← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 33

Sashe 27

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da Abba da Mommy ya kira ya zaunar dasu yake tambayarsu tsahon lokacin da Sageer shafe baida lafiya

.Nan Mommy ta zayyane masa irin halin da suka tsince shi.

"Hajiya wannan yaron depression yana nema ya kamashi,ga dukkan alamu damuwa ta mishi yawa".

" Subhanallahi".Suka furta a tare kowannensu fuskarsa da damuwa.

"Amma yanzu ya samu sa'uki InshaAllahu zamu cigaba da bashi kulawa kafin a sallame ku". Doc ya fad'a.

" Toh muna godiya likita".Cewar Abba kafin daga bisani suka fita.

AR²💖

Pls comment,vote and share.Love u all❤

Jasko💕
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣9⃣

  Sageer bayan kamar 30min ya farka,lokacinda suka shiga be bari ya had'a ido dasu ba ya kawar da kansa.

         Dukkansu suna tunanin wannan wata damuwa ce ke damun Sageer data saka shi ya shiga cikin wannan halin banda Reyhana da ita tasan komai.

                    ***
      Around 3pm bayan ya dawo gida ya tarar da Sadiq,yana parlor suna hira da Umma.Ahmad suna gaisawa ya koma d'akinsa seda ya watsa ruwa tukun ya fito zuwa parlor lokacin Umma bata ciki.

     "Abokina yane?" Cewar Sadiq.

     Daga yadda yayi magana ya gano d'aya daga cikin rashin mutunci ne irin na Sadiq yasan Umma ta zayyane masa komai.

       Banza yayi masa bece komai ba sema wayarsa daya d'akko yana tapping.

      "Yanzu sede naji magana a wajen Umma instead ka same ni ka fad'a mini da kanka?" Sadiq ya fad'a.

       "Ni nasan ma mey kake nufi". Ahmad ya fad'a yana cigaba da danna wayarsa.

      " Zaka gane neh  na Zainab ".Sadiq ya fad'a yana 'kare maganar da dariya.

       " Kai! zan zageka".Cewar Ahmad wannan karan ba waya  yake kalla ba.

      "Seda kar a kuma, bani labari mana mey kake shirya mana neh?"

       "Bansani ba".Ahmad ya fad'a.

       " Munafiki kana so kana kaiwa kasuwa ,kayi ka gama".Sadiq ya fad'a.

       "Base ka ganni ba zakai". Ahmad ya fad'a yana mi'kewa yabar d'akin.

       " Ina kuma zaka ,koh ka manta zaka d'akko Zainab".Ya jiyo Umma ta fad'a.

        "Nima ze ragen hanya" Sadiq ya fad'a yana daga parlor.

       "Toh kaji". Umma ta fad'a.

      Ahmad a cukule ya fita banda Sadiq daya biyo shi yana sake 'kular dashi.Dama ba wani rage hanya dan har school dashi aka je d'akko Zainab se bayan suna hanyar dawowa ya sauka.

        Ko shiga gida Ahmad beyi ba ya tafi makarantar su Nasreen ,seda ya tsaya yayi mata siya-siye.

       •••

    Sageer kwanansu biyu a asibiti aka sallamesu har yanzu be fad'a musu abinda ke damunsa ba.Se bayan sun dawo gida Mommy ta titsiye Reyhana dan taga alamar akwai abinda take 'boyewa.

        "Mommy wata yarinya fa yake so shine iyayenta suka 'ki ,su cousin d'inta suke son su bata". Reyhana ta fad'a.

       " Yanzu dama akan haka ya shiga wannan halin !?"Cewar Mommy.

       "Tun yaushe akai hakan baku fad'a ba?" Ta tambaya.

        "An d'an dad'e". Ta amsa.

        " Yayi kyau da 'boye-'boye ga result nan ai kungani ze kashe kansa akan wata yarinya ".

        Mommy d'akin Abba taje ta zayyane masa komai, shi fad'a yayi tayi." Akan wata soyayya yana nema ya samu shiga cikin wani yanayi sakarai kawai".

       Har d'akinsa Abba yaje, Mommy tana tsayar dashi amma ko sauraronta beyi ba.

        "Kai yanzu dama wannan abun ne yake damunka kabi ka wahalar da mutane!?"

        Sageer daya sunkuyar dakai ko 'kala ya'ki fad'a yana jin Abba yana fad'a.

       "Karka fasa damuwar tunda a kanka aka fara soyayya baban soyayya kaji".Abba ya fad'a tare da ficewa.

        Gidan tsit kowa ya shige d'akinsa Mommy an barta da tunani,a zuciyarta tana fad'in." Kamar d'anta za'a guje shi,meya rasa yaranta ba talaka ba da iliminsa kuma shi ba muni ba kuma baya shaye-shaye ko wani abu makamancin haka wane dalilin ne zesa a 'kishi ?" Abinda yake ta mata yawo aka.

                °°°
        8:34pm Ahmad bayan ya dawo daga masjid yai dialing numbern Reyhana kusan sau uku ya kira amma batai picking ba.Da farko ajje wayar yayi amma wata zuciyarta sake zigashi ,haka ya sake kiranta still batai picking ba be gaji ba ya cigaba da kira ,yafi sau 15 .

     Reyhana jin ya takura mata banda silent da tasa ba dama tayi anfani da wayar ko yaya ta soma tapping seta ga kiransa.

       "Lafiya?" Cewar Reyhana bayan ta d'aga wayar.

       "Ina fa lafiya". Ahmad ya fad'a.

       " Toh se aka yi yaya?" Ta tambaya.

       "Ina Nasreen?" Ya tambaya.

        "Tayi bacci". Ta amsa.

         " Toh ki shafa min kanta".

         "Bata bu'katar hakan tunda kullum babarta tana mata addu'a".

          " Toh mungode da hakan".Ya fad'a.

      Shiru ba wanda ya sake cewa komai kuma ba wanda ya katse.

      "Reyhana". Ya kira sunanta cikin sanyayyar murya.

      "Meye yanzu kuma?" Ta tambaya.

       "Just want to say sorry". Ya fad'a.

       " For what?" Ta tambaya kamar bata gane inda ya dosa ba.

       "For everything".Ya amsa.

         " Is that all?"Ta tambaya .

          "No". Ya fad'a.

           "Meya rage?"

           "Goodnight". Ya fad'a.

         Hanging tayi ba tare da ta sake magana ba kuma bata jira shima ya sake yi ba.

         Wayar kawai yabi da kallo yana murmushi sannan ya ajje ta a gefe.

         Reyhana bayan data katse wayar bata ajje ba seda ta 'karewa numbern kallo tukun ta maido da kallonta kan Nasreen da take ta bacci.

                  ***
      Mommy da ta kwana da damuwar d'anta a rai da safe bata iya ha'kuri ba dan haka taje tana ro'kon Abba daya yi wani abun akai.

       " Ni kike so na kwashi 'kafa kenan naje nace a bawa d'ana yarinyar!?"

        "Ba haka nake nufi ba amma de idan aka tura manya ai zasu ga da gaske ake koh" Mommy ta fad'a.

       "Ke baki ji bayanin bane since cousin d'inta zasu bata ,toh kuma se 'ka'ka zaki iya hanasu ne?"

       "Ya kake magana haka  kasani ko su chanja ra'ayinsu".

        " Saboda d'anki shine autan maza koh?"Cewar Abba.

       "Dan Allah na ro'ke ka ,ka taimaka kayiwa 'yan uwanka magana".

       " Naji shikenan amma inde basu amince ba bazan sake sa 'yan uwana a wannan mganar ba".

        "Na yarda".Mommy ta fad'a da sauri.

          Aiko hakan akai ,Sageer ya basu address d'in gidansu yarinyar suka je sukai magana da mahaifin yarinyar.

       Mommy tun basu dawo ba ta sakko 'kasa tana jiran su dawo taji ya aka kaya.Shima Sageer yana d'aki duk abinda ake hankalinsa nakai amma ya kasa fitowa dan kunya.

      Seda aka shafe kusan 30 min sega su sun dawo Mommy ziba ido tayi tana jira taga sun zauna taji bayani.

  °°°

Ahmad daga aiki ya biya d'akko Zainab daga makaranta,a da yana so idan ya maida ita gida yaje makarantar su Nasreen amma kuma lokaci baze bari ba dan lokacin tashin su ya kusa,hakan nan ya tafi da Zainab makarantarsu Nasreen.

     Ita de taga an baud'e hanya amma bata tambaya ba,shima kuma beyi bayani ba har suka isa school d'in.

     Lokacin har an tashe su sun fara fitowa,chan sega Nasreen ta fito.Yana ganin fitowarta ya fita shima.

      Da gudu ta 'karaso inda yake tana tsalle." Uncle !"

     Zainab da take daga mota tana hangensu ,tana ganin Nasreen ta kawo ita ce 'yar tashi a ranta.

      "Uncle dawa yau kazo?" Ta tambaya tana hangen Zainab dake mota.

       Waigowa yayi ya kalli Zainab tukun ya juyo da kallonsa kan Nasreen.

       "Anty ce". Ya amsa.

       " Anty sunanta?" Ta tambaya.

        "Eh". Ya amsa.

     Da sauri ta 'karaso motar harda 'ko'karin bud'ewa,Zainab ganin haka yasa itama ta bud'e mata 'kofar.

      " Ina kwana".Ta gaisheta.

      Zainab tana murmushi ta amsa "Lafiya lau har yanzu safiya ce kenan" Ta fad'a tana murmushi.

       "Sunanki Anty koh?" Nasreen ta fad'a.

        "Eh sunana Anty Zainab". Ta fad'a.

       " Anty Zainab".Nasreen ta  maimaita.

        "Eh,an tashi daga makaranta koh".

        " Eh yanzu driver zezo ya d'auke mu".Ta fad'a.

         Hira sosai tayi tayi da Zainab kamar dama ta santa,seda driver yazo tukun ta tafi suma suka komo gida a hanya Zainab take maganar Nasreen,kad'an-kad'an yana amsata.

   °°°

     Abba ne ya soma tambayarsu ya ta kaya,mommy tayi 'kuri tana ji.

     "Ba yadda bami da mahaifinta amma ya'ki, mahaifinta ya riga ya tsaida magana yace mu baku ha'kuri da shima yaron". Wani daga cikin 'kanin Abba ya fad'a.

      Wani takaici ne ya ziyarci Mommy tana mamakin irin wannan mutanen daga baya ma tashi tayi daga parlon ba tare da ta gama sauraran su ba dan ba wata kalma da zata sa taji sanyi.

       Nasreen kuwa tana dawowa gida koh uniform bata cire ba ta soma bawa Reyhana labarin Uncle da Anty Zainab.

       " Nasreen kika ce Anty Zainab tare suka zo?" Ta tambaya.

        "Eh da uncle suka zo ,na nuna mata classwork d'in da Anty ta bamu a aji". Ta fad'a.

     Reyhana ko 'karanshe labarin ma bata ji ba tuni ta tafi tunani.Tunanin last ganinta da Zainab d'in ma ta Shiva lokacin da suka je Zaria suka taho da ita ta zauna gidan Umma.

     " Dududu bata fi 13yrs ba lokacin ".Ta fad'a a zuciyarta.

     " Toh haka kuma zatai ta zama after all shekaru shida da suka wuce!?" Wani 'bangeren taji zuciyarta ta fad'a.

      "Atleast fa tayi 19 koh 20 yanzu,toh koh...anya..kai no..ko ya aureta ma? "

       Lokaci guda taji kanta ya fara d'aukan zafi,haushin sa ne ya sake kamata ma watoh ya raina mata hankali shine harda matar daya aura Zeke zuwa wajen 'yarta.

       Tana wannan batun sega kiran Ahmad, a 'kule ta d'auki wayar tare da switching off."Zaka ga wacce zata d'aga ,watoh ga sakarya".Ta fad'a a fili.

AR²💖

        *Pls comment vote and share.💋Next page there is gonna be a pic of...guess!*

Jasko💕

? *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣0⃣

Ahmad beyi mamakin
'kin picking call d'insa da Reyhana ta'ki yi ba kusan daman an saba shiyasa be kawo komai a ransa ba.

Ita kuwa Reyhana ta kasa samin sukuni se tunane-tunane takeyi ,ranar batai cikakken bacci ba.

***

An d'auki kwana biyu Reyhana bata picking call d'insa text kuwa baya gajiya haka zeta tura mata tana ignoring.

Yau da safe tana shirya Nasreen se ro'konta take barta taje gidansu Anty Zainab.

"Ko zaki d'ige bazaki ba gara ma kidena tunanin zuwa". Reyhana ta fad'a.

Chono baki tayi tana buntsire-bintsire baki." Tashi mije kiyi breakfast ki tafi makaranta".Reyhana ta fad'a

"Toh". Ta amsa.
Chapter 27 · 0% Book details