← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 33

Sashe 13

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

          " Toh yanzu de kiyi wa Mommy magana zan tafi se miyi sallama".Ahmad ya fad'a.

       "Toh". Ta amsa.

        Tana gama wayar ne ma sega Mommy ta shigo.

      " Mommy ga Ahmad ze tafi yace zakuyi sallama"Reyhana ta fad'a.

     "Uhm waya kukayi kenan". Mommy ta fad'a tare da ta'be baki.

      " Yaran yanzu baku da zuciya".Mommy ta fad'a.

      "Mommy kuka fa take shine naje kar'barta".Cewar Reyhana.

      "Rabu dani ". Mommy ta fad'a.

      Daga haka ta fita sukai sallama dashi.Wajen aiki ya wuce se wajen 4pm ya tashi kafin yaje gidan umma ya tsaya a store yayi wa Reyhana 'yan siyayyan mey jego dede halin sa.

               ***
   Around 6:40pm suka je gidan su Reyhana,har da'ki Mommy tayi mata iso shima Ahmad d'in tare da ita ya shigo.

        Bayan sun gaggaisa Mommy ta fita ,Reyhana ce ta rage a d'akin sesu Umma.

       "Umma Reyhana ta miki ta'kwara fah". Ahmad ya fad'a.

      " Toh!  mashaAllah an gode Allah, Allah ya raya mana AISHA".

       "Ameen ". Suka amsa.

      Suna zaune Abba ya dawo shima ya shigo suka gaisa dasu,lokacin da zasu tafi ya ajje kayan da ya siyo.

        A waje Ahmad ya ke'be da Abba ya bashi ha'kuri akan abinda ya faru Abba yace komai ya wuce.

        Mommy bayan sun tafi da ta shigo taga kayan kawai ta'be baki tayi bata ce komai ba.

        Se lokacin Reyhana ta samu tayi wanka akaiwa baby ma ,nan su Ikram sukai ta rangad'a mata pic iri-iri.

          Kusan kullum Ahmad seya zo ya dubasu idan ya tashi daga aiki,a haka kwanaki suka ja har ranar suna tazo.

        Anyi shirye-shirye sosai komai Mommy sun tanada Ahmad ya aiko da ragon suna aka yanka yarinya taci suna AISHA Mommy taji ba dad'i sede bata nuna ba.

      Nasreen za'a ke kiranta dashi,tasha ado daga ita har mey jego Reyhana  swiss lace purple me white torches tasa se necklace silver Ikram ta rangad'a mata d'auri sekace amarya.

      Ansha hotuna 'yan uwa da abokan arz'iki sun hallara,Ahmad da yamma shida abokansa uku suka zo se Umma da wasu sisters daga zaria.

       Reyhana dama ta tanadar musu abinci da sauran lemuna ta ajje dan haka da suka zo ta basu,sukai hotuna suma.

       Bayan an watse daga Nasreen har Reyhana sun gaji sosai ana wa Nasreen wanka tayi bacci Reyhana ma wannan tayi tasha tea ta kwanta.

       *Nima pen d'ina na ajje na kwanta😀*

AR²💖

    Please share...

Jasko💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣3⃣

  Washegari gajiyar da dama-dama sede Nasreen tasha bacci dan har lokacin bata farka ba.

      Har tayi wanka tayi breakfast Nasreen bata tashi ba,koda ta duba wayarta taga missed call na Ahmad ya kira tana bacci dan haka tayi calling ba.

      Kira d'aya tayi masa yayi picking.

       "Ummu Nasreen". Ahmad ya kira.

       "Abu Nasreen". Reyhana ta fad'a itama.

       " Ina kwana ".Ta gaisheshi.

       " Lafiya lao Azizaty,ya gajiyarku?"Ahmad ya amsa.

      "Gajiya ansha ta,har yanzu bacci take". Ta fad'a.

      "Allah sarki babyna du mutane sun wahalar min da ita".Ahmad ya fad'a.

      " Sannu mey baby".Reyhana ta fad'a cikin zolaya.

      "Ha! Toh ai gaskiya na fad'a". Cewar Ahmad yana dariya.

      " Toh nikuma fa banfita gajiya ba?" Reyhana ta fad'a.

     "Iyye! Kishi" Ahmad ya fad'a.

      "Haba kinsan da ina kusa da nayi maki tausa".Ahmad ya fad'a.

      " Nayi missing Azizaty ta ,your cooking pretty face everything yours Ummu Nasreen ".

      " Me too".Reyhana ta fad'a.

      "Toh yanzu kayi breakfast?" Ta tambaya.

      "Tea kawai nasha,yanzu zan fita ma". Ahmad ya fad'a.

      " Please ka samu kaci wani abun ko a wajen aikin ne".Cewar Reyhana tana mey nuna damuwa.

      "Ok Azizaty i will". Ya fad'a.

      " Toh bari na barka ka shirya".Ta fad'a.

      "Ok ki shafamin kan babyna i love you all". Ya fad'a.

     " Love you too,Allah ya kare mana kai".

     "Ameen". Ya amsa.

     Daga haka sukai sallama kowannensu fuskarsa d'auke da murmushi cikin ransu suna 'kara jin son junansu".

      Ba jimawa Nasreen ta tashi ,da kuka ta farka dan yunwa da take ji.Ta ded'e tana shan nono tukun aka yi mata wanka.

        Komai ya cigaba da gudana, Nasreen har bayan suna ana zuwa barka ga kayan gudumawa da ake bawa Reyhana yarinyar tayi goshi sosai banda kayan da Abba ya 'karo mata akan wanda su Umma suka kawo na barka.

        Ikram idan suna gida itace me d'aukan Nasreen Reyhana hutawarta take ,yarinyar ana ji da ita a gidannan Ahmad ma yana yawan zuwa baya kwana uku beje ba.

        Umma ma tana yawan kiransu su gaisa taji ya ta'kwararta.

      3weeks later,Ahmad yana ta irga musu kwanakinsu bashida buri su cika kwana 40 su dawo baya jin dad'in gidan kusan koyaushe yana unguwarsu wajen abokansa.

                  ***
      Mommy yau tai shirinta na zuwa gidan Anty Asma'u dan tunda Reyhana ta haihu bata samu ta fita ba.

         " Mommy dan Allah ku dawo da wuri saboda wankan Nasreen".Reyhana ta fad'a.

      "Yau ke zaki mata da kanki ai gara ki koya". Mommy ta fad'a.

       " Cabb! Kina so nasa mata sabulu a hanci". Reyhana ta fad'a.

      "Gaki gata kika samata kyasan yadda kikai". Mommy ta fad'a.

      Walida da tun tuni ta gama shiryawa Mommy take jira kawai su tafi.

        " lala Yaya baby Nasreen tayi pupu".Walida ta fad'a tana toshe hanci.

       "Ga babarta ta wanke mata danni na gama nawa". Mommy ta fad'a.

       " Kai Mommy nifa ban iya ba".Reyhana ta fad'a.

      "Zaki iya ne, ga inno can kice ta cire mata danni nayi nan,Walida taho mi tafi". Mommy ta fad'a tana sa'kala Jakarta.

      " Se kun dawo".Ta fad'a.

       "Muhmm! Me d'oyin kashi". Reyhana ta fad'a lokacinda  Nasreen ta kalleta.

       Haka nan ta tashi ta cire mata tana yi tana toshe hanci.

                  ***

      Mommy a d'an 'kan'kanin lokaci ta isa gidan Anty Asma'un.

        Suna parlour ita da yaranta." Oyoyo Walida".Anty ta fad'a tare da nufo inda suke.

       Walida tana gaisheta ta nufi inda Ameera take,kusan itace sa'arta sukuwa Mommy suka tafi d'aki.

        "Ya masu jego ?"Anty ta tambaya.

        " Mey jego tana nan qalau ita da baby".Mommy ta amsa.

        "Saura 'yan satittika su koma koh?" Cewar Anty.

        "Hmm!" Mommy ta furta .

         "Ya hmm! da wani abune?" Anty ta tambaya tana neman 'karin bayani.

        "Kusan de". Cewar Mommy.

        " Mey fah?" Anty ta tambaya.

        "Nifa ba maganar komawa da yarinyar nan zatai". Mommy ta fad'a.

        " Toh! dalili?" Ta tambaya.

         "Nifa bazan yarda da irin wannan rayuwar ba ta gidan Ahmad Reyhana ba class d'insa bace ki duba kiga nauyi ya 'karu a kansa idan da yana kula da mace d'aya toh yanzu ga nauyin babynnan abin is not easy". Mommy ta fad'a.

       " Amma fa kin matsa dayawa kina tunanin Abbanta ze bar faruwar hakan?"Cewar Anty Asma'u.

       "Barni dashi nasan ta inda zan 'bullo masa". Mommy ta fad'a.

       "Su kuma ya zaki dasu?" Anty ta tambaya.

        "Wannan bame wuya bane Reyhana ba kamar Ikram take ba,taimakon rayuwarta zanyi ita bata san kanta ba ita so ya rufe mata ido bazan zuba ido ta sake samun cikin na biyu ba gara tun wuri na dakatar dama rabon 'yace ya had'asu".Mommy ta fad'a.

      "Maryam kenan ,toh Allah ya saww'ake deh". Anty ta fad'a.

       " Yanzu Toh yaushe zaki fad'a ma Reyhana d'in?" Ta tambaya.

     "Nan bada jimawa ba". Mommy ta fad'a.

       Daga nan suka tsindima wata hirar ta daban.

        Reyhana kuwa a gida tana ta fama da Nasreen dan ta'ki komawa bacci gashi ta barta a d'aki ita d'ai tasa ihu Ikram bata dawo ba balle ta taya ta ,inno kuma ta fita.

        Ahmad daga wajen aiki ya tashi da wuri,wajen 4pm yazo gidansu Reyhana. Har lokacin Mommy bata dawo ba ,kiranta yayi a waya ya fad'a mata yana haraba tace ya shigo.

       A parlour ya zauna chan ba dad'ewa ta fito Nasreen a hannunta.

       Murmushi ya sakar mata me 'kayatarwa itama ta mayar masa,be jira ta zauna ba ya mi'ke domin kar'bar Nasreen.

            " Ummu Nasreen irin wannan kyau haka".Ahmad ya fad'a.

       Kuma powder ne da lipstick kawai ko kwalli bata sa ba,tayi kyau sosai cikin green d'in atamfar.

       "Babyna ta gane ni kinga tana mini murmushi". Ahmad ya fad'a yana 'ko'karin zama.

      Itama Reyhana zama tayi a kujerar dayake three seater ce.

       " Watoh har ta fara gane ka?"Cewar Reyhana.

      "Ehmana baki gani ba taga mey kama da ita". Ya fad'a.

      " Sonkai koh".Ta fad'a.

      "Mommy bata nan?" Ya tamabaya.

      "Ta fita d'azu". Ta amsa.

      " Yau ke aka bari da babyn tamu,karfa kice zaki mata wanka karki sa mata ruwa a hanci".Ahmad ya fad'a.

      "Aiko na iya". Reyhana ta fad'a.

      " No sekun dawo zaki dinga yi mata".Ya fad'a.

      "Kin fara had'a muku kayan ku de koh?"

      "Wane kaya ana zaune lau,sekace gobe zamu komo". Reyhana ta fad'a.

     " Lalle just kwanaki ne fah,gara ma ki fara shiri dan kun kusa komo wa keda baby Nasreen ".

       Tashi tayi ta tafi kitchen ta had'o masa abunsha da snacks ta kawo masa.Hira sosai sukai tayi har Ikram ta dawo Nasreen tayi bacci ta kaita d'aki,se kusan maghrib ya tafi har lokacin Mommy bata dawo ba.

      Se to 8pm tukun ,ba dad'ewa Abba ya dawo.Mommy se lokacin akai wa Nasreen wanka,Reyhana kuwa bayan tafiyar Ahmad.

        Mommy maganar tana cinta amma ta kasa fad'a wa Abba,a kwana a tashi Reyhana sunyi kwana 37 Mommy bata yi wa Reyhana maganar komawa ba.

     Shikuwa Ahmad kullum cikin lissafi dan yanzu a tunaninsa baza suyi 5days basu dawo ba,dan har siyayyar 'yan kayan stuffs yayi musu jiran dawowarsu kawai yake.

     Mommy yau de ta d'au alwashin fad'a wa Abba duk abinda ke ranta,around 8:32pm bayan sun gama dinner ta shiga d'akinsa lokacin yana 'yan danne-danne a phone d'insa.

       " Abban Reyhana ina so zami magana ne".Mommy ta fad'a tana tsaye.

     "Toh shigo ina jinki". Ya fad'a tare da ajje wayar gefe.

    Mommy waje ta samu ta zauna a kan gadon tana tunanin ta inda zata fara.

        " Dama akan Reyhana ne,ina nufin komawarta".Mommy ta fad'a.

       "Toh ina sauraro". Ya fad'a yana 'kara tattaro hankalinsa gareta.

      " A gaskiya nifa bazan yadda yarinyar nan ta koma gidanta ba".Mommy ta fad'a.

       Kuma yadda take maganar zaka gane da gaske take.Abba zama ya gyara yana kallon ikon Allah.

       "Toh bazata koma ba a gidanki zata cigaba da zaman auren kokuwa mey kike nufi?" Abba ya tambaya.

      "Ina nufin Ahmad ya sawwa'ke mata". Ta amsa ba tare da ta nuna alamar damuwa ba.
Chapter 13 · 0% Book details