← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 33

Sashe 20

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Xynab:"Ai bana class".

Ahmad:" where? "

Xynab:"Guess!"

Ahmad:"Hmm masjid"

Xynab:"No"

Ahmad:"Ok,school compound"

Xynab:"Hhh No"

Ahmad:"Then where?"

Xynab:"So you gave up"

Ahmad:"Uhmm"

Xynab:"Cafeteria".

Ahmad:" Acici"

Xynab:"Am not😞"

Ahmad:"Are you really not?"

Xynab:"Yes"

Ahmad:"I take back my word,Ok for you?"

5min silent batai reply ba,kuma bawai ta fita bane tana so taga ze damu.

Ahmad:"Hello are u there?"

Xynab:"Uhmm"

Ahmad:"I said am sorry "

Xynab:"😝"

Ahmad:"Hmm Xynab"

Xynab:"What??"

Ahmad:"Nothing"

Xynab:"Please say it"

Ahmad"U are acting childish
😁"

     Xynab:  "Am not"

Ahmad:"OK let see,how old are you?"

Xynab:"😯"

Ahmad:"Look at you girl,you think I don't know?"

Xynab:"Yes😕"

Ahmad:"Look at you ,I even..."

Xynab:"Yaya what?"

Ahmad:"Forget about it 🙊"

Xynab:"😱"

Ahmad:"Time up,prayer time"

Xynab:"OK"

Ahmad:"Bye"

Xynab:"✋"

Gaahide ya sauka amma ya kasa dena murmushi,Zainab had seda 'kawarta Siyama tayi tapping d'inta ta dawo daga tunanin data tafi wata duniyar.

       She can't stop blushing yau tayi chat da Yaya conversation d'in ya mata dad'i ."Ashe yana magana haka" Ta fad'a a ranta.

                    ***
    Reyhana koyaushe Sameer seya kira baya damuwa zata d'aga ko bazata d'aga ba.

      Sageer daba school yanzu take zuwa ba tinda ya gama  Ikram da ya rage mata 1yr kullum fama take da Sageer wajen kaita school ,Reyhana idan 'yan mutuncinta sun tashi wasu lokutan tana kaita.Yau ma ta shirya Sageer take jira jin shiru yasa Reyhana ta tashi taso shi dan idan Ikram da kanta zata rashin mutunci yake mata.

        Koda ta Shiga ta tatar yana bathroom ,har zata fito ta hangi wani rose flower akan mirror, dan san gulma da sauri ta 'karasa wajen ,rose d'in ta d'auka taga  greeting card daya sha ado cover d'in da heart kala-kala a ajje.

       "Lover boy". Ta furta a fili.

     " Yaya!" Ya kira ta da 'karfi tare da 'karasowa ya wafce rose d'in da card.

     "Iyee wata za'a kaiwa wannan Sageer?" Ta tambaya tana murmushi.

   "Babu". Ya amsa yana turasu a drawer.

" Idan baka fad'a min ba a bakin Abba Yaro".

   "Kai dan Allah waike.."

    "Yanzu de fara fita ka kaita school idan ka dawo mayi maganar lover yaro". Reyhana ta katseshi tare da fita tana dariya.

AR²💖

            *Whooo! how is the page?? Tell me what is about to happen BTW the two two😂 A&Z, S&R ❤*

choose whoaa!

*Pls comment,share and vote.*

Jasko💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣1⃣

     Zainab yanzu har ta saba ma kanta inde batai chatting da Ahmad ba bata jin dad'i,duk ranar friday kuwa seta kirashi sun gaisa.Umma har ta soma gano wani abun gameda Zainab dan ta tana lura da ita bata da zance sena Yaya Ahmad.

      Har pic d'insa ta saka ya turo mata wai duk sunan Umma ce zata gani dukda kuwa ba haka bane.Tun bata gasgata abinda zuciyarta ta fad'a yanzu ta yarda she fall for him.

                ***
Reyhana ce tsaye  hannunta ri'ke da yarinya ,a hankali ya 'karasa inda suke a tsayen.Koda ya isa wajensu ya tarar sun juya masa baya.

        "Reyhana". Ya kira sunanta cikin sanyin murya.

         A hankali ta juya fuskarta cikeda hawaye da nuna alamar damuwa.Kallonsa ya mayar kan yarinya ,a hankali ta waigo sede fuskarta ba komai(Hollow)

   A razane Ahmad ya farka,lokaci guda ya had'a zufa .Agogo ya kalla yaga 2:30am ,jikinsa a sanyaye ya shige bayi ya d'auro alwala ya tada sallah.

        Ko bayan ya idda sallar ya kasa komawa bacci,mafarkin da yayi ne yake ta masa yawo a kansa.

      " Koh wani abun ne ya faru?" Ya tambaya a zuciyarsa.

       "I have to call Reyhana  tomorrow morning".

        Wayarsa ya d'akko ya shiga gallery,photo na Nasreen tana baby ya bud'o yana kalla,hannu ya d'ora kan fuskarta yana shafawa a ransa yana ta sa'ke-sa'ke.Wayar na hannunsa bacci ya saceshi ,kan 'kirjinsa ya kifata ya soma bacci.

         Washegari da safe bayan yayi breakfast ya shige d'aki.Wayarsa ya d'auko ,number d'in Reyhana ya sa a wayar dan numbern ta baze goge a memoryn kansa ba.Da 'kyar ya samu yai dialing sede bata fara shiga ba ya katse.

      Kusan seda ya maimaita haka yafi sau hud'u amma sam baida courage yana tunanin ta ina zai soma magana kuma mey ze fad'a mata? Ya fad'a a ransa.

      Haka ya ha'kura da kiran ya ajje wayar gefe yana mey jin haushin kansa, da ace be d'au tsahon wannan lokacin ba da ba abinda ze hana ya kirata.

      Umma ya kira suka gaisa se sadiq shima dan sun kwana biyu basi waya ba.

               ***
Reyhana 'kawarta saudat ta haihu yau ake suna last two years tayi aure.

       Nasreen se tsalle take yau za'a unguwa da ita ta ishi kowa da maganar duk wanda ta gani seta fad'a masa Ummienta zata unguwa da ita dan Reyhana bata fiya fita unguwa da ita ba gara ma Mommy.

    3:30pm ta shirya ,itama Nasreen an shiryata tayi kyau sosai kamar a d'auka a gudu.

       Sallama sukai da Mommy suka fita.Ko barin layinsu batai ba mota ta tsaya yin duniya ta'ki tashi.

       Gashi Sageer baya gida balle ta kirashi ya kaita Mommy kuwa ta dena basu motarta.

      Tana cikin tunanin yadda zatai sega motar Sameer ta doso layin.

       "Shikenan kuma anace yazo". Ta fad'a tare da dukan steering motar.

        Aiko yana ganin motarta ya tsaya,yasan ko ya sauke glass d'in motarsa ba sauke nata zatai ba dan haka ya fito.

      Se da taga yazo daf ta zuge glass d'in.

       "Fita zaki ?" Ya tambayeta.

         Kai ta girgiza masa alamar "Eh".

        " Ok,but amma kamar motarki ya samu matsala koh?"

       "Eh amman zan samu napep". Ta fad'a dan karma yai mata tayi.

       " You don't need that,am here Reyhana senai dropping d'inki wajen da zaki". Ya 'kare maganar da murmushi.

       "No Sameer thanks don't worry zan tafi da kaina". Ta fad'a.

       " Reyhana come on ni nace fah'.Ya fad'a.

        "Sameer..."

          " Please".Ya katseta.

           "Ok". Ta furta.

     Dande ba yacca zatai neh kuma batason missing zuwa shiyasa dole ta ha'kura ze kaita.Baba mey gadi tasa ya kira mata mey gyara kafin ta dawo.

       Se janta da hira yake amma bata wani responding sosai " Eh" ko "A'a" shine abinda take amsasa. Ya rasa gane wace irin mace ita,har yanzu bata chanja ba tana nan da halinta ,sekace yau ta fara ganinsa.

    Rabin hirar ma da Nasreen sukai ,yana kaisu tace ya tafi zata kira Sageer yazo d'aukansu.

      ***

  Zainab yauma taci sa'a Ahmad na online, waje na musamman ta samu ta 'kule 'kuryar d'aki an d'auki pillow an d'ora a cinya ta aza hannunta akai se tapping phone take.

        Xynab: "Yaya an bamu wani assignment naso ace kana nan da ka koya min".

    Ahmad:" Hmm".

    Xynab: .Yaya wai me hmm d'innan take nufi da anyi magana sekace hmm".

    Ahmad: "Sarkin tambaya ".

Xynab: " Eyi ina so na sani".

Ahmad: Haka kike a school? "

Xynab:"Yes 😀"

Ahmad: "Ok, kina nufin kice duk wannan samarin class d'in naku haka kike musu koh"

Xynab: "Laa! 😱 Yaya ni bana kula mazan class d'in mu fa ,ni idan bakai bama ba wanda nake kulawa".

Ahmad:"Hmm".

Xynab: "Ka ganka koh😒"

Ahmad:"Stubborn ".

Xynab:" Naji,yaya saura wata nawa ka dawo?"

Ahmad: "Mey kika tanadar mini?"

Xynab: "I just ask".

Ahmad :"not more than 9"

Xynab: "😱har 9"

Ahmad: "Yayi nisa?"

Xynab: "Sosai,kai bama ka damuwa".

Ahmad:Toh ya zanyi inma na damun?"

Xynab:Umma kam tana kewarka"

Ahmad: Umma kad'ai?"

Xynab:"Uhm.."

   Ahmad :Wannan sister tawa batai missing d'ina ba".

A ranta seda taji ba dad'i ,ita bataso yake ce mata sister gara ya kira ta da sunanta.

Xynab: "I do mana🙈"

Ahmad: "Uhm harda rife ido".

Xynab:"...."

Ahmad: "Mey hakan yake nifi?"

Xynab: "😝😝"

Ahmad: "Kin ganki koh,shiyasa nace maki.."

Xynab: "Kace ni yarinyace koh? Yaya university fa nake kuma wanda yake 17yrs shine za'a kirashi yaro ? nide ba yarinya bace😠"

Ahmad :"Hhh just 17 ,sannu aunty Zainab"

Xynab: "😭😬 kuma an dena chat d'in".

  Kusan 5min bata sake typing ba shima haka,ganin da gaske take dan yaga alamar ta sau'ka seya kira.

      " Hello".Ta fad'a ciki-ciki.

      "Ayya sister sorry am just joking". Ya fad'a.

      Boom! Taji zuciyarta tayi alert ,wani tsantsar sonshi ne ya sake shiga zuciyarta,yanayin yadda yai magana ne yayi mata dad'i  dan bata ta'ba ji yayi irinta ba(Ahmad fa ya manta bada Reyhana yake magana ba😂)

        " Na'ki d'in". Zainab ta fad'a cikeda shagwa'ba.

        "Please". Ya fad'a.

         " Toh a koma chat tukun".Cewar Zainab.

         "No,sekin ha'kura.Ya fad'a.

           "Toh idan na ha'kura baza ka sake cemin yarinya ba?"

         "Bazan 'kara ba". Ya amsa.

           "Toh na ha'kura". Ta fad'a.

           " That's my zee". Ya fad'a shi kanshi besan lokacin ba.

      "Wannan wata irin su'butar baki ce ta sameshi?" Ya fad'a  a ransa.

      Zainab ta kasa sake cewa komai dan ruwan kanta ya 'kone what if shima yanda take ji haka yake ji? Kai amma da tafi kowa jin dad'i.Du ita kad'ai take zancenta a zuciyarta.

       "Zainab are you there?" Ya tambaya.

       "Eh". Ta amsa a hankali.

        " Bacci koh?" Ya tambaya.

          "Uhm". Ta amsa duk da ba baccin take ji ba kawai de over happy yasa wayar ma ba zata iya ba a yanzu.

            " Ok,toh kiyi addu'a ki kwanta". Ahmad ya fad'a.

         "Toh ,seda safe". Ta fad'a.

       Shima seda safen yace tukun yayi hanging.Da 'kyar ta iya saita kanta ta kwanta wayarta a gefen kanta tayi bacci dan pic nasa da imran yai masa ta 'kura ma ido tayi ta kalla.

      Yana ajje wayar gefe ya lura da Imran da yai tsaya yana wani murmushin na tarfo ka.

        " Mey kake kai kuma bakai bacci ba?" Ahmad ya tambaya yana wayancewa.

          "Mallam ba abinda zaka 'boyen,na jiyo ka". Imran ya fad'a.

          " Kaji mey? "Ahmad ya tambaya yana nuna be san komai ba.

         " Karka rainan hankali ka gane mey nake nifi,kullum ace sister toh yau 'karyarka ta 'kare".

      "Idan ba sister ta bace taya zance maka haka".

      " Ai shiyasa naji kana kwantar da murya ,ashe kaima ka iya, ko dayake dama ance irin ku.. "

    Be 'kare ba Ahmad ya cilla masa pillow a fuska.Dariya yai tayi sannan yace.

      "Gara ka lalla'bani ka bani labari idan ba haka ba na fallasa magana gun wa'ancen kasan su baza su raga ma ba".

        "Allah Imran ba wasa nake ba ni ba wani abu tsakanina da Zainab kawai na d'auketa a matsayin sister ne". Ahmad ya fad'a fuskarsa ba alamar wasa.
Chapter 20 · 0% Book details