Sashe 22
Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Seda ta tabbata tayi nisa da bacci tukun ta komo falo,duk yaran gidan suna falon amma banda Sageer.Kusan kwana biyu haka yake seya 'ki fito ba kamar da ba dayake fito a d'an yi hira kafin su kwanta.
"Walida Sageer be dawo bane?" Reyhana ta tambaya.
"Ya dawo yana d'aki". Ta amsa.
" Yaci abinci?" Ta sake tambaya.
"Beci ba ,Yaya Ikram ma tana masa magana yayi banza da ita ya wuce d'akinta".Cewar Walida murya 'kasa-'kasa.
Kai kawai ta kad'a ta zauna kan kujera.
AR²💖
Comment,vote and share.Luv u all💋
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 2⃣3⃣
Washegari da safe around 8:15am kowa ya hallara a dining seat d'in Walida ne kad'ai empty se Nasreen da tun d'azu driver ya kaita makaranta.
"Walida bata tashi bane?" Abba ya tambaya.
"Ta tashi". Ikram ta amsa.
" Toh mey take baza ta fito ba?" Mommy ta fad'a.
"Ikram kije ki kirata". Cewar Mommy.
" Mommy nafa makara is almost 8:30am".Ikram ta fad'a.
"Bari na kirata". Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa.
Murya taji 'kasa-'kasa lokacin da ta shiga d'akin,blanket taga alaman Walida ta rufe kanta dashi.
" My Prince ka daure kasha magani idan ba haka ba kanka ze cigaba da ciwone kaji".
Baki Reyhana ta saki jin muryar Walida tana waya.'Karasawa gadon tayi ta cukuikui blanket d'in ta yaye ta.
Cikin razana Walida ta mi'ke zaune ,wayar ma tayi cilli gefe da ita,a zatonta Mommy ce.Ganin Reyhana ce yasa ta d'an ji relief tasan komai zezo da sau'ki
"Iyye abinda kikeyi kenan?" Reyhana ta fad'a.
Walida a sukwane ta d'auki wayar tayi hanging sannan ta dawo da kallonta wajen Reyhana.
"Da 'kawata fa nake waya". Walida ta fad'a.
" Shiyasa naji kina cewa My Prince ko? Ke bazaki nutsu ba koh ? Shikenan zan fad'a wa Abba kinga se ya aurar dake kowa ya huta naga alamar aure kike so".
"Yaya dan Allah kiyi ha'kuri bazan 'kara ba". Walida ta fad'a.
"Waye wannan d'in?" Reyhana ta tambaya.
"Waseem". Ta amsa tana sosa kai.
" A ina yake?"
"Uhm..uhh d'an school d'inmu". Ta amsa a kunyace.
" Class mate d'inki?,'karya yake miki wannan iyayensa ba aure zasi masa yanzu ba har nawa yake,just wannan year d'in fa kukai graduating kuma shine kike kulashi sakarya ,duk sanda na sake gani kina waya dashi sena fad'a wa Abba ya miki auren dole".
Shiru tayi kanta a sunkuye ta'ki cewa 'kus.
"Tashi ki wuce ki breakfast". Ta fad'a tare da ficewa.
Bayanta tabi suka sauka 'kasa lokacin har Ikram ta tafi aiki.Muzurai tayi tayi kar Reyhana ta fad'a wa Mommy.
***
Ahmad yau ko breakfast beyi ba ya fice a motarsa marcedes mey black color, yana hanya sega kiran Zainab.
" Yaya ina kwana". Ta gaisheshi.
"Lafiya lau". Ya amsa.
" Umma tace gobe zaki dawo koh?"
"Eh".Ta amsa.
" Ok toh Allah ya kaimu".Ya fad'a ta amsa da Ameen ,daga haka sukai sallama ba tare da sunyi doguwar hira ba.
°°°
3pm Reyhana da Mommy suna zaune a falo kamar daga sama suka ji an turo 'kofa da 'karfi.
Sageer suka gani da sauri ya wuce d'akinsa ko ta kansu bebi ba.
"Mommy wai Sageer lafiyarsa lau kwana biyu?"Cewar Reyhana.
" Atoh gashinan de kullum cikin 'kunci da fushi".Mommy ta fad'a.
"Bari naje".Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa ta nufi d'akinsa.
A bud'e ta tarar da 'kofa saboda haka sallama tayi ta shiga.
A kwance ta iskeci yayi rigingine hannunsa akan goshinsa ya 'kura wa ceiling ido ko takalmin dake 'kafarsa be cire ba.
" Sageer meyake faruwane wai?"Reyhana ta tambaya.
Se lokacin ya kula ma tana d'akin.
"Babu". Ya fad'a ciki-ciki.
" Amma na ganka haka".
"Kawai na gaji ne". Ya fad'a.
" Nifa ba wacce zaka 'boyewa abu bace, meye amfanin 'yan uwa idan bazasu san matsalar ka ba su taimaka maka kayi solving ba?"
Mi'kewa yayi zaune fuskarsa damuwa 'karara ta banyana.
"Wannan abun ba abune wanda zaku iya taimaka min ba kuma ina ganin ma na makara". Ya fad'a.
" Koda addu'a ai mu masu taimaka maka ne,tell me meyake faruwa".Reyhana ta fad'a tare da 'karasowa inda yake.
Wayarsa kawai ya d'auko ya bud'o wani pic na mace 'yar budurwace kyakkyawa a kai.
"Fatima". Ya fad'a.
" Fatima? Itace damuwarka koh?"
"Ummien Nasreen Allah bazan iya rayuwa ba ita ba,I can't bear to loss her,suna nema su rabani da ita".
" Suwaye?" Ta tambaya cikin nuna damuwa.
"Iyayenta ,sune zasu aura mata cousin d'inta".Ya 'kare maganar kamar zeyi kuka.
Reyhana tausayin 'kanin nata ne ya kamata lokaci guda kuma ta tuno rabuwarsu da Ahmad.
" Komai zezo da sau'ki Sageer,zan taya ka da addu'a kaima ka dinga yi".Ta fad'a.
Kai ya gid'a almar "Toh" tare da fad'in "Amma karki fad'awa Mommy".
" Don't worry bazata sani ba".
"Thank you". Ya fad'a.
Murmushi ta 'kalo tace " Is okay".
***
Ahmad yana komawa gida ya tarar da Imran yazo,Umma tana fita daga falon Imran ya tinti'beshi.
"Ya ake ciki har yanzu baka Jeba?"
"Uhm". Ya amsa.
" Ina baka shawara ka gaggauta zuwa kar kazo kayi da kasani,this is too much 6yrs ba wasa bane Ahmad ya kamata ka gane".
"Ni kaina nasani Imran tunanin yadda Reyhana zata yarda da abunda zance mata nake"Ahmad ya fad'a.
" Malam ka cire wannan abun a ranka,ta yarda karta yarda Nasreen is your daughter ba yadda zasi ,dan haka gara ma ka mi'ke ba wajensu zaka ba 'yarka kaje gani".
Sosai maganar Imran ta shigeshi,yaji 'karfin gwiwa a yanzu ya shirya zuwa gidansu Reyhana.
Da daddare Umma take fad'a masa gobe ze d'akko Zainab daga tasha.
Beso kasancewar hakan ba saboda lissafinsa ze ruguje na zuwa gidansu Reyhana.
°°°
2days later
Daga aiki koh gida be komo ba Ahmad direct ya wuce gidansu Reyhana around 5pm lokacin.
Daga can nesa yai parking a zuciyarsa yana sa'ke-sa'ke iri -iri ,ya shafe kusan 30hrs be fito ba se shawarwari yake,gashi bega ko mutum d'aya na gidan ba a waje.
Ya dafa hannunsa a steering ya maida kallonsa gate d'in gidan ,mota ya gani ta sauke yara guda uku ta juya.
Biyu daga cikinsu mace da namiji d'ayar kuwa Nasreen ce suna sanye da uniform na Tahfiz.
Guda biyun gidan dake gefensu Reyhana suka shiga ita kuwa Nasreen bye tayi musu da hannu tsayawa tai gate ta hau kan wani tudu se cisgo flowers da suka shingid'o ta bango take.
Sam ya kasa bawa kansa amsar abinda zuciyarsa ke tambaya."Is she Nasreen? My daughter ?"
Baro 'kofar gidan tayi tana nufowa inda motarsa take,daya kalli direction da takeyi ya kula ashe ita mage ta biyo takeson d'auka.
A sanyaye ya fito daga motar ya bita da kallo magen ta gudan mata ,komowa tayi zata shige inda yake ya tsayar da ita.
"'Yar yarinya". Ya kira ta.
Waiwayowa tayi ta kalleshi" Ni gida zan tafi ummiena ta hanani magana da wasu a waje".Ta fad'a.
"Eh yanzu ai zan tafi,amma ya sunanki?" Ya tambayeta.
"Nasreen, Aisha Ahmad Yusuf". Ta amsa.
Amsar data bashi ya isheshi tabbatar da abinda yake tunani.
Ma'kwat! Ya had'iyi yawun daya tokare a ma'kgoronshi.
" Kaji kunya 'yarka bata sanka ba".Zuciyarsa ta fad'a.
Daurewa yayi yace" Ni sunana Uncle".
"Uncle ? Koya min karatu zaka yi?" Ta tambaya.
Fuskarsa d'auke da murmushi yace "Eh".
" A nan?" Ta sake tambaya.
"A'a ,ya sunan school d'inku?"
Amsa masa tayi sannan tace"Ummiena zata jamin kunne idan ban koma ba".
"Eh kije gida yanzu". Ya fad'a.
Da sauri ta wuce ta shiga gidan yana tsaye har ta shige tukun ya koma mota ya tafi.
Nasreen kuwa tana shiga gida ta soma bada labari taga wani sunansa Uncle.
" Ban hanaki yiwa mutanen waje magana ba?" Cewar Reyhana.
"Shine ya fara yimin magana wai ze koyan karatu".
" Toh karki sake kinji koh".Reyhana ta fad'a.
"Toh ummie". Nasreen ta fad'a tana cire hijabi.
Reyhana tunani ta shigayi wannan waye?
AR²💖
Comment,vote and share.love u all💋
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 2⃣4⃣
Lokacin da ya dawo gida su Umma na falo yana jiyo su ita da Zainab,d'akinsa ya shiga ya zauna yana ta tunano Nasreen.
Se yanzu ya sake gane rashin kyautawar da yayi na rashin bata kulawar da ta wajaba a kansa.
°°°
Se wajen maghrib daya fito zeje masjid Zainab ta ganshi.
"Laa dama ka dawo gida".
" Eh ai ban jima da dawowar ba". Ya amsa.
"Masallaci zaka?" Ta tambaya.
"Uhm". Ya amsa.
" Toh seka dawo". Ta fad'a.
Zainab bayan fitarsa ta shiga kitchen had'a abincin dare.
***
Reyhana tana d'aki hankalinta ya d'aga Sameer yazo Nigeria d'azu ya kirata ya fad'a mata.Yanzu bata da 'karyar da zata fad'a masa,bama shi kad'ai ba har Abba.Nasreen tuni tayi bacci ita kad'ai se juyi take ta kasa bacci tunani ya isheta.
Saudat ce abokiyar shawara yanzu kuma dare yayi sede gobe,abunda ya fad'o mata a rai kenan.Dakyar ta samu ta iya yin bacci.
***
Washegari da safe bayan ya gama shirinsa ya fito falo ,Zainab ya tarar tayi shirin school da alama ma shi take jira.Shi ya mance ma da kaita school se yanzu ya tina.
"Ina kwana yaya". Ta gaisheshi.
" Lafiya lau". Ya amsa.
'Kokari yayi ya kauda idonsa daga kallonta dan kwalliyarta tana masa 'kwarjini,sosai tayi mugun kyau.Doguwar riga blue tasa se rolling datai golden d'in mayafi ta sa'kala jakarta golden fuskarta tasha kwalliya ga maroon lipstick daya haskata.
"Ka shiryo kenan".Umma ta fad'a sanda ta shigo falon.
" Eh d'azu na shigo mu gaisa kuma kin koma bacci,ina kwana". Ya gaisheta.
"Lafiya lau,bazaka karya ba?" Ta tambaya.
"Eh se anjima". Ya amsa.
" Toh sekun dawo"Ta fad'a.
Yana ficewa tabi bayansa,a cikin ranta tana jin dad'i musamman da taga sunyi ango shi yasa blue d'in shadda.
Cikin 'kan'kanin lokaci ya kaita kafin ta fita daga motar ya 'kara mata kud'in makaranta dukda ana bata daga gidansu.
•••
Yauma daga aiki be koma gida ba seya je school d'insu Nasreen,4pm lokacin yana tsaya a gate d'in yana tunanin yadda ze ganta.
Da'kyar mey gadi ya barshi ya shiga wani daga cikin malamanne ya kira Nasreen tazo.
"Kinsan wannan?" Suka tambayeta.
Seda ta tsaya na d'an lokaci tukun tace "Eh".
Wata daga cikin malaman tace " Ai gashi ma kamar su d'aya".
"Walida Sageer be dawo bane?" Reyhana ta tambaya.
"Ya dawo yana d'aki". Ta amsa.
" Yaci abinci?" Ta sake tambaya.
"Beci ba ,Yaya Ikram ma tana masa magana yayi banza da ita ya wuce d'akinta".Cewar Walida murya 'kasa-'kasa.
Kai kawai ta kad'a ta zauna kan kujera.
AR²💖
Comment,vote and share.Luv u all💋
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 2⃣3⃣
Washegari da safe around 8:15am kowa ya hallara a dining seat d'in Walida ne kad'ai empty se Nasreen da tun d'azu driver ya kaita makaranta.
"Walida bata tashi bane?" Abba ya tambaya.
"Ta tashi". Ikram ta amsa.
" Toh mey take baza ta fito ba?" Mommy ta fad'a.
"Ikram kije ki kirata". Cewar Mommy.
" Mommy nafa makara is almost 8:30am".Ikram ta fad'a.
"Bari na kirata". Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa.
Murya taji 'kasa-'kasa lokacin da ta shiga d'akin,blanket taga alaman Walida ta rufe kanta dashi.
" My Prince ka daure kasha magani idan ba haka ba kanka ze cigaba da ciwone kaji".
Baki Reyhana ta saki jin muryar Walida tana waya.'Karasawa gadon tayi ta cukuikui blanket d'in ta yaye ta.
Cikin razana Walida ta mi'ke zaune ,wayar ma tayi cilli gefe da ita,a zatonta Mommy ce.Ganin Reyhana ce yasa ta d'an ji relief tasan komai zezo da sau'ki
"Iyye abinda kikeyi kenan?" Reyhana ta fad'a.
Walida a sukwane ta d'auki wayar tayi hanging sannan ta dawo da kallonta wajen Reyhana.
"Da 'kawata fa nake waya". Walida ta fad'a.
" Shiyasa naji kina cewa My Prince ko? Ke bazaki nutsu ba koh ? Shikenan zan fad'a wa Abba kinga se ya aurar dake kowa ya huta naga alamar aure kike so".
"Yaya dan Allah kiyi ha'kuri bazan 'kara ba". Walida ta fad'a.
"Waye wannan d'in?" Reyhana ta tambaya.
"Waseem". Ta amsa tana sosa kai.
" A ina yake?"
"Uhm..uhh d'an school d'inmu". Ta amsa a kunyace.
" Class mate d'inki?,'karya yake miki wannan iyayensa ba aure zasi masa yanzu ba har nawa yake,just wannan year d'in fa kukai graduating kuma shine kike kulashi sakarya ,duk sanda na sake gani kina waya dashi sena fad'a wa Abba ya miki auren dole".
Shiru tayi kanta a sunkuye ta'ki cewa 'kus.
"Tashi ki wuce ki breakfast". Ta fad'a tare da ficewa.
Bayanta tabi suka sauka 'kasa lokacin har Ikram ta tafi aiki.Muzurai tayi tayi kar Reyhana ta fad'a wa Mommy.
***
Ahmad yau ko breakfast beyi ba ya fice a motarsa marcedes mey black color, yana hanya sega kiran Zainab.
" Yaya ina kwana". Ta gaisheshi.
"Lafiya lau". Ya amsa.
" Umma tace gobe zaki dawo koh?"
"Eh".Ta amsa.
" Ok toh Allah ya kaimu".Ya fad'a ta amsa da Ameen ,daga haka sukai sallama ba tare da sunyi doguwar hira ba.
°°°
3pm Reyhana da Mommy suna zaune a falo kamar daga sama suka ji an turo 'kofa da 'karfi.
Sageer suka gani da sauri ya wuce d'akinsa ko ta kansu bebi ba.
"Mommy wai Sageer lafiyarsa lau kwana biyu?"Cewar Reyhana.
" Atoh gashinan de kullum cikin 'kunci da fushi".Mommy ta fad'a.
"Bari naje".Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa ta nufi d'akinsa.
A bud'e ta tarar da 'kofa saboda haka sallama tayi ta shiga.
A kwance ta iskeci yayi rigingine hannunsa akan goshinsa ya 'kura wa ceiling ido ko takalmin dake 'kafarsa be cire ba.
" Sageer meyake faruwane wai?"Reyhana ta tambaya.
Se lokacin ya kula ma tana d'akin.
"Babu". Ya fad'a ciki-ciki.
" Amma na ganka haka".
"Kawai na gaji ne". Ya fad'a.
" Nifa ba wacce zaka 'boyewa abu bace, meye amfanin 'yan uwa idan bazasu san matsalar ka ba su taimaka maka kayi solving ba?"
Mi'kewa yayi zaune fuskarsa damuwa 'karara ta banyana.
"Wannan abun ba abune wanda zaku iya taimaka min ba kuma ina ganin ma na makara". Ya fad'a.
" Koda addu'a ai mu masu taimaka maka ne,tell me meyake faruwa".Reyhana ta fad'a tare da 'karasowa inda yake.
Wayarsa kawai ya d'auko ya bud'o wani pic na mace 'yar budurwace kyakkyawa a kai.
"Fatima". Ya fad'a.
" Fatima? Itace damuwarka koh?"
"Ummien Nasreen Allah bazan iya rayuwa ba ita ba,I can't bear to loss her,suna nema su rabani da ita".
" Suwaye?" Ta tambaya cikin nuna damuwa.
"Iyayenta ,sune zasu aura mata cousin d'inta".Ya 'kare maganar kamar zeyi kuka.
Reyhana tausayin 'kanin nata ne ya kamata lokaci guda kuma ta tuno rabuwarsu da Ahmad.
" Komai zezo da sau'ki Sageer,zan taya ka da addu'a kaima ka dinga yi".Ta fad'a.
Kai ya gid'a almar "Toh" tare da fad'in "Amma karki fad'awa Mommy".
" Don't worry bazata sani ba".
"Thank you". Ya fad'a.
Murmushi ta 'kalo tace " Is okay".
***
Ahmad yana komawa gida ya tarar da Imran yazo,Umma tana fita daga falon Imran ya tinti'beshi.
"Ya ake ciki har yanzu baka Jeba?"
"Uhm". Ya amsa.
" Ina baka shawara ka gaggauta zuwa kar kazo kayi da kasani,this is too much 6yrs ba wasa bane Ahmad ya kamata ka gane".
"Ni kaina nasani Imran tunanin yadda Reyhana zata yarda da abunda zance mata nake"Ahmad ya fad'a.
" Malam ka cire wannan abun a ranka,ta yarda karta yarda Nasreen is your daughter ba yadda zasi ,dan haka gara ma ka mi'ke ba wajensu zaka ba 'yarka kaje gani".
Sosai maganar Imran ta shigeshi,yaji 'karfin gwiwa a yanzu ya shirya zuwa gidansu Reyhana.
Da daddare Umma take fad'a masa gobe ze d'akko Zainab daga tasha.
Beso kasancewar hakan ba saboda lissafinsa ze ruguje na zuwa gidansu Reyhana.
°°°
2days later
Daga aiki koh gida be komo ba Ahmad direct ya wuce gidansu Reyhana around 5pm lokacin.
Daga can nesa yai parking a zuciyarsa yana sa'ke-sa'ke iri -iri ,ya shafe kusan 30hrs be fito ba se shawarwari yake,gashi bega ko mutum d'aya na gidan ba a waje.
Ya dafa hannunsa a steering ya maida kallonsa gate d'in gidan ,mota ya gani ta sauke yara guda uku ta juya.
Biyu daga cikinsu mace da namiji d'ayar kuwa Nasreen ce suna sanye da uniform na Tahfiz.
Guda biyun gidan dake gefensu Reyhana suka shiga ita kuwa Nasreen bye tayi musu da hannu tsayawa tai gate ta hau kan wani tudu se cisgo flowers da suka shingid'o ta bango take.
Sam ya kasa bawa kansa amsar abinda zuciyarsa ke tambaya."Is she Nasreen? My daughter ?"
Baro 'kofar gidan tayi tana nufowa inda motarsa take,daya kalli direction da takeyi ya kula ashe ita mage ta biyo takeson d'auka.
A sanyaye ya fito daga motar ya bita da kallo magen ta gudan mata ,komowa tayi zata shige inda yake ya tsayar da ita.
"'Yar yarinya". Ya kira ta.
Waiwayowa tayi ta kalleshi" Ni gida zan tafi ummiena ta hanani magana da wasu a waje".Ta fad'a.
"Eh yanzu ai zan tafi,amma ya sunanki?" Ya tambayeta.
"Nasreen, Aisha Ahmad Yusuf". Ta amsa.
Amsar data bashi ya isheshi tabbatar da abinda yake tunani.
Ma'kwat! Ya had'iyi yawun daya tokare a ma'kgoronshi.
" Kaji kunya 'yarka bata sanka ba".Zuciyarsa ta fad'a.
Daurewa yayi yace" Ni sunana Uncle".
"Uncle ? Koya min karatu zaka yi?" Ta tambaya.
Fuskarsa d'auke da murmushi yace "Eh".
" A nan?" Ta sake tambaya.
"A'a ,ya sunan school d'inku?"
Amsa masa tayi sannan tace"Ummiena zata jamin kunne idan ban koma ba".
"Eh kije gida yanzu". Ya fad'a.
Da sauri ta wuce ta shiga gidan yana tsaye har ta shige tukun ya koma mota ya tafi.
Nasreen kuwa tana shiga gida ta soma bada labari taga wani sunansa Uncle.
" Ban hanaki yiwa mutanen waje magana ba?" Cewar Reyhana.
"Shine ya fara yimin magana wai ze koyan karatu".
" Toh karki sake kinji koh".Reyhana ta fad'a.
"Toh ummie". Nasreen ta fad'a tana cire hijabi.
Reyhana tunani ta shigayi wannan waye?
AR²💖
Comment,vote and share.love u all💋
Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 2⃣4⃣
Lokacin da ya dawo gida su Umma na falo yana jiyo su ita da Zainab,d'akinsa ya shiga ya zauna yana ta tunano Nasreen.
Se yanzu ya sake gane rashin kyautawar da yayi na rashin bata kulawar da ta wajaba a kansa.
°°°
Se wajen maghrib daya fito zeje masjid Zainab ta ganshi.
"Laa dama ka dawo gida".
" Eh ai ban jima da dawowar ba". Ya amsa.
"Masallaci zaka?" Ta tambaya.
"Uhm". Ya amsa.
" Toh seka dawo". Ta fad'a.
Zainab bayan fitarsa ta shiga kitchen had'a abincin dare.
***
Reyhana tana d'aki hankalinta ya d'aga Sameer yazo Nigeria d'azu ya kirata ya fad'a mata.Yanzu bata da 'karyar da zata fad'a masa,bama shi kad'ai ba har Abba.Nasreen tuni tayi bacci ita kad'ai se juyi take ta kasa bacci tunani ya isheta.
Saudat ce abokiyar shawara yanzu kuma dare yayi sede gobe,abunda ya fad'o mata a rai kenan.Dakyar ta samu ta iya yin bacci.
***
Washegari da safe bayan ya gama shirinsa ya fito falo ,Zainab ya tarar tayi shirin school da alama ma shi take jira.Shi ya mance ma da kaita school se yanzu ya tina.
"Ina kwana yaya". Ta gaisheshi.
" Lafiya lau". Ya amsa.
'Kokari yayi ya kauda idonsa daga kallonta dan kwalliyarta tana masa 'kwarjini,sosai tayi mugun kyau.Doguwar riga blue tasa se rolling datai golden d'in mayafi ta sa'kala jakarta golden fuskarta tasha kwalliya ga maroon lipstick daya haskata.
"Ka shiryo kenan".Umma ta fad'a sanda ta shigo falon.
" Eh d'azu na shigo mu gaisa kuma kin koma bacci,ina kwana". Ya gaisheta.
"Lafiya lau,bazaka karya ba?" Ta tambaya.
"Eh se anjima". Ya amsa.
" Toh sekun dawo"Ta fad'a.
Yana ficewa tabi bayansa,a cikin ranta tana jin dad'i musamman da taga sunyi ango shi yasa blue d'in shadda.
Cikin 'kan'kanin lokaci ya kaita kafin ta fita daga motar ya 'kara mata kud'in makaranta dukda ana bata daga gidansu.
•••
Yauma daga aiki be koma gida ba seya je school d'insu Nasreen,4pm lokacin yana tsaya a gate d'in yana tunanin yadda ze ganta.
Da'kyar mey gadi ya barshi ya shiga wani daga cikin malamanne ya kira Nasreen tazo.
"Kinsan wannan?" Suka tambayeta.
Seda ta tsaya na d'an lokaci tukun tace "Eh".
Wata daga cikin malaman tace " Ai gashi ma kamar su d'aya".