← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 33

Sashe 28

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Reyhana ce ta fara fita a tunaninta ko Nasreen tana biye da ita.Ganin Ummienta tayi gaba tayi sauri ta bud'e wardrobe ta ciro kayanta kala d'aya ta cusa a cikin jakarta ta fito se muzurai take.

Mommy kafin ta 'karaso dinning d'in ta nufi d'akin Sageer.

" Yau ma bazaka aikin ba?"Ta tambaya.

"Zanje se anjima". Ya amsa.

" Toh ka fito kayi breakfast mana kai shikenan kuma se kaita 'buya a d'aki".

Da 'kyar ya taso,sake cin magani yayi dan ya lura da su Ikram kallon munafinci sike masa,daga ya had'a ido da Abba seya kauda kai.

"Nasreen ya naga jakarnan ta 'kara wani tudu mey kika sa aciki?" Walida ta tambaya.

Reyhana se lokacin ta lura da tudun jakar,hannu tasa tana shafawa ko zataji wani abun da sauri Nasreen taja baya.

"Ba komai fa". Ta fad'a kamar mey shirin yin kuka.

" Toh kiyi sauri ki gama ci kafin driver yazo".Reyhana ta fad'a.

Mommy da hankalinta baya gunsu ko tanka musu ma batai ba.

°°°

Mommy bayan ta komo d'aki ta kira Anty Asma'u ta sanar mata halin da ake ciki daga baya Anty Asma'u tace zata zo Sageer d'in ya kaita gidan itama ta gwada tata sa'ar.

Ahmad se bayan ya dawo gida ya tafi school d'in su Nasreen, lokacin daya je ba'a tashe su ba seda ya jira.

Tana ganinsu ta kyalla da gudu hadda tuntu'be.

"Uncle !" Ta kira sunansa.

"Uncle ita Anty Zainab bata zo ba yau?" Ta tambaya.

"Ehyyi". Ya amsa.

" Uncle ka kaini wajenta". Ta fad'a.

"Driver zezo ya d'auke ki ,ki bari se kin fad'awa Ummienki".

" Ai na fad'a mata ,kaga ta bani wasu kayan ma". Ta fad'a tana zuge zip d'in jakar.

Shide yasan Reyhana baza ta bari ya kaita gida ba.

"Ummienki bata san kin d'akko ba koh?". Ahmad ya fad'a.

" Toh dan Allah ka kaini ai bazan dad'e ba seka fad'a mata".

"Ince mata mey?"

"Kace mata ka kaini wajen Anty Zainab".

" Yanzu yamma tayi ki bari se gobe kinga ba school ma".Ya fad'a.

"Uncle dan Allah ka kaini". Ta fad'a tana bubbuga kafa kamar zatai kuka.

Seda ya d'an nisa tukun yace " Toh zan kaiki".

Tsalle ta shiga yi tana murna ,da sauri ta shige motar.Ahmad seda driver yazo d'aukansu ya fad'a masa Nasreen baza ta biyo su ba.

Ya kira Reyhana a waya dan ya fad'a mata amma ta'ki d'aga wa ,daga baya kawai ya tura mata text  sannan suka tafi.

     Sanda suka isa gidan Nasreen ta 'ki sakewa.

    "Taho ki gaishe da Umma". Ahmad ya fad'a tare da kamo hannunta.

       A hankali ta 'karasa wajen Umma kanta a sunkuye ta gaisheta.

      " An dawo daga makaranta koh?" Umma ta fad'a.

      "Eh". Ta amsa tare da gid'a kai.

      Ganin Zainab ta shigo yasa ta yin murmushi tare da 'karasawa inda take.

      "'Yan mata yau kece a gidan?"

        Nan ma kai ta gid'a bata ce komai ba.

     "A cire jakar koh?"Zainab ta fad'a.

      " Eh,kayana ma suna cikin jaka".Ta fad'a.

       "Iyee kwana nawa za'ai mana?" Umma ta tambaya.

        "Zaki kwana?" Zainab ta tambaya.

     Kai ta gid'a tana murmushi ,Zainab ce ta jata d'akinta ta sauya mata kayanta, cikin 'kan'kanin lokaci ta fara sakin jiki tana ta labarin school.

     Reyhana yanzu ne ta lura da text d'in daya tura mata a take ta kira Ahmad.Yana parlor kiranta ya shigo dan haka ya d'an fita tukun yayi picking.

     "Ina ka kaimin yarinya?" Ta tambaya bayan ya d'aga.

     "Kinsan de bazan sace taba koh" Ahmad ya fad'a cikin sanyin murya.

     "Taya zan shede ka nasan mey ka zama". Cewar Reyhana.

      " Don't worry ba dad'ewa zatai ba".Ya fad'a.

       "Yanzu nake so ta dawo ni bana son gantali".Ta fad'a.

        " Ita fa tace a kaita wajen Zainab ".Ya fad'a.

         " Ni be shafen ba a dawo min da yarinya yamma tayi".Ta fad'a.

       "Toh an gama". Ya fad'a kamar mey shirin yin dariya.

      Bata jira ya sake wata maganar ba ta katse.

        Jealous?  Ya tambayi kansa.

      Yana komawa yace Nasreen ta taso ya maida ita ta'ki ita se anjima,Umma ma hakan tace haka ya 'kyaleta.

     Ba zato ba tsammani hadari ya murtike garin kafin ace mey ruwa ya sauka.Reyhana ta gama 'kulewa takaici ya isheta ita a tunaninta ma yana sane ya'ki dawo da ita.

     Ahmad kuwa ba haka bane a gunsa ya 'kagu ruwan ya tsagaita ya kaita amma shiru 'karfin ruwan ma 'karuwa yake.Nasreen kuwa ko a jikinta se game take a wayar Zainab a haka lokaci yai ta ja, gashi idan ya kira Reyhana baya samunta saboda 'karancin network.

       Har bayan maghrib ana ruwa,Ahmad du yabi ya damu dan yasan Reyhana tana nan ta cika tayi fam.

       Zainab wayar ta amsa daga hannun Nasreen tace zatai mata photo, ba musu ta bata.Tsayawa tayi ta nutsu ta bada attention tana jira a  'kyasta mata.

    Ana d'auka  ta kar'ba taje ta nuna wa Ahmad.



Nasreen

   " Iyye! Toh jeki nuna wa Umma". Ahmad ya fad'a.

      Da sauri taje ta nuna mata itama ,bayan nan Umma ta zuba mata abinci taci ,ba jimawa tayi bacci.

        "Bakai waya da mamanta ba ka fad'a mata?" Umma ta tambaya.

        "Na kira ban sameta ba ba network me kyau". Ya fad'a.

        " Toh ga wayar Zainab ka kira koh zaka semeta kaga shirin ba dad'i".Cewar Umma.

      Wayar Zainab yayi amfani da ita ya kira Reyhana kiran farko ta d'aga.

      "Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

      " Waalaikumussalam".Ya amsa.

       "Reyhana it's me". Ya fad'a.

       "Mey zaka fad'a mini kuma?" Ta tambaya cikeda takaici.

       "Na dad'e ina kiranki bana saminki ,kinga yanayin garin baze yiwu mu fito ba". Ahmad ya fad'a.

      " Kana sane kayi hakan ,daga nan ta ri'keta karta baro ta ta dawo". Ta fad'a daga nan tayi hanging.

       Daman yasan za'ai haka bata tsaya ma ta saurare shi ba balle yayi mata maganar tayi Nasreen tayi bacci.

       Reyhana tunda take bata ta'ba kaiwa irin wannan lokacin bata tare da Nasreen ba dan ba inda take iya zuwa ta kwana.

     Su kansu 'yan gidan kowa kewarta yake,tunda Reyhana taga 9pm yayi ta fidda ran dawowarta yau.

      Kowa ya shige d'akinsa itama haka ,ta 'kurawa side da Nasreen take yin bacci se tunanota take,bata jin zata iya yarda Ahmad ya raba ta da Nasreen.

        Wata zuciyarce tace mata ta kira shi,dan haka ta d'auki waya ta kira.Tana tsammanin taji muryar Ahmad amma seta ji muryar mace.

       "Assalamu Alaykum". Aka fad'a.

       Da'kyar ta iya cewa "waalaikumussalm".

      " Uh..ya mance wayar ne a gida".Taji an fad'a.

        Bata ce komai ba ta katse wayar, a zuciyarta tana sa'ke-sa'ke.

         "Zainab?" Ta tambayi kanta.

         Tashi tayi daga zaunen tana ta tunani iri-iri  da ta kalli window ta hangi kamar hasken mota daga gate.'Karasawa wajen tagar tayi ta le'ka ,gani tayi da gaske mota ce ta tsaya lokaci guda zuciyarta ta fad'a mata Ahmad ne.

      Mayafinta tai sauri ta yafa ta fita a sand'a dan garin yayi tsit ga sanyi -sanyi daya ke busawa.

°•°
      Ahmad yana gani ruwan ya tsaya around 9:09pm ya d'auka key ,Nasreen da tayi nisa da bacci haka ya d'auketa ya fita.Zainab se bayan ya fita ta lura da phone d'insa daya manta,bayan mintina da fitarsa taji ringing d'in wayar da batai niyyar d'agawa ba seda Umma tace ta d'aga tukun.

        "Azizaty❤" sunan da tagani a screen d'in,dan haka a sanyaye ta d'aga ,da'kyar ta iya tayi bayanin baya nan  and lastly abinda tayi noticing shine an katse wayar.

          Koda ta komo d'aki ba abinda yake mata yawo aka kamar sunan da taga ni a jiki.

       "Har yanzu yana yin waya da ita kenan? hakan yana nufin ze dawo da ita?"

        "Toh ko wata budurwar tashi ce ?" Abinda tayi ta tambaya kenan wanda bata da amsarsu.

      Ahmad koda ya isa gidansu Reyhana wayarsa ya shiga laluba dan ya kira ta amma yaga babu.

         Yana shawarar fitowa daga motar sega Reyhana ta bud'e'kofar gate d'in.

AR²💖

     Pls comment,vote and share💋

Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣1⃣

Tana daga bakin 'kofar ta'ki 'karasowa gashi fitilar motar ta hasketa.

Fitowa yayi daga motar ya 'karasa har inda take a ransa yana tunanin mey ze fara ce mata.

"Reyhana am sorry ban kawo ta da wuri ba". Ya fad'a .

" Yanzun tana ina?" Ta tambaya.

"Tana cikin mota ,tayi bacci ne".Ya amsa.

Takawa tayi ta 'karasa inda motar take, ta bud'e 'kofar zata d'akko ta ya maida 'kofar ya rufe.

" Ka d'auke hannunka a 'kofar nan".Ta fad'a.

"We need to talk". Ya fad'a.

" Bani da wannan lokacin".Cewar Reyhana tare da watsa masa harara.

"Se yaushe ? Gobe? jibi? Yaushene zaki yarda dani ? Reyhana how many times do I have to tell you,kema kinsan ina nan bazan ta'ba d'aukan wannan tsahon lokacin ban zo ba ,ko bayan da na dawo kece kika hana ni zuwa you know why?" Cikin d'aga murya yake wannan maganar.

"Saboda na rasa abinda zance maki ki yarda dani a wannan lokacin,Umma tayi iya 'ko'karinta tazo amma mey ya faru ? Can you explain that?"

Reyhana shiru tayi ta kasa sake cewa komai ta kau da kanta gefe.

"Why are you punishing me like that ? am begging you please forgive me ,am very sorry!"

Bata ce masa komai ba , kasancewar ya d'auke hannunsa daga 'kofar motar hakan ya bata dama ta bud'e ,Nasreen dake kwance ta kinkimeta ta d'ora a kafad'a.

Bece mata komai ba ya bud'e 'kofar gidan gaba ya ciro jakar Nasreen ya mi'ka mata.

Hannu tasa ta kar'ba ta wuce,seda yaga shigewarta gida ya komo mota ya tafi.

Tana shiga gida ta kwantar da ita ,se lokacin taji sa'ida ba 'karamin dad'i taji ba daya dawo mata da ita.Se lokacin ta samu itama ta kwanta amma kuma se tuna muryar Zainab da taji d'azu take a wayar Ahmad,da wannan tunanin tayi bacci.

***
Washegari da safe bayan Nasreen ta tashi ta soma bawa Reyhana labari.

"Anty Zainab ce ta chanja min kayana". Nasreen ta fad'a.

" Jiya dama kaya ne a jakar ki koh ,shine kika hana a gani".

"Kuma ta d'aukeni a wayar ta". Nasreen ta fad'a.

"Kinci abinci jiyan?" Reyhana ta tambaya.

"Eh Umma ce ta bani ma". Ta amsa.

" Umma?".Reyhana ta tambaya.

"Eh Umman su Uncle ce ".
Chapter 28 · 0% Book details