← Book details Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 33

Sashe 21

Arziki Rabo 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

       " Hmm ai daga sister d'in ake zarcewa,kuma ni ai hakan ma dad'i yayi mini kaga du sauran damuwarka na past zaka manta dashi".Imran ya fad'a.

       "Na fad'a maka ni aure ma baya gaba na,koda ace na gama karatu ba aure zan bafa". Ahmad ya fad'a.

      " Kasan kaima hakan baze yiwu ba mahaifiyarka bazata bar hakan ba,akan wata bazaka kashe life d'inka ba".

       "Who knows ma koh ita tayi nata auren,saboda haka kawai ka bawa Zainab dama bakasan irin alkairi dake tattare da ita ba kuma koh a yanzu kasan she is a kind person".

        " Imran please let not talk about this now,bacci nake ji".Ahmad ya fad'a.

      "Ok ,amma kayi tunani". Imran ya fad'a tare da nufar nashi gadon.

      Ahmad sam bawai baccin yake ba kawai de ya kwanta ne ,kalaman Imran sun basa tsoro mussaman maganar " Who knows ma ko tayi nata auren".Abinda ya tsaya masa a rai kenan.

       "What if abinda ya fad'a gaske ne,3yrs zeyi wuya ace bata sake aure ba,but Zainab? toh ita Zainab damage tana da feelings a kaina ne? taya zata so ni? taya zan aureta ma yarinya ce fah? No this is not possible". Da wannan tunanin yayi bacci.

AR²💖

*Please vote, comment and share.Love u all😘*

Jasko💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣2⃣

      Ahmad tun sanda sukai chat da Zainab be sake hawa online ba yau sati d'aya.Yana so yayi avoiding d'inta yana mey tsoron kar maganar Imran ta tabbata,d'azunma yana ganin kiranta amma ya'ki picking.

       Littafinsa ya d'auko ya soma karatu su Imran sun fita shi kad'ai ne a gidan.Kiran Umma ne ya shigo wayarsa,da farko yayi tunanin koh Zainab ce seya share,se a kira na biyu ya duba yaga Umma.

        "Umma ina kwana". Ya gaisheta.

        " Lafiya lau,ya karatu?"Umma ta tambaya.

        "Alhamdulillah". Ya amsa.

         " D'azu muka dawo daga asibiti Zainab bata da lafiya". Umma ta fad'a.

         " Toh! Meya sameta?"Ya tambaya.

         "Malaria neh". Ta amsa.

          " Allah ya sawwa'ke".Ya fad'a.

          "Ameen". Ta amsa sannan sukai sallama.

      " Shiyasa ta kirani ashe,Allah sarki".Ya fad'a a ransa.

     Dialing number d'inta yayi amma batai picking ba kusan 3× dole ya ha'kura a ransa ya ayyana ko fushi tayi tunda taga ya amsa kiran Umma.

      Karatunsa ya cigaba dayi se bayan 1hr tukun ya sake kiranta ,se a karo na biyu ta d'aga.

      "Assalamu Alaykum"

       "Waalaikumussalam". Ta amsa a hankali.

        " Zainab ".Ya kira sunanta.

         " Uhm".Ta amsa a ciki.

          "Ya jiki?" Ya tambaya.

           "Naji sau'ki". Ta amsa.

   Sunfi 2min ba wanda ya sake cewa komai.

       " Am sorry d'azu bana kusa da wayar lokacin da kika kira".Ahmad ya daure ya fad'a.

       "Uhm na gane".Ta fad'a.

        " Kinsha magani?" Ya tambaya yana so ya chanja topic.

      "Eh nasha". Ta amsa.

      " Toh ki daure ki dinga cin abinci kinji".

       "Tahm". Ta fad'a.

       Daga haka sukai sallama,ta ajje wayarta befi 1min ba message ya shigo.

    " Get well soon Sis"

     Lokaci guda ta saki murmushi ,har cikin ranta taji dad'i ya damu da ita.

                 ***
     Reyhana ce a d'aki ta ciga tayi fam haushin ya isheta saboda Abba yayi mata zancen Sameer.

      Mahaifiyar Sameer da kanta tazo wajen Mommy sukai maganar Reyhana Mommy kuma ta fad'a wa Abba abinda yake faruwa.

     Tana cikin wannan yanayin Walida ta shigo take fad'a mata Sameer yazo.

      "Kije kice ganinan".Reyhana ta fad'a.

      Mayafi ta d'auka ta yafa sannan ta fita.

      A falo ta tarar dashi shi kad'ai ko Nasreen bata nan,zama tayi opposite dashi.

       Bayan sun gaisa Sameer ya fara magana"Uh..Reyhana bakya ganin it's the right time?".

      " Right time for what?" Ta tambaya.

        "To give me chance, Reyhana baza kice bakisan abinda ke raina ba   duk iya tsahon shekarunnan ,at first nayi losing and now ga second chance na sake samu i don't want to miss it you know ,I so much care about your life,  everything yours you are always in my mind ,my love for you  will never vanish from my heart you are the only one i ever loved,  you are my first love and no woman can ever take your place in my heart, yet I never find someone like you  ,Reyhana you are different from others, you are unique, if am to stay here for years I can't stop describing how i valued you and the love that I have for you,Reyhana please consider".

       Reyhana sam kalamansa beyi tasiri a zuciyarta ba dan be hanata fad'a masa;" Sameer,a yanzu inaso na koma karatu and i need to wait for Nasreen to start schooling".

       "Kina nufin kice se ta fara makaranta and se kin kammala masters right?"

      "Yes". Ta amsa.

        Jira take taga mey zece ,zuciyarta tana fad'a mata " Shikenan kin kawo 'karshen abin,Sameer baze iya jira har wannan lokacin ba".

       D'an guntun murmushi yayi kafin yace"Reyhana how many times do i have to tell you i am always your supporter I promise to be by your side always and forever, wannan ba wani matsala bace I promise to wait for you no matter how long it wiil take us".

         "Sameer taya zaka jirani har wannan lokacin b..." Bata 'kare ba ya  katseta.

      "I promised Reyhana".

       Shiru tayi bata sake cewa komai ba ,shigowar Nasreen  tasa basu cigaba da magana ba.'Karasowa tayi wajen ummienta tana mata hira,daga baya ta koma gun Sameer.

            °•° >3 years Later <°•°

   " Nasreen!" Reyhana ta kwala mata kira tana daga d'aki.

         Seda ta kwashi minti kusan 5 ta shigo d'akin,tana manne daga jikin 'kofa ta 'ki 'karasowa se zazzare ido take cikeda tsoro.

       "Zonan!" Ta kira ta tsawace.

          "Ummie dan Allah karki dakeni". Ta fad'a cikin rawar murya.

           " Ayyo! Watoh kinsan mey kikai? Zonan nace".Reyhana ta fad'a tana mata nuni da yatsa.

     A hankali ta 'karaso gurin kanta a sunkuye.

      Rigar uniform d'inta ta makaranta ta d'auko ta nuna mata.

       "Waya yanka wannan?" Ta tambayeta.

        Shiru tayi bata amsa ba yanzun ta d'ago kanta.

       "Ba magana nake ba?"

        "Ummie kiyi ha'kuri na dena". Ta fad'a kamar zatai kuka.

        Reyhana da hanzari ta tashi tana shirin fizgota sega Abba ya shigo d'akin.

     Da gudu taje ta ma'kale a jikin Abba.

      " Toh meya faru kuma?" Ya tamabaya yana d'ago kanta.

     "Dukana ummie zatai".Ta amsa.

     " Ya da haka?" Cewar Abba yana kallon Reyhana.

      "Abba rigar makarantarta ta yaga saboda karta je gobe".Ta amsa tana nuna masa.

       "Ayi mata afuwa yanzu bazata 'karaba ,uniform d'in ba biyu bane?" Abba ya tambaya.

    Se lokacin ta tuna biyu ne da idonta ya rife,Nasreen jin ance biyu ta tur'bina fuska dan bata son zuwa makaranta.

      "Ungo chocolates d'inki". Abba ya fad'a tare da mi'ka mata nylon dake hannunsa.

     Tsalle ta shiga yi tazo wajen Reyhana tana nuna mata.

     " Toh nagani seki ce kin gode".Ta fad'a.

      "Abba thank you". Ta fad'a.

       " Yawwa 'yar baturiya".Abba ya fad'a.

      Tare suka sauka 'kasa da Abba ta ruga a guje  wajen su Walida tana nuna musu.

         Walida da anzama 'yan mata da ace dane da seta ce ta bata, yanzu kuwa kau da kanta tayi ta cigaba da abinda take.

       A shekaru ukunnan abubuwa da dama sun gudana.Reyhana ta kammala masters d'inta,Nasreen kuwa an sata makaranta 2yrs da suka wuce yanzu tana nursery 2 koyaushe fama ake da ita wajen shiryawa school.

      Sageer tuntuni ya fara aiki a asibiti as medical laboratory technician ya zama busy ba kasafai suke ganinshi a gida ba se dare.

       Ikram ma ta zama cikakkiyar journalist tana zuwa aikinta itama,se Bassam da saura shekara d'aya ya rage ya kammala degree d'insa,Walida wannan shekarar tayi graduating yanzu admission take jira.

       Sameer kuwa ya koma America amma yana zuwa jefi-jefi kuma wani sa'in suna waya da Reyhana.

       Mommy se kallo dan wani lokacin idan ta gansu full house setaga kamar ba ita ta haifesu ba ,kowa ya girma.

                   ***
Ahmad°•°

        Shigowarshi gida kenan daga gidansu Sadiq yake bayan ya dawo daga aiki ya biya se yanzu ya shigo gida,6:02pm.

        D'akinsa ya shiga ya watsa ruwa tukun ya fito cikin 'kananan kaya blue jean da ba'kin T-shirt.

    A falo ya iske Umma,cikin girmamawa ya gaisheta.

      "Yaushe ka shigo banjiba?" Ta tambaya.

       "Ba jimawa". Ya amsa.

        " Toh abinci fah".Ta tambaya.

       "A'a na 'koshi". Ya amsa.

        " Nikam gajiya akai da abincin nawa yau kusan kwana uku ba a ci".Umma ta fad'a.

        "No kawai bana jin yunwa neh fa anjima zanci". Ya fad'a da murmushi kad'an a fuskarsa.

     "Toh ai shikenan". Ta fad'a.

       Remote  dake kan center carpet ya d'auka ya chanja channel daga Arewa24 zuwa MBC Action.

         " Aikin kenan ,wannan masu damben koh me za'a kalla anan oho". Umma ta fad'a.

       Ahmad kuwa murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba ya cigaba da kallonsa.

       1 year kenan da fara aikinsa ,mahaifin Zainab shi ya taimaka masa ya samu aiki a NGOs(Non-governmental organizations).

     Komai ya sauya tun sanda ya samu aiki,Ya gyara musu gidansu ya koma kamar sabo ba abinda Umma ta rasa a yanzu inde na bu'katar alatu da sauran wani jin dad'i although rayuwa ba koyaushe ake cikin jin dad'i ba no matter how billionaire you are.

       A yanzu haka yana da farmland na noman shinkafa kuma cikin ikon Allah yana samun profit kuma wannan shawarar Umma ce ta sashi yin noman shinkafar.

      Zainab tana zaria, ta kwashe 2weeks a can amma nan da kwana biyu zata dawo tunda wannan week d'in aka koma school.

      Zainab ba abinda ya chanja a cikin ranta gameda son da take wa Ahmad sede har yanzu bata fito tace tana sonsa ba.

     Tun sanda ya dawo gida Nigeria Umma tayi ta tirsasashi yaje gidansu Reyhana amma kullum seya ce mata ba yanzu ba,daya gaji da tunatar dashi da take seyai 'karya yace yaje,idan ta tambayeshi ya sake zuwa seyace mata "Eh" akan haka ya barta.

     Daga yayi attempting zuwa seya fasa, baida kalaman daze fad'a mata(A tunaninsa) from bad to worse da ana maganar 4yrs yanzu 6yrs be saka 'yarsa a ido ba,shikanshi idan ya tuna yana jin haushin kansa.

                    ***

     Reyhana kuwa a zuciyarta tana 'ko'karin mantawa da Ahmad amma kamannin da Nasreen ta d'auko na Ahmad yasa bazata mance da fuskarsa ba,ita tama fidda ran sake ganinsa a rayuwarta.

      9pm lokacin baccin Nasreen,seda tayi addu'a kamar koyaushe Reyhana tana karanta mata ita kuma tana repeating.
Chapter 21 · 0% Book details