen d'in.

      "Lafiya?" Ta tambaya.

      "Mommy idona!" Abinda yake fad'a kenan.

       "Kai mey ta kaika sa yaji a ido sekace yaro". Mommy ta fad'a tana dafa ha'ba.

        " Zoka tara idon a fanfo ka wanke".Reyhana ta fad'a kamar mey shirin yin dariya.

        "A daddafe ya 'karasa sink d'in yaje ya tara fuska ,duk da ya wanke idon be fasa dafe idon ba.

       " Ka tsaya mana a hure ma".Reyhana ta fad'a tana d'age ta dafe kansa sekace 'kan'kanin yaro.

      Ba su Ikram ba har Mommy seda tayi dariya,'kwace kansa yayi ya tsaya yana gogewa da hannun rigarsa.

     Ficewa yayi daga kitchen d'in ya barsu suna dariya."Maganinka kenan".Reyhana ta fad'a.  

     Kafin su gama girkin seda suka 'bata kitchen d'in, se 10:30am suka chi abincin.

     Nasreen da ta dad'e da tashi amma bata fito ba tana toilet ta saki fanfo se wasan ruwa take.

        Seda Reyhana ta koma d'aki ta jiyota,fito da ita tayi ta 'kwa'k'kwad'eta tayi ta kuka seda Abba ya rarrasheta.

       Har Reyhana tayi wanka ta shirya Nasreen bata sake hawowa saman ba,a falo ta iskesu ita da su Mommy.

      "Zo muje nayi miki wanka".Ta mi'ka mata hannu.

      Kafad'a ta ma'kale ita bazata yi ba,Reyhana ta mance ma fushi take.

      " Ki zauna hakan ina ruwa na,ki fara zuwa makaranta kowa ma ya huta".Cewar Reyhana tare da zama daga gefen Walida.

     Ba jimawa wayarta tayi ringing, tana dubawa taga Sameer.

        "Mtchww!". Tayi tsaki ta ajje wayar.

         Mommy data kula da ita tace " 'Kalau?"

       "Sameer ne". Ta amsa.

        "Toh kuma seki 'ki picking? Ni bana son wula'kanci".

         " Mommy damuna zeyi kawai".Reyhana ta fad'a.

      Se a kira na biyu neh tayi picking,bayan sun gaisa take ce mata yana bakin gate.

      "Toh ka shigo mana". Ta fad'a.
Chapter 18 · 0% Book details