← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 33

Sashe 31

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jisku har dhadkan tu ho aise🎶

Dil ko kya dhadkana🎶

O Zaalima o zaalima🎶

(The one whose every heartbeat are you,
Why quicken his heartbeat?
O cruel one!)

Saasson mein🎶

Teri naz deekiyon ka🎶

Ittar tu ghol de-ghol de🎶

(Mix the perfume of your closeness In my breath)

Main hi kyun 🎶

Ishq Zaahir Karin 🎶

Tu bhi kabhi bol de..bol de🎶

(Why I alone should express my love,
You too express your

Le ke jaan hi🎶

Jayega meri🎶

qaatil har tera🎶

Bahana hua🎶

(Your every excuse is a killer,
It will definitely kill me)

Tujhse hi shuru🎶

Tujhpe hi khatam🎶

Mere pyar ka🎶

Fasan hua🎶

(The story of my love Commenced
and culminated at you)

Tu shamma hai to yaad rakhna🎶

Main bhi hoon parwana 🎶

O Zaalima o zaalima🎶

(If you are a candle, remember that
I am a moth (Moth is attracted to the flame)
O cruel one!)

Deedar tera milne me baadhi🎶

Chhote meri angdaayi🎶

Tu hi bata de kyun Zaalima🎶

Main kehlaayi🎶

(I pandiculate only after I see you
Now you tell me,
why I am called cruel?)

          Wa'kar har ya gama playing Reyhana bata kalle shi ba ,ta sani yana sane ya 'karo volume d'in.

      Zaalima (lol)

       Yana parking Nasreen ta fara fita se itama Reyhana tayi saurin yun'kurin bud'e 'kofar Ahmad yai saurin kullewa.

        "Ka bud'e min na fita".Ta fad'a ba tare da ta kalleshi ba.

        " Why are you punishing me like this Reyhana?"Cewar Ahmad bayan ya waigo.

       "Kaide kake punishing kanka".Ta fad'a.

       " How?"Ya tambaya.

        "Please ka bud'en na fice". Ta fad'a.

        " Naji zan bud'e miki amma sekin amsan tambayar da zanyi miki".

       Banza tayi dashi bata ce komai ba ta kauda kai.

      "Do you really love him?" Ya tambayeta.

       D'an murmushi tayi ta kallo shi"Yes i do meyasa zaka damu kanka?"

     "Saboda nasan 'karya ne, ba kya sonshi I can see it in your eyes"

     "Really?"

     "Yes,Reyhana ki dena pretending nasan you still love me ,don't worry bazaki zauna da kishiya ba". Ahmad ya fad'a.

  " Tunda na amsa maka ai yanzu seka bud'e min koh".Ta fad'a.

     "Fine ". Ya fad'a sannan ya bud'e 'kofar ta fita,ko waiwayowa batai ba ta shiga wajen taron.

         Se bayan ta shige tukun ya tafi.

                    ***

   2days later°•°

         Nasreen a kwana biyunnan tana fama da rashin lafiya ,an kaita asibiti amma zazza'bi ya dawo.

      " Reyhana ki kira Ahmad ki fad'a masa yarinyar nan bata da lafiya". Mommy ta fad'a.

      "Mommy ki bari kawai zan maida ita da kaina base an fad'a masa ba".

      " Koh kin kaita da kanki ai ya kamata de ki fad'a masa koh". Cewar Mommy.

      "Toh". Reyhana ta fad'a.

      Tare da Walida suka tafi asibitin Nasreen se kuka take tana shagwa'ba,doctor na duba ta aka ce se an mata 'Karin ruwa zama ya kamasu.

      Hakannan bayan an d'aura mata drip ta kira Ahmad ta fad'a masa.Aikoba jimawa yazo wajen 12pm lokacin.

       " Uncle". Nasreen ta kira sunanshi murya a sanyaye.

      "Sorry kinji  zaki sami sau'ki". Ya fad'a yana dafa goshinta da zazza'bin ya soma sauka.

       "Meyasa baki fad'a mini da wuri ba?" Ya tambaya yana kallon Reyhana.

       Shiru tayi bata amsa shi ba sema phone d'inta data d'auko a jaka ta fara tapping.

         Ahmad ganin tayi masa banza bata yi masa magana ba ya tura mata da text.

    Ana yi miki magana kin'ki amsawa why?

Se lokacin ta d'ago ta kalleshi sannan ta kauda kanta.

         Gefe ya samu ya zauna ya kira Umma yake fad'a mata.Tashi yayi ya fita bata san ina zaije ba shima be fad'a mata ba.

      Fruit ya siya masu da gasashshen chicken se takeaway da juice ya dawo ,fuskar daya gani a room d'in yasa ya had'e rai lokaci guda.

         "" Wannan banzan meya ke yi anan?"Ahmad ya fad'a a zuciyarsa.

        'Karasowa yayi ciki ya samu waje ya ajje ledar kayan sanna yaja gefe ya tsaya,kallon -kallon suka shiga yi da Sameer da take opposite dashi ,Reyhana kuma ta zaune gefen Nasreen da ta ri'ke mata hannu karta barta .

      Ahmad wata uwar harara ya watsa masa  shima Sameer ya mayar masa,yau ko gaisawar basi ba.

     Takawa Ahmad ya yi har kusa da Nasreen ya shafa mata kai yana mata sannu,ta gefen ido kuwa yana kallon Sameer yana so ya nuna  shine fa mey 'ya.Itama Reyhana ta gano haka amma setai kamar bata gansu ba.

         Bayan kamar 20min sega su Mommy da Abba kusan dukansu banda Sageer da Ikram.Suma shagwa'bar tayi ta musu tana nuna musu hannunta da aka saka mata carnular.

       Sameer ne ya fara tafiya kafin Ahmad dan se wajen 3pm hakan ma bawai ya tafi duka bane su Umma ya tafi d'aukowa.Mommy ce ta bud'e ledar taga siyayyar daya yo musu ta bawa Nasreen,Reyhana kuwa 'kinci tayi ,abincin da su mommy suka kawo shi ta ci.

         Reyhana da batai tsammanin ganin Zainab a asibitin ba tasha mamaki ganin su tare da Umma ,a zuciyarta tana fad'in."Haka ta girma yarinyarnan?"

      Kamar bazata amsa gaisuwa ba Reyhana tace "Lafiya".Bayan Zainab ta gaisheta.

         Ahmad yana kallonta ya gano sauyin fuskarta suna had'a ido ta watsa  masa
harara ,shi dariya ma ta bashi kai de basarwa yayi.

      " Anty Zainab anan zaki sauna?" Nasreen ta tambaya.

       Murmushi tayi mata ba tare da ta amsa ba.

     "Ai ba kwana zami anan ba anjima zamu tafi".Reyhanana ta fad'a tana kallon Zainab.

       " Kijimin mata kallonnan na miye kuma?"Zainab ta fad'a a ranta.

       Da Umma suka tashi zasi tafi Nasreen tace ita  a lalle se Zainab ta zauna,haushi du ya ishi Reyhana .Mommy tace toh su sesi ragewa Umma hanya anjima Zainab sesu tafi da Ahmad.

      Haka kuwa aka yi Umma tabi su Mommy ,aka bari daga Zainab ,Reyhana se Ahmad.Shuru ne ya ziyarci d'akin bame magana itama Nasreen d'in ta gaji.

     Zainab a gefenta na dama Reyhana a hagu Ahmad yana daga gefe.

        Lokacin maghrib ya yi Ahmad ya fita  sallah ,bashi ya dawo ba se bayan isha'i.Yana shigowa yaga doctor yazo ,lokacin za'a sallamesu.Duk wani charges Ahmad ne ya biya ,sannan suka fito tafiya.

      Ya d'auki Nasreen da ta langa'be a kafad'a."Ni ba a gaba zan zauna ba ,a baya nakeson kwantawa ".Nasreen ta fad'a lokacin da suka 'karaso jikin motar.

        Bayan ya bud'e ya kwantar da ita tukun ya bud'e nashi gidan gaban.A tsaye ya gansu kowacce bata Shiga ba  ,suna daga bayan,kowacce a ranta tana tunanin mey shiga gidan gaba.

     " Ko a zuwanma a gidan gaba ta zauna ?da alama yanzun ma so take ta zauna ,Chab! aiko sede ta zauna a baya".Cewar Zainab.

     "Rawar jiki kike ki Shiga gaba? aiko sorrynki gaba nake dake yarinya duk da ba son shiga nake ba yau sena zauna let me see tsakanin nida ke waya fi damuwa da ita ,naga duk wannan kurarin da ake a iya ina ya tsaya son". Reyhana ta fad'a tana matsawa gaba.

      " What is she trying to do ? Matar nan itace mey 'kin shiga gaba amma yanzu ,she is looking for trouble ,wait itama Zainab shigar take so tayi?"Ya tambayi kansa lokacin da yaga itama Zainab tana matsowa.

AR²💖
              1807+ words I try koh? ,dan dan Zee &Rey WWE RAW🔥 😹

    Don't forget to tap on that Star below,comment and share pls.love u all💋

Jasko 💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣4⃣

    Ahmad ya kasa cewa komai yana kallonsu,Reyhana wani kallon tara saura tayi mata tun daga sama har 'kasa sannan ta 'karasa bakin 'kofar ta bud'e ta shige cikeda ta'kama.

     Zainab baki ta saki taga 'karfa-'karfa,chak ta tsaya batada alamar shiga motar.

     Ahmad ne yai mata alama ta shiga baya lokacin da suka had'a ido ,seda taci 1min tukun ta shiga baya ta ra'be gefe haushi ya isheta.

    Shiru kowa yayi a ransu kowa da sa'ke-sa'ken da yake. A haka har aka 'karasa gidansu Reyhana ,yana parking ta fito daga motar ko takan Nasreen bata bi ba tasan dole ze d'akkota kuma da biyu tayi hakan dan ta sake ba'kanta wa Zainab.

       Bayan ya fito ya bud'e gidan baya ya d'akko ta ,tayi nisa ma da bacci.

      Zainab lokacin da taga yana fitowa daga gidan ta kauda kanta ta sake had'e rai,tunda ya shigo motar ya fiskanci hakan.

      "Ki dawo nan gaba". Ya fad'a.

       Yitai kamar bata ji ba seda ya sake maimaitawa tace.

        " A'a nan ma yayi".Ta fad'a muryarta ciki-ciki.

        "Zainab ki dawo nace".Ya fad'a wannan karan ya waiwayo.

        Bata sake cewa komai ba ta fita ta koma gaba tare da rufo 'kofar da 'karfi.

       " Fishi kike da Antyn taki?" Ahmad ya fad'a bayan ta shigo.

       "Anty ta". Ta maimaita tare da ta'be baki.

       "Ehmana ko kin mata ita Antynki ce?"

        Shiru tayi bata sake wata maganar ba tana kallon waje har suka  isa gida.

     Tunda suka shiga gida ta shige d'akinta takaici ya isheta.

                  ***

      Reyhana bayan tafiyarsa ta kai Nasreen d'aki ta kwantar da ita,tunani ta shiga yi na abinda ya faru,murmushi ta tsinci kanta tana yi ."Ko zata koma gaban oho mata".Ta fad'a a zuciyarta.

       Tana wannan batun sega kiran Ahmad ya shigo wayarta,yau a karan farko tayi picking.

      "Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

       " Waalaikumussalam"Ya fad'a.

        "Ya jikin nata?" Ya tambaya.

         "Da sau'ki har yanzu bacci take". Ta fad'a.

          "Ok,toh idan ta tashi karki manta ki bata magani".Ya fad'a.

          " You don't have to mention dan bazan manta ba".Reyhana ta fad'a cikin sanyin murya.

      "Kina so kice kin fini damuwa da ita kenan" Ahmad ya fad'a.

       "Toh wa zai had'a ma". Cewar Reyhana.

        " Haka de kika ce ,itama ai ta sani".Ya fad'a.

        "Cabb! Waya fad'a ma nide kullum kodayaushe muna tare ko bacci baya raba mu".

      "Kwana nawa ne zan d'auke ta". Ahmad ya fad'a.

      " Ba inda zata".Reyhana ta fad'a.

       "In kina so ki zauna tare da ita seki biyo ta". Ya fad'a.

       "Hmm".

       " Hmm meh?"Ya tambaya.

        "Babu ,am hanging now". Ta fad'a.

       "So kike ki wayance de ,shikenan toh goodnight". Ya fad'a.

        " Ok ,ka gaida Umma". Ta fad'a.

         "Kinyi mantuwa". Ya fad'a.

          " Name fa?" Ta tambaya tana neman bayani.

          "Baki ce kina gaida Zainab ba". Ya fad'a.

           " Goodnight ". Ta fad'a tare da katse wayar.

      Hakan yasa shin yin dariya ,text ya tura mata tukun ya ajje wayar gefe.
Chapter 31 · 0% Book details