Sashe 15
Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Ahmad na gama maganar nan bazan chanja ra'ayina ba,kaje ka sake tunani".Mommy ta fad'a tare da barin parlorn.
Ahmad ai zama yayi dirshan hawaye na ziba a fuskarsa ya rasa inda ze saka kansa.Wayarsa ya lalubo a aljihu yai dialing number ta Reyhana.
Ya kirata yafi a 'kirga amma bata d'aga ba,koba a fad'a ba yasan tana cikin wani hali yanzune ya gano dalilin dayasa bata maganar komowarsu sede kullum shi yayi mata.
Mommy kuwa tana hayewa sama d'akinta ta shige ita kanta ta tausaya masu amma ba ta jin zata iya 'kyalesu haka.
Reyhana kuwa tana ganin wayarsa amma ta kasa picking dan tuni tasan aikin gama ya gama,batasan mey zata ce dashi ba.
Ya shafe yafi 30min kafin ya fita daga gidansu Reyhana jiyake kamar yaje d'akin da Reyhana take,haka da'kyar ya iya tafiya direct gidan Umma ya wuce.
Umma ta tsorata ganin yanayinsa ,kuka yasa mata a tsakar parlour kamar d'an yaro ,ta 'kosa taji abinda ya faru ita ta zaci ko wani abunne ya sami Reyhana ko Nasreen.
"Ahmad kukan ya isa nace, ka fad'a mini mey yake faruwa se kayita kuka". Umma ta fad'a.
" UMMA Reyhana,bazan iya rabuwa da ita ba".Ya fad'a cikin kuka.
"Reyhana? Wa yace zaka rabu da ita?" Ta tamabaya a kid'ime.
"Mommy ce Umma ,bazan iya ba Umma dan Allah kije ki bata ha'kuri". Ahmad ya fad'a.
Umma ita kanta batasan sanda hawaye ya zubo a fuskarta ba,take tausayin d'anta ya 'karu a zuciyarta.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'u". Abinda ta furta kenan.
" Ita Mommy da kanta tace ka rabu da 'yarta?" Ta tamabaya.
"Mommy wai na saki Reyhana taya zan iya rabuwa dasu Umma ?"
Umma dafe kanta tayi ta rasa mey yake mata dad'i.An d'an tsahon lokaci a haka ,Ahmad ya bar sheshe'kar kukan sede hawaye gashi idanuwansa yayi ja jijiyoyinsa ma sun tashi fuskarsa tayi jazir.
"Kayi ha'kuri in Allah ya yarda baza ka rabu da ita ba ,addu'a zakai". Umma ta fad'a.
Duba da lokacin yasa bata tafi gidan ba ,8pm tayi.
Gidansu Reyhana kuwa shiru kukeji kowa yana d'aki dan koda Abba ya dawo Sageer ya zayyane wa Abba komai dan yana jiyo Mommy da Ahmad.
Abba ransa a 'bace ya shiga d'akinsa jira yake gobe tayi ya shawo kan matsalar(Hmm😶).
Reyhana da dare yayi ko bacci ta kasa gashi Nasser tana ta mata kuka koh cikinta yake ciwo ,ita kad'ai take ta lallashinta amma ta'ki shiru hakan yasa itama Reyhana ta taya ta sukaita kuka bame rarrashin kowa.
Ahmad ko gidansa be koma ba yana parlourn Umma sallah yayi koh abinci ya'ki ci tunanin Reyhana da Nasreen kawai yake.
***
Washegari da safe Umma tun asubah bata koma ba ,shiko Ahmad dama jiya beyi wani bacci ba sallah yayi yaita adduo',ise around 4:30am bacci yai gaba dashi.
Tun bayan sallahr Asubah be koma ba dukda kuwa baccine a idanuwansa.
Umma around 8am ta tafi gidansu Reyhana dan hankalinta ya kasa kwanciya,inno ce tayi mata iso.Nan inno taje ta sanarwa da Mommy ,ba dad'ewa ta sakko 'kasa.
Sama-sama ta gaisa da Umma dama tasan meke tafe da ita.
"Mommyn Reyhana meyai zafi haka...". Ko 'kare maganar batayi ba Mommy ta katseta.
" Duk wani abu da zan fad'a na riga na fad'a wa Ahmad saboda haka banga amfanin dawo da zance baya ba".Cewar Mommy ba ko damuwa a tare da ita.
"Ehyi nasan da haka amma dan Allah ki tausayawa yaranannan ki bashi dama ,Ahmad rabuwa da Reyhana matsala ne a gunsa abune me wuya". Umma ta fad'a cikeda tausayawa.
" Itama Reyhana zama dashi abune mey wuya a gunta damu kanmu baza muso ta shiga 'kuncin rayuwa ba".Mommy ta fad'a.
"Dan Allah kiyi ha'kuri ki bar maganar nan". Umma ta fad'a.
Mommy ta 'kosa sosai dan ta fara kad'a 'kafa komai ze iya fitowa daga bakinta.
" Nifa yanzu takardarta nake jira bana san sake jin komai".Mommy ta fad'a.
"Baze sake tan ba".Abba ya fad'a.
Dama ya gano sanda Umma ta shigo gidan a d'akinsa.
" Kiyi ha'kuri Umman Ahmad inshAllahu ma yau zan maido da ita gidanta da kaina.Abba ya fad'a.
"Ba inda zata je, ta gama zaman gidan Ahmad". Mommy ta fad'a.
Umma da take zaune ta mi'ke tsaye taga abun ba na zama bane.
Itako already Mommy tun sakkowar Abba ta mi'ke tsaye.
Ikram datake shirin sakkowa ta hangi abinda ke faruwa dan haka ta shiga d'akin Reyhana da sauri ta fad'a mata.
" Yaya Umman Ahmad tazo ,kinga Abba ma ya fito suna magana Mommy kuma...".Bata 'karasa ba tayi shiru.
Reyhana ko bata fad'a ba ta gano inda ta nufa,da sauri ta tashi zuwa parlour.
Daga can gefen bene suka tsaya itada Ikram suna kallon ikon Allah.
"Ni na fad'a a yau seta koma gidanta". Abba ya fad'a cikin d'aga murya.
" Ba inda zata je".Cewar Mommy.
"Dan Allah ayi ha'kuri". Umma ta fad'a.
Da ace tasan hakan abin ze kaya da bata zo ba,dan haka tayi ta basu ha'kuri.Suna kallo ta fita daga gidan,su kuwa basu fasa ba.
" Ke kike da iko da ita koh ni?"Abba ya fad'a.
"Bani bace,kayi yanda kake so kaji". Mommy ta fad'a cikin fushi.
" Kece kuwa ? ".Abba ya tamabaya .
Yana mamakin yadda ta sauya ,yasanta da zafi amma ba irin haka ba ace yau har a gaban sirika yana fad'a tana fad'a.
Yana cikin wannan batun Mommy tayi wucewarta ta haye sama yaran suna kallo.Sageer da se lokacin ya fito daga d'akin ,wajen Abba Reyhana ta 'karasa tana basa ha'kuri ,ba abinda yake illa jinjina kai.
" Mommy ina zaki je?" Suka jiyo muryar Walida da ta biyo bayan Mommy.Wani irin shock gabaki d'ayansu suka ji ganin Mommy tana sakkowa da trolley.
Ta yafa gyale ga takalmi data saka hannunta key na motarta,hakan ya bayyana tafiya zatai.
"Mommy?" Reyhana ta furta cikeda mamaki.
Har gabansa ta 'karaso ba tare da ta kalli yaran ba tace."Sanda kaga bana nan seka tabbata nice,ga yaranka kaine kake da iko dasu".Mommy ta fad'a fuuu ta wuce.
AR²💖
Jasko💕
Pls share.
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 1⃣6⃣
Gabaki d'aya yaran da sauri suka 'karasa wajen Mommy da ta kusa kaiwa 'kofar fita.
"Mommy dan Allah karki tafi ki barmu". Walida ta fad'a tana ta'be baki zatai kuka.
" Mommy please kar kiyi haka".Reyhana ta fad'a ta ri'ko hannun Mommy.
Se lokacin ta kalleta ,Sageer ma 'karasowa yayi.
Mommy dan Allah ".Ya fad'a muryarsa a raunane.
" Sakeni".Mommy ta fad'a tana mata wani kallo.
Reyhana a hankali ta sauke hannunta dan tasan duk dalilinta hakan ta fara.
Suna ji suna kallo ta fita ,Walida take ta buga 'kafa tana ta kuka tana kiran Mommy.
Abba da tun d'azu be kalli inda take ba duk da kuwa abun ya damesa sosai ,seda yaga ta fita ga Walida tana kuka.Fita yayi ,yaran zasu biyosa yace su tsaya.
"Maryam". Abba ya kira sunanta.
Yana 'karasawa inda take ya fisge trolley d'in daga hannunta.
" Mey kike tunanin yi? Idan kin tafi ina zaki je"?" Ya tamabaya.
"Gidan kawu na". Ta amsa.
" Ki shiga ciki nace".Abba ya fad'a yana nuni da 'kofa.
"Kusha zaman ku kaida yaranka muddin baze saketa ba ni kuma bazan dawo gidannan ba". Ta fad'a.
" Adalci kenan ,ki raba auren yarannan?"
Shiru tayi bata ce komai ba tana tsaye ita bata shiga motar ba kuma bata koma ba.
"Ki duba kiga yarannan,haka zaki tafi ki barsu wani hali zasi shiga? Abba ya fad'a a sanyaye.
" Nide na fad'a maka muddin na koma toh seya saketa".Mommy ta fad'a.
"Muje ki shiga ciki". Abba ya fad'a.
Tana huci tabi bayansa yaran suna kallo ta shigo da sauri suka je wajenta.
Reyhana kuwa komawa tayi d'aki jiki a sanyaye. A zuciyarta tana tunanin mafita " Yanzu a kaina yau Mommy take 'ko'karin barin gidannan!" Reyhana ta fad'a a zuciyarta hawaye na gangarowa a idanuwanta.
***
Umma tana komawa gida Ahmad ya 'karaso inda take.
"Umma ta ha'kura Mommyn" .Ya tambaya muryarsa a raunane.
Kallonsa kawai tayi amma ta kasa cewa komai.
"Umma ki fad'a min". Ya fad'a.
" Ahmad sede mu cigaba da addu'a ,Mommyn ta ta'ki amincewa mahaifinta ne de ya goyi bayanta ba". Umma ta fad'a.
Labarin duk abunda ya faru ta zayyane masa,hannu yasa ya dafe goshi kansa yana sarawa.
"Ha'kuri zakai Ahmad duk abinda kaga ya faru Allah ne ya tsara". Umma ta fad'a.
Seda tayi da gaske yaci abinci kad'an koh fita ya 'kiyi,wayarsa ya d'auka bayan yayi sallahr zuhr yayi dialing number na Reyhana.
Seda ta kusa katsewa tayi picking.
" Reyhana ".Ya kira sunanta.
" Uhmm".Ta amsa dan idan tayi 'kwakkwarar magana kuka zatai.
"Reyhana dan Allah karki rabu dani ,bazan iya zama bake ba ina 'kaunarki Reyhana". Ya fad'a muryarsa na rawa.
Jin haka yasa ta shiga kukan da take dannewa." Ahmad taya zanso na barka kaima kasan bazan so na rabu da kai ba".Ta fad'a.
"I know Reyhana". Ya fad'a.
" Yaya ina tsoro".Ta fad'a.
"Reyhana inshaAllah muna tare". Ya fad'a duk da kuwa zuciyarsa ta karaya.
Labarin abunda ya faru bayan tafiyar Umma ta basa, hakan ba 'karamin tsorata sa yayi ba.
" Yaya bazan iya bari Mommy ta bar Abba a dalilina ba".Ta fad'a.
Kai kawai ya kad'a kamar yana kusa da ita,sun d'au lokaci kafin Ahmad ya sake magana.
"I love you so much that I can't afford lose you Azizaty".Ya fad'a.
" Idan na rabu dake ya zami da Nasreen ? Reyhana I can't do this".Ya fad'a zuciyarsa na sake karaya.
Kud'in wayar ne da suka 'kare yasa basu cigaba da magana ba ,Reyhana wani sabon kukan ta soma yi Allah yasa Nasreen bacci take.
Kowa rayuwar ta'ki masa dad'i ,dukansu sun shiga damuwa gashi idan yaje gidan baya samun ganinta yanzu Mommy ma wayar ma so take ta hana su kuma.Reyhana jikinta yayi sanyi dan bata jin zata iya bari a dalilinta Mommy tabar gidan dan haka yanzu tana ganin zatace wa Ahmad ya bata takardarta muddin hakan ze dawo da faruncikin Mommy.Dan yanzu Mommy bata wani sakkowa 'kasa idan kuwa Abba yana parlour bata zama.
Ahmad koya kira Mommy ya sake ro'konta bata picking call d'insa sede yayi ta tura mata text amma kamar bayi yake ba.
Ahmad ai zama yayi dirshan hawaye na ziba a fuskarsa ya rasa inda ze saka kansa.Wayarsa ya lalubo a aljihu yai dialing number ta Reyhana.
Ya kirata yafi a 'kirga amma bata d'aga ba,koba a fad'a ba yasan tana cikin wani hali yanzune ya gano dalilin dayasa bata maganar komowarsu sede kullum shi yayi mata.
Mommy kuwa tana hayewa sama d'akinta ta shige ita kanta ta tausaya masu amma ba ta jin zata iya 'kyalesu haka.
Reyhana kuwa tana ganin wayarsa amma ta kasa picking dan tuni tasan aikin gama ya gama,batasan mey zata ce dashi ba.
Ya shafe yafi 30min kafin ya fita daga gidansu Reyhana jiyake kamar yaje d'akin da Reyhana take,haka da'kyar ya iya tafiya direct gidan Umma ya wuce.
Umma ta tsorata ganin yanayinsa ,kuka yasa mata a tsakar parlour kamar d'an yaro ,ta 'kosa taji abinda ya faru ita ta zaci ko wani abunne ya sami Reyhana ko Nasreen.
"Ahmad kukan ya isa nace, ka fad'a mini mey yake faruwa se kayita kuka". Umma ta fad'a.
" UMMA Reyhana,bazan iya rabuwa da ita ba".Ya fad'a cikin kuka.
"Reyhana? Wa yace zaka rabu da ita?" Ta tamabaya a kid'ime.
"Mommy ce Umma ,bazan iya ba Umma dan Allah kije ki bata ha'kuri". Ahmad ya fad'a.
Umma ita kanta batasan sanda hawaye ya zubo a fuskarta ba,take tausayin d'anta ya 'karu a zuciyarta.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'u". Abinda ta furta kenan.
" Ita Mommy da kanta tace ka rabu da 'yarta?" Ta tamabaya.
"Mommy wai na saki Reyhana taya zan iya rabuwa dasu Umma ?"
Umma dafe kanta tayi ta rasa mey yake mata dad'i.An d'an tsahon lokaci a haka ,Ahmad ya bar sheshe'kar kukan sede hawaye gashi idanuwansa yayi ja jijiyoyinsa ma sun tashi fuskarsa tayi jazir.
"Kayi ha'kuri in Allah ya yarda baza ka rabu da ita ba ,addu'a zakai". Umma ta fad'a.
Duba da lokacin yasa bata tafi gidan ba ,8pm tayi.
Gidansu Reyhana kuwa shiru kukeji kowa yana d'aki dan koda Abba ya dawo Sageer ya zayyane wa Abba komai dan yana jiyo Mommy da Ahmad.
Abba ransa a 'bace ya shiga d'akinsa jira yake gobe tayi ya shawo kan matsalar(Hmm😶).
Reyhana da dare yayi ko bacci ta kasa gashi Nasser tana ta mata kuka koh cikinta yake ciwo ,ita kad'ai take ta lallashinta amma ta'ki shiru hakan yasa itama Reyhana ta taya ta sukaita kuka bame rarrashin kowa.
Ahmad ko gidansa be koma ba yana parlourn Umma sallah yayi koh abinci ya'ki ci tunanin Reyhana da Nasreen kawai yake.
***
Washegari da safe Umma tun asubah bata koma ba ,shiko Ahmad dama jiya beyi wani bacci ba sallah yayi yaita adduo',ise around 4:30am bacci yai gaba dashi.
Tun bayan sallahr Asubah be koma ba dukda kuwa baccine a idanuwansa.
Umma around 8am ta tafi gidansu Reyhana dan hankalinta ya kasa kwanciya,inno ce tayi mata iso.Nan inno taje ta sanarwa da Mommy ,ba dad'ewa ta sakko 'kasa.
Sama-sama ta gaisa da Umma dama tasan meke tafe da ita.
"Mommyn Reyhana meyai zafi haka...". Ko 'kare maganar batayi ba Mommy ta katseta.
" Duk wani abu da zan fad'a na riga na fad'a wa Ahmad saboda haka banga amfanin dawo da zance baya ba".Cewar Mommy ba ko damuwa a tare da ita.
"Ehyi nasan da haka amma dan Allah ki tausayawa yaranannan ki bashi dama ,Ahmad rabuwa da Reyhana matsala ne a gunsa abune me wuya". Umma ta fad'a cikeda tausayawa.
" Itama Reyhana zama dashi abune mey wuya a gunta damu kanmu baza muso ta shiga 'kuncin rayuwa ba".Mommy ta fad'a.
"Dan Allah kiyi ha'kuri ki bar maganar nan". Umma ta fad'a.
Mommy ta 'kosa sosai dan ta fara kad'a 'kafa komai ze iya fitowa daga bakinta.
" Nifa yanzu takardarta nake jira bana san sake jin komai".Mommy ta fad'a.
"Baze sake tan ba".Abba ya fad'a.
Dama ya gano sanda Umma ta shigo gidan a d'akinsa.
" Kiyi ha'kuri Umman Ahmad inshAllahu ma yau zan maido da ita gidanta da kaina.Abba ya fad'a.
"Ba inda zata je, ta gama zaman gidan Ahmad". Mommy ta fad'a.
Umma da take zaune ta mi'ke tsaye taga abun ba na zama bane.
Itako already Mommy tun sakkowar Abba ta mi'ke tsaye.
Ikram datake shirin sakkowa ta hangi abinda ke faruwa dan haka ta shiga d'akin Reyhana da sauri ta fad'a mata.
" Yaya Umman Ahmad tazo ,kinga Abba ma ya fito suna magana Mommy kuma...".Bata 'karasa ba tayi shiru.
Reyhana ko bata fad'a ba ta gano inda ta nufa,da sauri ta tashi zuwa parlour.
Daga can gefen bene suka tsaya itada Ikram suna kallon ikon Allah.
"Ni na fad'a a yau seta koma gidanta". Abba ya fad'a cikin d'aga murya.
" Ba inda zata je".Cewar Mommy.
"Dan Allah ayi ha'kuri". Umma ta fad'a.
Da ace tasan hakan abin ze kaya da bata zo ba,dan haka tayi ta basu ha'kuri.Suna kallo ta fita daga gidan,su kuwa basu fasa ba.
" Ke kike da iko da ita koh ni?"Abba ya fad'a.
"Bani bace,kayi yanda kake so kaji". Mommy ta fad'a cikin fushi.
" Kece kuwa ? ".Abba ya tamabaya .
Yana mamakin yadda ta sauya ,yasanta da zafi amma ba irin haka ba ace yau har a gaban sirika yana fad'a tana fad'a.
Yana cikin wannan batun Mommy tayi wucewarta ta haye sama yaran suna kallo.Sageer da se lokacin ya fito daga d'akin ,wajen Abba Reyhana ta 'karasa tana basa ha'kuri ,ba abinda yake illa jinjina kai.
" Mommy ina zaki je?" Suka jiyo muryar Walida da ta biyo bayan Mommy.Wani irin shock gabaki d'ayansu suka ji ganin Mommy tana sakkowa da trolley.
Ta yafa gyale ga takalmi data saka hannunta key na motarta,hakan ya bayyana tafiya zatai.
"Mommy?" Reyhana ta furta cikeda mamaki.
Har gabansa ta 'karaso ba tare da ta kalli yaran ba tace."Sanda kaga bana nan seka tabbata nice,ga yaranka kaine kake da iko dasu".Mommy ta fad'a fuuu ta wuce.
AR²💖
Jasko💕
Pls share.
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 1⃣6⃣
Gabaki d'aya yaran da sauri suka 'karasa wajen Mommy da ta kusa kaiwa 'kofar fita.
"Mommy dan Allah karki tafi ki barmu". Walida ta fad'a tana ta'be baki zatai kuka.
" Mommy please kar kiyi haka".Reyhana ta fad'a ta ri'ko hannun Mommy.
Se lokacin ta kalleta ,Sageer ma 'karasowa yayi.
Mommy dan Allah ".Ya fad'a muryarsa a raunane.
" Sakeni".Mommy ta fad'a tana mata wani kallo.
Reyhana a hankali ta sauke hannunta dan tasan duk dalilinta hakan ta fara.
Suna ji suna kallo ta fita ,Walida take ta buga 'kafa tana ta kuka tana kiran Mommy.
Abba da tun d'azu be kalli inda take ba duk da kuwa abun ya damesa sosai ,seda yaga ta fita ga Walida tana kuka.Fita yayi ,yaran zasu biyosa yace su tsaya.
"Maryam". Abba ya kira sunanta.
Yana 'karasawa inda take ya fisge trolley d'in daga hannunta.
" Mey kike tunanin yi? Idan kin tafi ina zaki je"?" Ya tamabaya.
"Gidan kawu na". Ta amsa.
" Ki shiga ciki nace".Abba ya fad'a yana nuni da 'kofa.
"Kusha zaman ku kaida yaranka muddin baze saketa ba ni kuma bazan dawo gidannan ba". Ta fad'a.
" Adalci kenan ,ki raba auren yarannan?"
Shiru tayi bata ce komai ba tana tsaye ita bata shiga motar ba kuma bata koma ba.
"Ki duba kiga yarannan,haka zaki tafi ki barsu wani hali zasi shiga? Abba ya fad'a a sanyaye.
" Nide na fad'a maka muddin na koma toh seya saketa".Mommy ta fad'a.
"Muje ki shiga ciki". Abba ya fad'a.
Tana huci tabi bayansa yaran suna kallo ta shigo da sauri suka je wajenta.
Reyhana kuwa komawa tayi d'aki jiki a sanyaye. A zuciyarta tana tunanin mafita " Yanzu a kaina yau Mommy take 'ko'karin barin gidannan!" Reyhana ta fad'a a zuciyarta hawaye na gangarowa a idanuwanta.
***
Umma tana komawa gida Ahmad ya 'karaso inda take.
"Umma ta ha'kura Mommyn" .Ya tambaya muryarsa a raunane.
Kallonsa kawai tayi amma ta kasa cewa komai.
"Umma ki fad'a min". Ya fad'a.
" Ahmad sede mu cigaba da addu'a ,Mommyn ta ta'ki amincewa mahaifinta ne de ya goyi bayanta ba". Umma ta fad'a.
Labarin duk abunda ya faru ta zayyane masa,hannu yasa ya dafe goshi kansa yana sarawa.
"Ha'kuri zakai Ahmad duk abinda kaga ya faru Allah ne ya tsara". Umma ta fad'a.
Seda tayi da gaske yaci abinci kad'an koh fita ya 'kiyi,wayarsa ya d'auka bayan yayi sallahr zuhr yayi dialing number na Reyhana.
Seda ta kusa katsewa tayi picking.
" Reyhana ".Ya kira sunanta.
" Uhmm".Ta amsa dan idan tayi 'kwakkwarar magana kuka zatai.
"Reyhana dan Allah karki rabu dani ,bazan iya zama bake ba ina 'kaunarki Reyhana". Ya fad'a muryarsa na rawa.
Jin haka yasa ta shiga kukan da take dannewa." Ahmad taya zanso na barka kaima kasan bazan so na rabu da kai ba".Ta fad'a.
"I know Reyhana". Ya fad'a.
" Yaya ina tsoro".Ta fad'a.
"Reyhana inshaAllah muna tare". Ya fad'a duk da kuwa zuciyarsa ta karaya.
Labarin abunda ya faru bayan tafiyar Umma ta basa, hakan ba 'karamin tsorata sa yayi ba.
" Yaya bazan iya bari Mommy ta bar Abba a dalilina ba".Ta fad'a.
Kai kawai ya kad'a kamar yana kusa da ita,sun d'au lokaci kafin Ahmad ya sake magana.
"I love you so much that I can't afford lose you Azizaty".Ya fad'a.
" Idan na rabu dake ya zami da Nasreen ? Reyhana I can't do this".Ya fad'a zuciyarsa na sake karaya.
Kud'in wayar ne da suka 'kare yasa basu cigaba da magana ba ,Reyhana wani sabon kukan ta soma yi Allah yasa Nasreen bacci take.
Kowa rayuwar ta'ki masa dad'i ,dukansu sun shiga damuwa gashi idan yaje gidan baya samun ganinta yanzu Mommy ma wayar ma so take ta hana su kuma.Reyhana jikinta yayi sanyi dan bata jin zata iya bari a dalilinta Mommy tabar gidan dan haka yanzu tana ganin zatace wa Ahmad ya bata takardarta muddin hakan ze dawo da faruncikin Mommy.Dan yanzu Mommy bata wani sakkowa 'kasa idan kuwa Abba yana parlour bata zama.
Ahmad koya kira Mommy ya sake ro'konta bata picking call d'insa sede yayi ta tura mata text amma kamar bayi yake ba.