Sashe 16
Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Reyhana tana d'aki tana shirya Nasreen Ahmad ya kira ,wani tausayinsa taji dan yau kusan kwana biyu Mommy ta hanata picking call d'insa.
"Reyhana". Ya kira sunanta bayan ta d'aga.
" Yaya".Ta kira sunansa itama.
"Are you OK?" Ya tambayeta.
"No am not". Ta amsasa idanuwanta na tsiyayar hawaye.
" Reyhana ki dena kuka please ".Ya fad'a
Bata 'kara magana ba sega Mommy ta shigo.Wata uwar harara Mommy ta watsa mata dan haka ta katse wayar.
Mommy 'karasowa inda wayar take ta d'auka tayi switching off ba tare da tayi magana ba ta fita.
An d'au kusan month da arba'in ,ba abunda ya chanza Mommy haryanzu tana kan bakarta dan yanzu ta gaji da zama a haka da ake so take Ahmad ya rubutowa Reyhana takardarta.
Da kanta yau ta d'au 'kafa taje gidansu Ahmad,Umma kad'ai ta samu a gidan.
Bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata abinda ya kawota.
" Mommyn Reyhana ba wanda yasan gobe gabaki d'ayanmu,shiyasa nake ro'konki da ki sake bashi dama ko ze samu wani aikin".Umma ta fad'a.
"Umman Ahmad banzo nan ba dan mu sake tattaunawa akan maganarnan ba ,takardarta nazo kar'ba".Mommy ta fad'a.
Hakan ba 'karamin 'konawa Umma rai yayi ba ,tasan ta d'areta nesa ba kusa ba danma bata haifi Ahmad da wuri ba amma shine take mata irin wannan maganar cikin kakkausan harshe sekace 'yarta ko si'arta.
" Amma yanzu de ai kinga yaron baya nan koh?" Cewar Umma.
"Toh ai shiyasa na zo sanar wa da mahaifiyarsa wata'kila koya rubuta". Mommy ta fad'a.
" Shikenan inde takardarta ce ze kawo mata da kansa".Umma ta fad'a ranta a 'bace.
Tashi tayi Mommy ta fita disappointed dan taso ace Ahmad yana nan.
Umma kawai bin bayan ta da kallo tayi ta girgiza kai.
Ahmad yana wajen aikinsa amma hankalinsa yana gun Reyhana baida tunani sai nata.
Wajajen 4pm Ahmad ya shigo gidan dan yanzu kusan koyaushe yana gidan kwana ne yake maidashi gidansa.
Umma seda taga ya kammala cin abincin sannan tayi masa maganar zuwan Mommy.
"Ahmad yaushe zaka bata takardarta?"Umma ta tambaya.
"Umma ya kike fad'an haka?" Cewar Ahmad.
"Kai baka gaji da wannan abun ba ,lokaci yayi da zaka ha'kura Ahmad babu yanda zami da 'kaddara". Umma ta fad'a.
" Umma saki fa ba abune mey sau'ki ba".Ahmad ya fad'a.
"Ka fiso a cigaba da zuwa ana cimin mutunci ko,har yanzu baka gaji da wula'kanci ba? Kokuwa so kake se an kai maganar kotu?" Cewar Mommy, daga yadda take maganar ya gano tana cikin 'bacin rai.
"Umma mey tace miki?" Ya tambaya lokaci guda zuciyarta ta fara tafasa dan zaey iya jure komai amma banda wulan'kanta mahaifiyarsa
"Jin mey tace mini ba shine ba kawai kayi ha'kuri ka sawwa'ke mata kowa ya huta". Umma ta fad'a.
Kai kawai ya kad'a ba tare da yace komai ba ya fita.
Gidansa ya nufa,d'akinsu ya shiga ya bud'e wardrobe d'in wasu kayan Reyhana da bata tafi dashi ba ya d'auka yana sha'kar 'kamshin turarenta ,take hawaye ya gangaro fuskarsa.Tun farkon had'uwarsu da ita ya tuna da auren su,sanda tana laulayi,da tafiyarta gida.
" Shine 'karshen zamanta a gidana kenan?"Ya tamabayi kansa.
Tuna maganar Umma da yayi yasa ya janyo drawer ta gadon ,takarda da biro ya d'akko ,se 'karewa takardar kallo yake a zuciyarsa yana jin nauyin rubuta mata saki.
Ya shafe kusan 20min kafin ya d'ora biro a kai.
Ni Ahmad Yusuf, yau laraba ././... Ya rubuta date.Na saki mata ta Reyhana saki d'aya.
Yana gama rubutawa yai folding d'inta.
Seda yasha kukansa tukun ya fito daga gidan,be tsaya a ko ina ba se gidansu Reyhana. A 'kofar gida ya tarar da Sageer ,cikin mutuntawa suka gaisa ya mi'ka masa takardar dan bayajin zai iya bata hannu da hannu.
Yana bashi ya tafi,shikanshi Sageer jiyake kamar yai kuka.Ko ba'a fad'a ba yasan mene,a d'aki ya isketa tana ta lalla'ba Nasreen tayi bacci.
Ganin Sageer 'ki'kam a tsaye ya kasa magana amma fuskarsa da damuwa.
"Sageer meya faru?" Ta tambaya.
Takardar ya mi'ka mata ba tare da yace komai ba ya fita.
A sanyaye ta bud'e takardar gwiwarta tayi sanyi...
AR²💖
Jasko💕
Pls share.
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 1⃣7⃣
Safar da take hannunta ta Nasreen ta saki a 'kasa,kukan ma ta kasa.
"Ahmad ya sakeni?" Abinda take ta nanatawa kamar zautacciya.
Kuka mara sauti ta soma,ita kuwa Nasreen se wuri wuri da ido take tana d'aga 'kafafuwa sama.
Ahmad kuwa daga gidansu Reyhana gidansa ya koma yai zaman dirshan ,hotunan bikinsu ya d'auko yana ta kalla harda murmushin yake.
Umma tayi tsammanin dawowarsa amma taji shiru,da ta kira wayarsa a kashe taji dan kuwa baya son jin kowa komai kawai yafison ya zauna shi kad'ai.
Mommy da maghrib bayan tayi sallah ta shiga d'akin Reyhana lokacin tana toilet.Har zata fita ta hangi takardar a kan gado.
A hankali ta 'karasa ta d'auka,koda ta karanta wani sanyi taji ya ratsa ta a zuciyarta tace"Alhamdulillah,an rabu da 'kaya".
Hannunta ri'ke da takardar Reyhana ta fito fuskarta ba annuri da ka ganta za kasan tana cikin damuwa.
Mommy ita kanta rasa abinda zata ce mata tayi dan tasan a wannan lokacin tana tare da 'bacin rai saboda haka Mommy ta ajje takardar ta fice.
Abba kuwa da ya dawo Mommy ko kunya haka ta shiga d'akinsa ta sanar masa.
"Toh yanzu hankalinki ya kwanta koh?" Abba ya fad'a
Mommy shiru tayi bata ce komai ba se turo baki datai a zuciyarta kuwa tana mey jin dad'i.
Ahmad se wajen 10:30am tukun ya koma gidan Umma da hankalinta ya tashi.
"Kai kuwa ina ka shiga ina kiranka a kashe wayar?" Umma ta tambaya.
"Naje gida neh". Ya amsa ciki ciki.
" Du ka tayar min da hankali". Umma ta fad'a.
"Kiyi ha'kuri". Ahmad ya fad'a.
" Abinci fa?" Ta tambaya.
"Na 'koshi ". Ya amsa ya shige d'aki.
Kai kawai ta girgiza ta koma d'aki.
Daren ranar daga Reyhana har Ahmad ba wanda ya iya bacci,daga ya fara gyangyad'i seyai mafarkin Reyhana tana kuka a firgice yake tashi.
***
2weeks later
Mommy itada Anty Asma'u sukaje gidan Ahmad suka sa aka kwaso kayanta ,dama kud'in hayar ya kusan 'karewa dan haka suna kwashe kayansu Ahmad ya dan'kawa mey gida gidansa.Shi kuwa ya komo gidan Umma.
9:46pm yana rigingine ya 'kurawa ceiling ido yana tuna last maganar da sukai da Reyhana a waya.
** Waiwaye**
" Reyhana am so sorry, I have no choice ".
" Yaya na fahimta,stop apologizing ".Reyhana ta fad'a.
"Wannan itace 'kaddararmu". Ahmad ya fad'a.
Da'kyar ya iya rintse idonsa ba isashshen bacci yake ba yanzu.
Mommy kuwa abin Reyhana ya fara isarta tun sanda Ahmad ya bata takardar ta ta dena sakin fuska ,fitowa parlour ma wataran se a wuni bata fito ba.
Tana gyara gado dan shirin kwanciya Mommy ta shiga d'akin.
Waje ta samu ta zauna,bayan data d'auki Nasreen da har lokacin idonta biyu.
" Reyhana ".Ta kira sunanta.
" Uhm".Ta amsa tana cigaba da abinda take.
"Reyhana saboda nasa Ahmad ya rabu dake shine bakya son yi mini magana?" Cewar Mommy.
"Mommy ba haka bane".Ta fad'a tabar abinda take.
" Toh yayane?"Mommy ta tambaya.
'Karasowa tayi kusa da Mommy ta zauna gefen gado ta zauna opposite da Mommy.
"Mommy taya za'ai na'ki yi miki magana akan haka". Reyhana ta fad'a.
"Toh ya akai kin chanja bakya shiga cikin 'kannanki ko abinci ma bakya ci damu kinga dole nayi tunani ko kina gab..". Mommy bata 'karasa ba Reyhana ta katse ta.
" Mommy kidena fad'in haka,dan Allah kiyi ha'kuri amma banyi hakan dan na 'batamiki ba ,na bari ".Reyhana ta fad'a tare da tasowa ta zauna gefen Mommy tasa hannunta ta ri'ko yatsinta tana murzawa.
" Kiyi ha'kuri Mommy ".Reyhana ta fad'a hawaye na sakkowa daga idanunta.
Mommy kafad'arta ta d'ora kan Reyhana tana tapping bayanta" Ya isa kukan".Ta fad'a.
Kai kawai take kad'awa ba tare da tace komai ba.
Daga wannan lokacin Reyhana ta cigaba da sakewa dasu,sun dawo kamar da tana sakkowa parlourn suyi kallo duk wata damuwarta ta danne a ranta.
Ta 'bangaren Ahmad a 'yan kwanakinnan yakan fita majalissa wajen abokansa,ko be fito ba Sadiq abokinsa da kansa yana shigowa ya tayashi hira kuma yana kwantar masa da hankali.
Yau d'inma ganin be fito ba yasa sadiq ya zo gidan.A d'aki ya tarar dashi ,wayarsa ce a hannunsa amma bawai tapping yake ba kawai wasa da ita yake a hannunsa amma hankalinsa baya gun.
"Maza! Yane ka zauna a d'aki kai d'aya baka fito ba?" Sadiq ya tambaya.
A kasalance ya d'ago da kansa ya kalli sadiq.
"Sadiq". Ya kira sunansa.
Zama yayi kusa da shi kan katifarsa.
" Ahmad kai baka gajiya neh? Koyaushe cikin tunani haba mana ya kamata ka dena damun kanka haka".Sadiq ya fad'a.
"Sadiq baza ka gane bane,bakasan yanda nake ji bane". Ahmad ya fad'a.
" Ai gashi se rama kake,lafiyarka nake jiye ma se kace ba namiji ba duk wani abu daya sami mutum qaddararsa ce haka ba yadda zami,yin haka ba abinda ze 'karama illa kashe maka zuciya".Sadiq ya fad'a.
"Toh naji".Cewar Ahmad yana gyara kwanciyarsa.
" Ni da zaka bi shawara ta ma da ka mance da wannan damuwar".Sadiq ya fad'a.
"Na mance" Ahmad ya maimaita cikeda rainin hankali.
"Yes,akwai wani scholarship da naji ana cikewa na cyprus ,abinda yasa banyi ba saboda waec d'ina banda English ,kai kuwa naga kana da result mey kyau why not kai applying?"
"Mtchww! Ina cikin wannan yanayin zakai min maganar scholarship". Ahmad ya fad'a.
" Cigaba ne fa ,wai kai shikenan ka kashe rayuwarka ko meh,rabuwa da Reyhana baya nufin yin destroying life d'inka koh ita ance ma haka zata zauna tayi ta damuwa kamar yadda kake ?" Sadiq ya fad'a cikin fushi.
"Ni kaga rabu dani". Ya fad'a.
"Karka saurareni d'in rago kawai ". Sadiq ya fad'a tare da talle masa tafin 'kafarsa ya fita.
Ahmad ya d'au pillow da niyyar cilla masa yaga ya fice.
Washegari da safe koda ya gaisheda Umma yaji tayi masa maganar da Sadiq yayi mishi jiya.
" So zuwa yayi ya fad'a mata".Ahmad ya fad'a a ransa.
"Umma ki rabu dashi shirmensa ne". Cewar Ahmad.
" Kaide kake shirme,ca akai ma kowa irinka neh da be iya ri'ke 'kaddara ba".Umma ta fad'a.
"Reyhana". Ya kira sunanta bayan ta d'aga.
" Yaya".Ta kira sunansa itama.
"Are you OK?" Ya tambayeta.
"No am not". Ta amsasa idanuwanta na tsiyayar hawaye.
" Reyhana ki dena kuka please ".Ya fad'a
Bata 'kara magana ba sega Mommy ta shigo.Wata uwar harara Mommy ta watsa mata dan haka ta katse wayar.
Mommy 'karasowa inda wayar take ta d'auka tayi switching off ba tare da tayi magana ba ta fita.
An d'au kusan month da arba'in ,ba abunda ya chanza Mommy haryanzu tana kan bakarta dan yanzu ta gaji da zama a haka da ake so take Ahmad ya rubutowa Reyhana takardarta.
Da kanta yau ta d'au 'kafa taje gidansu Ahmad,Umma kad'ai ta samu a gidan.
Bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata abinda ya kawota.
" Mommyn Reyhana ba wanda yasan gobe gabaki d'ayanmu,shiyasa nake ro'konki da ki sake bashi dama ko ze samu wani aikin".Umma ta fad'a.
"Umman Ahmad banzo nan ba dan mu sake tattaunawa akan maganarnan ba ,takardarta nazo kar'ba".Mommy ta fad'a.
Hakan ba 'karamin 'konawa Umma rai yayi ba ,tasan ta d'areta nesa ba kusa ba danma bata haifi Ahmad da wuri ba amma shine take mata irin wannan maganar cikin kakkausan harshe sekace 'yarta ko si'arta.
" Amma yanzu de ai kinga yaron baya nan koh?" Cewar Umma.
"Toh ai shiyasa na zo sanar wa da mahaifiyarsa wata'kila koya rubuta". Mommy ta fad'a.
" Shikenan inde takardarta ce ze kawo mata da kansa".Umma ta fad'a ranta a 'bace.
Tashi tayi Mommy ta fita disappointed dan taso ace Ahmad yana nan.
Umma kawai bin bayan ta da kallo tayi ta girgiza kai.
Ahmad yana wajen aikinsa amma hankalinsa yana gun Reyhana baida tunani sai nata.
Wajajen 4pm Ahmad ya shigo gidan dan yanzu kusan koyaushe yana gidan kwana ne yake maidashi gidansa.
Umma seda taga ya kammala cin abincin sannan tayi masa maganar zuwan Mommy.
"Ahmad yaushe zaka bata takardarta?"Umma ta tambaya.
"Umma ya kike fad'an haka?" Cewar Ahmad.
"Kai baka gaji da wannan abun ba ,lokaci yayi da zaka ha'kura Ahmad babu yanda zami da 'kaddara". Umma ta fad'a.
" Umma saki fa ba abune mey sau'ki ba".Ahmad ya fad'a.
"Ka fiso a cigaba da zuwa ana cimin mutunci ko,har yanzu baka gaji da wula'kanci ba? Kokuwa so kake se an kai maganar kotu?" Cewar Mommy, daga yadda take maganar ya gano tana cikin 'bacin rai.
"Umma mey tace miki?" Ya tambaya lokaci guda zuciyarta ta fara tafasa dan zaey iya jure komai amma banda wulan'kanta mahaifiyarsa
"Jin mey tace mini ba shine ba kawai kayi ha'kuri ka sawwa'ke mata kowa ya huta". Umma ta fad'a.
Kai kawai ya kad'a ba tare da yace komai ba ya fita.
Gidansa ya nufa,d'akinsu ya shiga ya bud'e wardrobe d'in wasu kayan Reyhana da bata tafi dashi ba ya d'auka yana sha'kar 'kamshin turarenta ,take hawaye ya gangaro fuskarsa.Tun farkon had'uwarsu da ita ya tuna da auren su,sanda tana laulayi,da tafiyarta gida.
" Shine 'karshen zamanta a gidana kenan?"Ya tamabayi kansa.
Tuna maganar Umma da yayi yasa ya janyo drawer ta gadon ,takarda da biro ya d'akko ,se 'karewa takardar kallo yake a zuciyarsa yana jin nauyin rubuta mata saki.
Ya shafe kusan 20min kafin ya d'ora biro a kai.
Ni Ahmad Yusuf, yau laraba ././... Ya rubuta date.Na saki mata ta Reyhana saki d'aya.
Yana gama rubutawa yai folding d'inta.
Seda yasha kukansa tukun ya fito daga gidan,be tsaya a ko ina ba se gidansu Reyhana. A 'kofar gida ya tarar da Sageer ,cikin mutuntawa suka gaisa ya mi'ka masa takardar dan bayajin zai iya bata hannu da hannu.
Yana bashi ya tafi,shikanshi Sageer jiyake kamar yai kuka.Ko ba'a fad'a ba yasan mene,a d'aki ya isketa tana ta lalla'ba Nasreen tayi bacci.
Ganin Sageer 'ki'kam a tsaye ya kasa magana amma fuskarsa da damuwa.
"Sageer meya faru?" Ta tambaya.
Takardar ya mi'ka mata ba tare da yace komai ba ya fita.
A sanyaye ta bud'e takardar gwiwarta tayi sanyi...
AR²💖
Jasko💕
Pls share.
🎍 *ARZI'KI RABO*🎍
*WRITTEN BY DIJENSY*
*WATTPAD @dijensy*
🅿 1⃣7⃣
Safar da take hannunta ta Nasreen ta saki a 'kasa,kukan ma ta kasa.
"Ahmad ya sakeni?" Abinda take ta nanatawa kamar zautacciya.
Kuka mara sauti ta soma,ita kuwa Nasreen se wuri wuri da ido take tana d'aga 'kafafuwa sama.
Ahmad kuwa daga gidansu Reyhana gidansa ya koma yai zaman dirshan ,hotunan bikinsu ya d'auko yana ta kalla harda murmushin yake.
Umma tayi tsammanin dawowarsa amma taji shiru,da ta kira wayarsa a kashe taji dan kuwa baya son jin kowa komai kawai yafison ya zauna shi kad'ai.
Mommy da maghrib bayan tayi sallah ta shiga d'akin Reyhana lokacin tana toilet.Har zata fita ta hangi takardar a kan gado.
A hankali ta 'karasa ta d'auka,koda ta karanta wani sanyi taji ya ratsa ta a zuciyarta tace"Alhamdulillah,an rabu da 'kaya".
Hannunta ri'ke da takardar Reyhana ta fito fuskarta ba annuri da ka ganta za kasan tana cikin damuwa.
Mommy ita kanta rasa abinda zata ce mata tayi dan tasan a wannan lokacin tana tare da 'bacin rai saboda haka Mommy ta ajje takardar ta fice.
Abba kuwa da ya dawo Mommy ko kunya haka ta shiga d'akinsa ta sanar masa.
"Toh yanzu hankalinki ya kwanta koh?" Abba ya fad'a
Mommy shiru tayi bata ce komai ba se turo baki datai a zuciyarta kuwa tana mey jin dad'i.
Ahmad se wajen 10:30am tukun ya koma gidan Umma da hankalinta ya tashi.
"Kai kuwa ina ka shiga ina kiranka a kashe wayar?" Umma ta tambaya.
"Naje gida neh". Ya amsa ciki ciki.
" Du ka tayar min da hankali". Umma ta fad'a.
"Kiyi ha'kuri". Ahmad ya fad'a.
" Abinci fa?" Ta tambaya.
"Na 'koshi ". Ya amsa ya shige d'aki.
Kai kawai ta girgiza ta koma d'aki.
Daren ranar daga Reyhana har Ahmad ba wanda ya iya bacci,daga ya fara gyangyad'i seyai mafarkin Reyhana tana kuka a firgice yake tashi.
***
2weeks later
Mommy itada Anty Asma'u sukaje gidan Ahmad suka sa aka kwaso kayanta ,dama kud'in hayar ya kusan 'karewa dan haka suna kwashe kayansu Ahmad ya dan'kawa mey gida gidansa.Shi kuwa ya komo gidan Umma.
9:46pm yana rigingine ya 'kurawa ceiling ido yana tuna last maganar da sukai da Reyhana a waya.
** Waiwaye**
" Reyhana am so sorry, I have no choice ".
" Yaya na fahimta,stop apologizing ".Reyhana ta fad'a.
"Wannan itace 'kaddararmu". Ahmad ya fad'a.
Da'kyar ya iya rintse idonsa ba isashshen bacci yake ba yanzu.
Mommy kuwa abin Reyhana ya fara isarta tun sanda Ahmad ya bata takardar ta ta dena sakin fuska ,fitowa parlour ma wataran se a wuni bata fito ba.
Tana gyara gado dan shirin kwanciya Mommy ta shiga d'akin.
Waje ta samu ta zauna,bayan data d'auki Nasreen da har lokacin idonta biyu.
" Reyhana ".Ta kira sunanta.
" Uhm".Ta amsa tana cigaba da abinda take.
"Reyhana saboda nasa Ahmad ya rabu dake shine bakya son yi mini magana?" Cewar Mommy.
"Mommy ba haka bane".Ta fad'a tabar abinda take.
" Toh yayane?"Mommy ta tambaya.
'Karasowa tayi kusa da Mommy ta zauna gefen gado ta zauna opposite da Mommy.
"Mommy taya za'ai na'ki yi miki magana akan haka". Reyhana ta fad'a.
"Toh ya akai kin chanja bakya shiga cikin 'kannanki ko abinci ma bakya ci damu kinga dole nayi tunani ko kina gab..". Mommy bata 'karasa ba Reyhana ta katse ta.
" Mommy kidena fad'in haka,dan Allah kiyi ha'kuri amma banyi hakan dan na 'batamiki ba ,na bari ".Reyhana ta fad'a tare da tasowa ta zauna gefen Mommy tasa hannunta ta ri'ko yatsinta tana murzawa.
" Kiyi ha'kuri Mommy ".Reyhana ta fad'a hawaye na sakkowa daga idanunta.
Mommy kafad'arta ta d'ora kan Reyhana tana tapping bayanta" Ya isa kukan".Ta fad'a.
Kai kawai take kad'awa ba tare da tace komai ba.
Daga wannan lokacin Reyhana ta cigaba da sakewa dasu,sun dawo kamar da tana sakkowa parlourn suyi kallo duk wata damuwarta ta danne a ranta.
Ta 'bangaren Ahmad a 'yan kwanakinnan yakan fita majalissa wajen abokansa,ko be fito ba Sadiq abokinsa da kansa yana shigowa ya tayashi hira kuma yana kwantar masa da hankali.
Yau d'inma ganin be fito ba yasa sadiq ya zo gidan.A d'aki ya tarar dashi ,wayarsa ce a hannunsa amma bawai tapping yake ba kawai wasa da ita yake a hannunsa amma hankalinsa baya gun.
"Maza! Yane ka zauna a d'aki kai d'aya baka fito ba?" Sadiq ya tambaya.
A kasalance ya d'ago da kansa ya kalli sadiq.
"Sadiq". Ya kira sunansa.
Zama yayi kusa da shi kan katifarsa.
" Ahmad kai baka gajiya neh? Koyaushe cikin tunani haba mana ya kamata ka dena damun kanka haka".Sadiq ya fad'a.
"Sadiq baza ka gane bane,bakasan yanda nake ji bane". Ahmad ya fad'a.
" Ai gashi se rama kake,lafiyarka nake jiye ma se kace ba namiji ba duk wani abu daya sami mutum qaddararsa ce haka ba yadda zami,yin haka ba abinda ze 'karama illa kashe maka zuciya".Sadiq ya fad'a.
"Toh naji".Cewar Ahmad yana gyara kwanciyarsa.
" Ni da zaka bi shawara ta ma da ka mance da wannan damuwar".Sadiq ya fad'a.
"Na mance" Ahmad ya maimaita cikeda rainin hankali.
"Yes,akwai wani scholarship da naji ana cikewa na cyprus ,abinda yasa banyi ba saboda waec d'ina banda English ,kai kuwa naga kana da result mey kyau why not kai applying?"
"Mtchww! Ina cikin wannan yanayin zakai min maganar scholarship". Ahmad ya fad'a.
" Cigaba ne fa ,wai kai shikenan ka kashe rayuwarka ko meh,rabuwa da Reyhana baya nufin yin destroying life d'inka koh ita ance ma haka zata zauna tayi ta damuwa kamar yadda kake ?" Sadiq ya fad'a cikin fushi.
"Ni kaga rabu dani". Ya fad'a.
"Karka saurareni d'in rago kawai ". Sadiq ya fad'a tare da talle masa tafin 'kafarsa ya fita.
Ahmad ya d'au pillow da niyyar cilla masa yaga ya fice.
Washegari da safe koda ya gaisheda Umma yaji tayi masa maganar da Sadiq yayi mishi jiya.
" So zuwa yayi ya fad'a mata".Ahmad ya fad'a a ransa.
"Umma ki rabu dashi shirmensa ne". Cewar Ahmad.
" Kaide kake shirme,ca akai ma kowa irinka neh da be iya ri'ke 'kaddara ba".Umma ta fad'a.