← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 33

Sashe 26

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

     " Uncle kaga yau Ummie ta 'kwace min chocolates d'ina ,guda biyu kawai ta bani nayi kuka amma bata bani ba". Nasreen ta fad'a.

     "Toh kiyi ha'kuri Ummie bata so kiyi ciwon ha'kori". Ahmad ya fad'a.

      " Ha'kori na zeyi ciwo ina sha dayawa?"

      "Eh". Ya amsa.

       Seda aka koma class tukun ta koma ciki Ahmad ya tafi, a hanya ya kira Reyhana a waya duk da kuwa yasan baza ta d'aga ba,kusan sau uku ya kira bata d'aga ba ya ha'kura.

      Wajajen 7:30pm bayan ya koma gida ya iske Umma a parlor, tafiya da zeyi gobe zuwa Lagos ya sanar mata.

    "Allah ya kaimu" Ta fad'a.  

     "Ameen". Ya amsa .

     Ya zaci zata tambayi kwana nawa zeyi amma yaji ba haka ba,a sanyaye ya mi'ke ze fita ta kirashi.

     " Ahmad ".

   Da sauri ya waiwayi " Na'am".Ya amsa.

     "Kwana nawa zakai a can?" Ta tambaya.

      "Kwana biyu". Ya amsa.

      "Toh bayan ka dawo zami wata magana da kai". Ta fad'a.

     " Toh Umma".Ya fad'a.

     Se bayan ya koma d'aki tukun ya shiga tunanin maganar da zatai masa."Ko mey zata ce? Ko akan Reyhana ne?" Ya tambaya a ransa.

     Da daddare ya had'a kayansa a suit case ,wayarsa ya d'auka ya kira Reyhana, kamar yadda yayi tsammani batai picking ba.

        Pick my call please, i want to talk to my daughter.

Text d'in dariya ma ita ya bata."Watoh gadara ma zeyi,lalle wuyansa ya isa yanka let see".Ta fad'a.

     Sake kiranta yayi karo na biyu,bakinta fal da magana ta shirya rashin mutunci ,ba jimawa tayi picking.

AR²💖

     Next page there is gonna be a special thing👄👄

    Pls comment,vote and share.luv u all💋

Jasko💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣8⃣

Ahmad yana sane ya fad'i haka dama so yake ta kulashi.

Shiru tayi lokacin da tayi picking ,yana jira yaji tayi magana amma shiru dan haka shi ya fara.

"Bata wayar koh". Ya fad'a.

" Seriously? master right?" Ta fad'a.

"Reyhana waya zaki bata yarinya tana son jin muryar babanta"

"Force me,gara ma kadena wannan mafarkin dan bata san da kaiba kadena wani shishshige mata atoh dan kwanannan seka dena ganinta".

" Ko kuma ke ki dena ganinta ba". Ahmad ya fad'a.

"Au haka ma zaka ce? Yaushe kasanta ma gabad'aya ? Sanda take bu'katarka ina kake?"

"Reyhana kidena fad'in haka ,yaushe zaki yarda dani ne? Believe me ba'a son rai na na d'au tsahon wannan lokutan banzo gareta ba,please i am sorry forgive me".

" You better stop apologizing".Ta fad'a cikin jin haushi.

"Ok then wazan tambaya Nasreen?"

"Don't ever try it,tana yarinyarta bazaka jagula mata lissafi ba"

"Ok toh naji,yanzu tana ina?" Ya tambaya.

"Mey zakai mata?"

"Gaisawa mana". Ya amsa.

" Tayi bacci ".Tayi 'karya.

"'Karya".Ya fad'a.

" Ni nake maka 'karya?"

"Au sorry".Ahmad ya fad'a kamar mey shirin yin dariya.

" Don't sorry me ".Ta fad'a.

Kafin ya sake wata maganar har ta katse wayar.Conversation d'in da sukai ba 'karamin dad'i yayi masa ba ,text ya tura mata kamar haka.

Am sorry Ummien Nasreen,goodnight 😘😘 to my Angel.I mean Nasreen

Check your whatapp pls..

Tana gama karancewa tayi tsaki abin nasa ya soma isarta dan taga alamar ya 'karo wula'kanci.

Da ta ajje wayar se kuma ta d'akko ta kunna data ta hau whatapp.Number d'inshi taga ya turo message tana bud'ewa taga image na teddy bear pink an rubuta

"for someone special❤

Reyhana:"Mey zanyi dashi?"

Ahmad: "Waya ce naki neh? na Baby na neh".

Reyhana: Toh meye na turo mini se ka bari idan ka had'u da ,'yar taka ka nuna mata"

Ahmad:"Bafa baby Nasreen ba,ki gane mana".

Reyhana:" Wai kai 'kalau kake? Wace babyn taka tukunna ma"

Ahmad:"Bafa ke nace ba,ina nufin...."

Reyhana:"Kai ya rage ma".

Daga haka ta sauka ta ajje wayar gefe ,shima ganin bata kai ya ajje wayar.

***
Tunda ya tafi Lagos be samu sunyi waya da ita ba sede yana turo mata apology text,kwanansa biyu ya dawo kano se bayan maghrib ya diro kano a ranar be samu yaje gidansu Reyhana ba.

Umma ta sakko yanzu ta dena fishin da koda ya tafi tana kiransa taji lafiyarsa.

Yau wajajen 10:30am ya biya makarantarsu Nasreen be jima ba ya komo gida ,daya gwada kiran Reyhana yaji switchoff.

Yana zaune Umma ta shigo d'akin,dama yana jira yaji tayi masa maganar da tace zasi bayan ya dawo kuma yaga bata yi ba.

Gefe guda ta samu ta zauna kan wani wani kujera.Gyaran murya tayi kafin ta soma magana.

"Kaga yanzu de baka da wata matsala da take a gabanka da zaka ce ta hanaka yin aure,da farko nayi tsammani na fara jin maganar daga gareka amma shiru shiyasa da kaina zan tambayeka akwai wacce kake da burin aura koh babu a yanzu?"

Tambayar Umma ba 'karamin razana shi tayi ba ,ba dan komai ba se dan baida amsar da zai bata.

"Baka ce komai ba". Cewar Umma.

" Uh..babu".Ya amsa yana sosa 'keya.

"Babu". Ta mamimaita a fili.

Dama haka take son ji dan ta dad'e da 'kudura wani abun daban ,da ace zece da akwai wata bata da hujja amma yanzu tunda babu komai zezo yadda take so.

" Toh mu muna da ta gida". Ta fad'a.

A rikice yace "Uhm?" Yana so ya tantace ko kunnensa neh beji dede ba.

"Nace akwai a gida,abune ya riga daya faru tun farko kuma dama Allah yayi da rabon 'ya shiyasa ba yadda za'ayi amma dama shiyasa so dayawa iyaye da kakanni suka fi gane auren gida gudun irin faruwar hakan ,d'an uwanka yafi sanin darajar ka da mutuncin ka ba kamar bare ba,kuma nasan wannan yarinyar bazata ta'ba wula'kanta ka ba yarinyace me hankali ".

Duk wannan maganganun da take shi ba sune damuwarsa ba kawai soyake yaji ta fad'i yarinya da take nufi.

" Kai kanka kasan halin yarinyarnan Zainab a zamaninnan masu hali irin nata tsirari ne".

"Zainab? Ni nace mata ina son Zainab?

"Toh dole seka ce?" Wata zuciyar ta fad'a masa.

"Amma Umma.." Be 'karasa ba ta katse shi.

"Wani uzurin zaka zake bayarwa? Zan baka gurguwar shawara ne kake tunani ? Kai shikenan kafi so ka cigaba da zama haka ,ka gama karatun,ka samu aiki mey kyau kuma mey kake bu'kata?" Ko wata 'karyar zaka sake yi min?" Ta 'kare fuskarta tana nuna alamar fushi.

Tuna yadda Umma bata iya fushi ba kuma baya so ya sake 'bata mata rai laifi goma da ashirin shiyasa yai shiru yana tunanin amsar da zata fito daga bakinsa.

"Umma duk yadda kika ce ,hakan ba damuwa bane Umma kuma nasan baza ki za'bamin wacce ba ta gari ba".

Umma taji dad'in amsarsa sosai ,tasan yin hakan ba 'karamin farantawa iyayen Zainab ze ba ,kuma zasu ga sun saka musu da tallafawa Ahmad samun aiki da mahaifinta yayi.

"Barka haka nake son ji ,zan kira kawunka miyi magana dashi anjima".

" Umma amma ita ai bata gama makaranta ba".Ahmad ya fad'a du dan ya samo mafita.

"Makaranta ai ba matsala bace abinda ta kusa gamawa ma ,koh Lagos d'in za'a tafi da 'Yar tawa ban sani ba". Cewar Umma cikeda zolayi.

Murmushin ya'ke kawai yayi dan hankalinsa ya d'aga.

Yana ji tana masa maganar ya soma gina wani plot dayake dashi kawai uhm yake amsata tunaninsa sam baya gun har ta fita.

Ya rasa wanne daga cikin abokanansa ze kira yaji sa'ida ,yasan sadiq dariya ma zeyi masa gwara Imran.

Koda ya kira imran ba wani support hakan ba'karamin sake bashi haushi yayi ba,yau yaga abu da girmansa za'ai masa auren dole sekace a 'kauye .Abinda yayi tunani a zuciyarsa kenan.

Ko abincin rana kasa ci yayi be fito daga d'aki ba se lokacin da taji Umma ta kirashi yaje ya d'akko Zainab daga makaranta.

A hankali yake tu'kin har ya isa makarantar ,yana parking ya kirata ya fad'a mata yana jiranta.

Ba'a wuce 5min ba ya hangota tana tahowa.Kallanta yayi tayi tana tahowa shi tunda yake be ta'ba kawota a ransa a matsayin matar da ze aura ba.

Yana wannan tunanin ta 'karaso har motar.Ita kallonta da yake yasa ta sunkuiyar dakai a tunaninta ko du cikin love ne.Se da ta bud'e 'kofar motar tukun ya dawo daga tunanin dayake.

"Yaya barka da rana". Ta fad'a sanda ta shigo.

" Yawwa ya school d'in?"Ya tambaya.

"Alhamdulillah". Ta amsa.

Daga haka be sake cewa komai ba har suka isa gida.

Yana shiga d'akinsa ya sake kiran Reyhana yayi sa'a akai picking.

" Hello".Yaji an fad'a cikin 'yar 'karamar murya.

"Nasreen?" Ya tambaya dan yaji kamar ita.

"Na'am". Ta amsa.

" Uncle neh".Ya fad'a.

"Laa! Uncle ,d'azu Auntynmu ta kawo ni gida kaina yana tayi mini ciwo nayi kuka". Nasreen ta fad'a.

" Ciwon kai kuma,ayya! Sorry kinji ,kinsha magani?" Ya tambaya.

"Eh Ummiena ta bani". Ta fad'a.

" Yanzu ya dena?" Ya tambaya.

"Eh".Ta amsa.

" Ina Ummienki?"Ya tambaya.

"Tana kitchen na kai mata?"

"A'a anjima". Ya fad'a dan yasan kashewa ma zatai.

Labarin school tayi ta bashi kafin daga bisani sukai sallama.

Nasreen da kanta taje har kitchen ta fad'a ma Reyhana tayi waya da Uncle

" Ban hanaki d'aga min kira ba?"

"Ummie Uncle ne fa". Ta fad'a.

" Karki sake kinji koh".Tayi warning d'inta danma tayi ciwon kai da se taja mata kunne.

°°°

Umma ba 'bata lokaci ta kira kawun Ahmad tayi masa bayanin komai bayan ta gama ta kira wata sister tata itama ta sanar mata da abinda ake ciki.

***
Ko sati d'aya ba'ai ba aka je neman auren Zainab,dududu wata uku aka sa Ahmad gani yake kamar mafarki kawai kallon su yake suna abinsu,Zainab murna a gurinta ba'a misaltawa.

Reyhana yau da kanta ta kai Nasreen makaranta ,daga nan zata biya school fees na Nasreen seji tayi an fad'a mata Ahmad ya biya.

"Watoh ta nan kuma yanzu ze 'bullo". Reyhana ta fad'a.

Tana wannan batun sega kiran Ikram,tana d'agawa taji suna asibiti Sageer ba lafiya,da sauri-sauri ta shiga. mota se asibiti.

Mommy, Abba se Ikram sinyi cirko-cirko a bakin 'kofar d'akin da aka shigar dashi.

" Mommy meya sameshi?" Ta tambaya.

"Bassam ne ya shiga d'akinsa ze Kira shi ya tarar dashi a sume".Cewar Mommy.

" Subhanallahi".Reyhana ta furta.

Bata sake wata maganar ba sega doctor ya fito daga d'akin.
Chapter 26 · 0% Book details