Sashe 9
Alakar Yarinta Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
Misalin ƙarfe biyar na yammacin ranar laraba, zaune take akan sallayarta tana karatun qurani mai girma tun da ta yi sallar la'asar take karatun, bayan ta gama ta rufe qur'anin tare da ɗaga hannunta sama tana ta addu'a wanda ba a jin me take cewa sai dai hawaye na ta kwaranya daga idanunta har ta kammala ta shafa.Qur'anin ta ɗauka ta mayar dashi ma'ajjinsa sannan ta linke hijabin da sallayar ta ajiyesu, kan gadonta ta koma ta kwanta idanunta a sama har lokacin hawaye na kwaranyowa a idanun nata, ita kaɗai ta san me take ji a zuciyarta game da abin da take tunawa Allah ne kuma kaɗai ya san damuwarta domin duk duniya babu wanda ta taɓa faɗawa damuwarta.Amma dai ta san kullum idan ta tuno shi tana jin damuwa a ranta kuma in ba kuka ta yi ba bata samun sassauci a zuciyarta, idan kuma ta rufe idanunta shi take gani lokacin da ya faɗo daga jikinta, da kuma lokacin da aka gama gyarashi aka miƙo mata shi, Allah sarki idan kuma ta tuna lokacin da aka ce ya mutu aka sanyashi a kwali aka ce gida za a je ayi suturarsa sai ta ji zuciyarta ta yi rauni da yawa.Gashi yau tsawon shekaru goma sha shida kuma bata sake samun wani cikin ba bare ayi zancen sake haihuwa bata sani ba ko za ta haihu a gaba ko kuma shi ne kaɗai rabonta.
"Ya Allah kai kaɗai ne ka san damuwata Allah ka kawo min mafita, ya Allah ka bani wani rabon kafin na bar duniya, idan kuma shi kaɗai ne rabona ya Allah ka...kafin ta ƙarasa sai kuka ya ƙwace mata.Haka dai tana nan tana tunani har dai Suhailat mai mata aiki ta faɗa mata cewa Alhaji ya dawo haka ta wanke fuskarta ta gyara fes kamar ma ba ita ke cikin damuwa da yin kuka ba ta shafa powder da lipstick ta fito abinta sai tashin ƙamshi take.
Tana zuwa kwa ta ga Abie tsaye yana jiranta dan ko upstairs É—in ma ya kasa hawa
"Welcome back"Ta ce tana sakar masa murmushi tare da É—aukan jakar office É—in nasa.
"Ni na yi fushi" Ya ce yana juya mata baya.
Wani murmushi ne ya suɓuce mata.
"Ai wanda ya yi fushi ba shi yake faÉ—a ba, wanda aka yiwa fushin ne ke fahimtar haka"
"Koma dai menene ni bana kulaki"
"Ni ce fa" Ta faɗa lokacin da ta zo inda ya juya ɗin.Ƙara juyawa ɗaya side ɗin ya yi.Ita ma komawa ta yi tare da ajiye jakar hannunta ta ce
"Ni ko? Afwan" Ta faɗa tana haɗe hannayenta wuri ɗaya alamar roƙo.
Da murmushi ya juyo suka fuskanci juna, sannan ya ce
"Ba ke ce ba kika ƙyaleni ina ta jiranki, kuma kinsan ba zan iya haurawa sama ba matuƙar dai baki fito ba gashi na gaji ba zan iya zuwa ɓangarenki ba"
"To ka yi haƙuri ka ji? Ina can ina ɗan maka kwalliya ne"
"To me yasa baki yi min kafin dawo wa ta ba?"
"Afwan wani ɗan abu ne ya riƙe ni har na shagala da hakan, amma ai ka san ina ji da kai"
"To shikenan na huce, ai ni na ma fi ji da ke"
"Godiya nake"Ta ce tare da ɗaukan jakar ya riƙo ƙugunta suka haura sama abinsu suna zantukan soyayya.
_JIGAWA STATE_
_GAGARAWA L.G_
Tafe ta ke a gefen titi sai sosa kan ta take tana dariya ita kaɗai, sanye take da kaya wanda suka yi wani datti kan ta babu ɗankwali gashin kan nata mai tsawo da yalwa ya bazo har gadon bayanta, ga ƙura da datti a jikin gashi da suk canja masa kama daga baƙi zuwa wani ja, kyakkyawar mace ce duk da yanayin jikinta ya nuna baya samu kulawa kasancewarta a cikin hali na hauka.
Ƙarasowa ta yi wajen wani maina inda mai shayi da kuma mai tsire a gefe da ma masu sayar da abubuwa da dama a wurin, tsayawa ta yi tana bi tana miƙa hannu a bata, da alama abinci take buƙata.
"Ke dalla kauce ki ba mutane waje sai kin je kin sakawa mutane wannan dattin jikin naki ko kim saka mana gashi kij kashe mana kasuwa"Cewar mai tsiren cikin zafin rai.Cikin sauri ta matsa dan har tsorata ta yi yadda ya zafice ta, tana tafiya tana waiwayen dan gani take biyota zai yi ya daketa, bata gani ba ta bige wa wata mai siyar da abinci kwanan miya ds yake ta tafi wurin wasu samari ta karɓo kwanukan ta da kuɗin, daga can ta hango mahaukaciyar ta mata ɓarin jar miya ai kuwa da cikin sauri ta taho tana zuwa ta sanya hannu ta damƙo gashin mahaukaciyar ta juyo da ita suka fuskanci juna da yake ita ko da ta ɓarar da miyar ma bata kawo aka ta yi wani abu ba da yake a halin rashin hankali.
"Wane ɗan iskan ya ce ki ɓarar min da miya?" Cikin tsoro mahaukaciyar ke kallonta tana tattakurewa, ai kuwa mai abincin nan ta ɗaga hannu ta ɗauketa da wani mari, cikin gigicewa ta dafe kuncinta tare da ƙoƙarin ƙwace kan ta daga gashinta da ta riƙe mata da hannu ɗayan, nan dai mutane suka taru wasu na bata haƙuri wasu na cewa bata kyauta ba tunda bata da hankali daƙer dai matar nan ta ƙyale mahaukaciyar bayan wani mutum ya biyata kuɗin miyar, sannan ya siyawa mahaukaciyar abinci a wurin wata aka zuba mata a leda dan sun ce ba za su bata a kwano ba.
Karɓar abincin ta yi ta juya cikin sauri dan dama yunwa take ji tun jiya rabonta da abinci, ƙarƙashin wata bishiya ta koma can nesa da mutane ta zauna ta bule abincin nan taliya da miya ce amma ba ruwanta da cakuɗawa haka ta shiga ci babu ƙaƙƙautawa wani sa'in ta ɗakko wurin miya wani lokacin kuma ta ɗakko inda babu miya, sai da ta cinye tas sannan ta kwanta a ƙasan wurin a take bacci ya ɗauketa.
Mmn afrahðŸ˜ðŸ¥°ðŸ˜˜
â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸
💕ALAƘAR YARINTA💞
â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸
NA
MAMAN AFRAH
FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
PAGE 1ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£0ï¸âƒ£
_Jigawa state Dutse gadawur_
Gidan Alhaji Sagiru sarkin yaƙin Dutse, Alhaji sagiru ne zaune a bakin gado ya yi tagumi fa duka hannayensa, da alama dai ya yi nisa a cikin tunani sai dai shi kansa bai san takamaimai tunanin me yake ba.Kullum ya kan tsinci kansa a irin wannan halin idan har ya keɓance kansa daga mutane yana ji ya rasa sukuni yana jin damuwa da tunani sun addabi zuciya da ƙwaƙwalwarsa, amma kash sai dai baya taɓa tantance tunanin me yake, sai dai ya gaji ya haƙura da tunanin da ke addabarsa wani sa'ilin ma har sai ya zubar da ruwan hawaye sannan yake samun sauƙi a ransa.
Hajiya Suwaida ce tafe cikin wani tsadadden lashi da aka mata ɗinkin buba sai zuba ƙamshi take yi abinta, upstairs ta haura domin dubo mai gidan nata saboda ta ga shiru bai sakko ba.A hankali ta tura ƙofar ɗakin da ta san za ta sameshi, ta maida ƙofar ta rufe amma har ta ƙaraso cikin ɗakin da alama ma bai san ta shigo ba, inda yake kallo ta kalla sai ta ga idanunsa na kan wani ƙaton hotonsa da ke manne jikin bango, hoton an ɗaukesa ne a ranar da aka naɗashi sarkin yaƙin garin Dutse yanzu kusan shekaru ashirin kenan.Sanye yake da kufta da aka yiwa aikin irin na sarauta sai alkyabba da da aka ɗora akan kayan yana riƙe da sanda irin ta sarauta, ya kafe hoton da ido ga kuma idanun nasa sun masa jajawur.Yatsina fuska ta yi tare da taɓe baki, dan ta san zancen gizo baya wuce na ƙoƙi shi kullum yana tunani kuma in ka tambayeshi sai yace shi kansa bai san danuwarsa ba hasalima sai yace bai san me yake tunawa ba ita har gajiya take da tambayarsa.
Bakin gadon ta ƙarasa ta zauna, a kusa dashi amma har lokacin bai san tana wurin ba, hannu ta sanya ta dafa kafaɗarsa, shiru bao san tana yi ba har sai da ta ɗan jijjiga kafaɗar tasa sannan ya juyo a ɗan firgice.
"Hajiya" Ya kirata da ɗan ruɗewa a muryarsa saboda ya ɗan razana da ta taɓashi sanadin nisan da ya yi a cikin tunani.
"Na'am Alhajina, tunanin nan ne da har yanzu kake yi haba sarkin yaƙi mai takobin zinare kaifin takobinka zai sa kowa ya watse" Ta ce tana wani murmushi a fili a ranta kuma tana ayyana cewa ƙaryarka dubu ka tuno abin da kake son tunowa wannan ɓoyayyen sirri ya rufu har gaba da abada babu mai tunowa bare har ya fallasa.
Murmushi ne ya kuɓuce masa na kirarin da ta masa, duk da bai wani dawo daidai ba daga halin da ya shiga ba, dan har wani sarawa ya ji kansa na masa sannan yace
"Wallahi Hajiya ni kaina inason na daina tunanin nan amma bansan lokacin da yake zuwa min ba saidai in tsinci kainana ciki dumu-dumu"Ya faÉ—a yana dafe goshinsanda hannu.
"Ka yi haƙuri za ka daina ai da kaɗan-kaɗan zai barka tunda yanzu ba kamar da babya ragu"
"Ke kike gani ya ragu amma ni nasan bai ragubba saboda kullum sai na yi babu adadi, ni abin da ke damuna bai wuce ba rashin rashin sanin takamai man abin da nake tunawa ba sai dai fa in ƙari tunani amma tunanin nawa baya kaiwa inda nakeso ya kai saidai na gaji na haƙura"
Haka kwa za kake gajiya har abada dan babu wani abu da ƙwalƙwalwarka za ta tuna, saidai ka gaji ka haƙura, ta faɗi hakan a ranta a fili kuma sai ta ce
"Allah sarki Alhajina nima bana jin daɗin halin da kake kasancewa wallaho saidai dan ba yadda zan yi ne, amma ka yi haƙuri zaka daina watarana"
"To Hajiya Suwaida shi sa nake alfahri da kasancewarki mata ta"
"Ni ma ina alfahri da kasancewarka miji a gareni"
A haka ta lallaɓashi ya shiga wanka ya shirya suka sakko ƙasan tare, lokacin ma'aikatan gidan na ta hidima kowa ya kama aikinsa.
"Ya Allah kai kaɗai ne ka san damuwata Allah ka kawo min mafita, ya Allah ka bani wani rabon kafin na bar duniya, idan kuma shi kaɗai ne rabona ya Allah ka...kafin ta ƙarasa sai kuka ya ƙwace mata.Haka dai tana nan tana tunani har dai Suhailat mai mata aiki ta faɗa mata cewa Alhaji ya dawo haka ta wanke fuskarta ta gyara fes kamar ma ba ita ke cikin damuwa da yin kuka ba ta shafa powder da lipstick ta fito abinta sai tashin ƙamshi take.
Tana zuwa kwa ta ga Abie tsaye yana jiranta dan ko upstairs É—in ma ya kasa hawa
"Welcome back"Ta ce tana sakar masa murmushi tare da É—aukan jakar office É—in nasa.
"Ni na yi fushi" Ya ce yana juya mata baya.
Wani murmushi ne ya suɓuce mata.
"Ai wanda ya yi fushi ba shi yake faÉ—a ba, wanda aka yiwa fushin ne ke fahimtar haka"
"Koma dai menene ni bana kulaki"
"Ni ce fa" Ta faɗa lokacin da ta zo inda ya juya ɗin.Ƙara juyawa ɗaya side ɗin ya yi.Ita ma komawa ta yi tare da ajiye jakar hannunta ta ce
"Ni ko? Afwan" Ta faɗa tana haɗe hannayenta wuri ɗaya alamar roƙo.
Da murmushi ya juyo suka fuskanci juna, sannan ya ce
"Ba ke ce ba kika ƙyaleni ina ta jiranki, kuma kinsan ba zan iya haurawa sama ba matuƙar dai baki fito ba gashi na gaji ba zan iya zuwa ɓangarenki ba"
"To ka yi haƙuri ka ji? Ina can ina ɗan maka kwalliya ne"
"To me yasa baki yi min kafin dawo wa ta ba?"
"Afwan wani ɗan abu ne ya riƙe ni har na shagala da hakan, amma ai ka san ina ji da kai"
"To shikenan na huce, ai ni na ma fi ji da ke"
"Godiya nake"Ta ce tare da ɗaukan jakar ya riƙo ƙugunta suka haura sama abinsu suna zantukan soyayya.
_JIGAWA STATE_
_GAGARAWA L.G_
Tafe ta ke a gefen titi sai sosa kan ta take tana dariya ita kaɗai, sanye take da kaya wanda suka yi wani datti kan ta babu ɗankwali gashin kan nata mai tsawo da yalwa ya bazo har gadon bayanta, ga ƙura da datti a jikin gashi da suk canja masa kama daga baƙi zuwa wani ja, kyakkyawar mace ce duk da yanayin jikinta ya nuna baya samu kulawa kasancewarta a cikin hali na hauka.
Ƙarasowa ta yi wajen wani maina inda mai shayi da kuma mai tsire a gefe da ma masu sayar da abubuwa da dama a wurin, tsayawa ta yi tana bi tana miƙa hannu a bata, da alama abinci take buƙata.
"Ke dalla kauce ki ba mutane waje sai kin je kin sakawa mutane wannan dattin jikin naki ko kim saka mana gashi kij kashe mana kasuwa"Cewar mai tsiren cikin zafin rai.Cikin sauri ta matsa dan har tsorata ta yi yadda ya zafice ta, tana tafiya tana waiwayen dan gani take biyota zai yi ya daketa, bata gani ba ta bige wa wata mai siyar da abinci kwanan miya ds yake ta tafi wurin wasu samari ta karɓo kwanukan ta da kuɗin, daga can ta hango mahaukaciyar ta mata ɓarin jar miya ai kuwa da cikin sauri ta taho tana zuwa ta sanya hannu ta damƙo gashin mahaukaciyar ta juyo da ita suka fuskanci juna da yake ita ko da ta ɓarar da miyar ma bata kawo aka ta yi wani abu ba da yake a halin rashin hankali.
"Wane ɗan iskan ya ce ki ɓarar min da miya?" Cikin tsoro mahaukaciyar ke kallonta tana tattakurewa, ai kuwa mai abincin nan ta ɗaga hannu ta ɗauketa da wani mari, cikin gigicewa ta dafe kuncinta tare da ƙoƙarin ƙwace kan ta daga gashinta da ta riƙe mata da hannu ɗayan, nan dai mutane suka taru wasu na bata haƙuri wasu na cewa bata kyauta ba tunda bata da hankali daƙer dai matar nan ta ƙyale mahaukaciyar bayan wani mutum ya biyata kuɗin miyar, sannan ya siyawa mahaukaciyar abinci a wurin wata aka zuba mata a leda dan sun ce ba za su bata a kwano ba.
Karɓar abincin ta yi ta juya cikin sauri dan dama yunwa take ji tun jiya rabonta da abinci, ƙarƙashin wata bishiya ta koma can nesa da mutane ta zauna ta bule abincin nan taliya da miya ce amma ba ruwanta da cakuɗawa haka ta shiga ci babu ƙaƙƙautawa wani sa'in ta ɗakko wurin miya wani lokacin kuma ta ɗakko inda babu miya, sai da ta cinye tas sannan ta kwanta a ƙasan wurin a take bacci ya ɗauketa.
Mmn afrahðŸ˜ðŸ¥°ðŸ˜˜
â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸
💕ALAƘAR YARINTA💞
â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸
NA
MAMAN AFRAH
FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
PAGE 1ï¸âƒ£9ï¸âƒ£&2ï¸âƒ£0ï¸âƒ£
_Jigawa state Dutse gadawur_
Gidan Alhaji Sagiru sarkin yaƙin Dutse, Alhaji sagiru ne zaune a bakin gado ya yi tagumi fa duka hannayensa, da alama dai ya yi nisa a cikin tunani sai dai shi kansa bai san takamaimai tunanin me yake ba.Kullum ya kan tsinci kansa a irin wannan halin idan har ya keɓance kansa daga mutane yana ji ya rasa sukuni yana jin damuwa da tunani sun addabi zuciya da ƙwaƙwalwarsa, amma kash sai dai baya taɓa tantance tunanin me yake, sai dai ya gaji ya haƙura da tunanin da ke addabarsa wani sa'ilin ma har sai ya zubar da ruwan hawaye sannan yake samun sauƙi a ransa.
Hajiya Suwaida ce tafe cikin wani tsadadden lashi da aka mata ɗinkin buba sai zuba ƙamshi take yi abinta, upstairs ta haura domin dubo mai gidan nata saboda ta ga shiru bai sakko ba.A hankali ta tura ƙofar ɗakin da ta san za ta sameshi, ta maida ƙofar ta rufe amma har ta ƙaraso cikin ɗakin da alama ma bai san ta shigo ba, inda yake kallo ta kalla sai ta ga idanunsa na kan wani ƙaton hotonsa da ke manne jikin bango, hoton an ɗaukesa ne a ranar da aka naɗashi sarkin yaƙin garin Dutse yanzu kusan shekaru ashirin kenan.Sanye yake da kufta da aka yiwa aikin irin na sarauta sai alkyabba da da aka ɗora akan kayan yana riƙe da sanda irin ta sarauta, ya kafe hoton da ido ga kuma idanun nasa sun masa jajawur.Yatsina fuska ta yi tare da taɓe baki, dan ta san zancen gizo baya wuce na ƙoƙi shi kullum yana tunani kuma in ka tambayeshi sai yace shi kansa bai san danuwarsa ba hasalima sai yace bai san me yake tunawa ba ita har gajiya take da tambayarsa.
Bakin gadon ta ƙarasa ta zauna, a kusa dashi amma har lokacin bai san tana wurin ba, hannu ta sanya ta dafa kafaɗarsa, shiru bao san tana yi ba har sai da ta ɗan jijjiga kafaɗar tasa sannan ya juyo a ɗan firgice.
"Hajiya" Ya kirata da ɗan ruɗewa a muryarsa saboda ya ɗan razana da ta taɓashi sanadin nisan da ya yi a cikin tunani.
"Na'am Alhajina, tunanin nan ne da har yanzu kake yi haba sarkin yaƙi mai takobin zinare kaifin takobinka zai sa kowa ya watse" Ta ce tana wani murmushi a fili a ranta kuma tana ayyana cewa ƙaryarka dubu ka tuno abin da kake son tunowa wannan ɓoyayyen sirri ya rufu har gaba da abada babu mai tunowa bare har ya fallasa.
Murmushi ne ya kuɓuce masa na kirarin da ta masa, duk da bai wani dawo daidai ba daga halin da ya shiga ba, dan har wani sarawa ya ji kansa na masa sannan yace
"Wallahi Hajiya ni kaina inason na daina tunanin nan amma bansan lokacin da yake zuwa min ba saidai in tsinci kainana ciki dumu-dumu"Ya faÉ—a yana dafe goshinsanda hannu.
"Ka yi haƙuri za ka daina ai da kaɗan-kaɗan zai barka tunda yanzu ba kamar da babya ragu"
"Ke kike gani ya ragu amma ni nasan bai ragubba saboda kullum sai na yi babu adadi, ni abin da ke damuna bai wuce ba rashin rashin sanin takamai man abin da nake tunawa ba sai dai fa in ƙari tunani amma tunanin nawa baya kaiwa inda nakeso ya kai saidai na gaji na haƙura"
Haka kwa za kake gajiya har abada dan babu wani abu da ƙwalƙwalwarka za ta tuna, saidai ka gaji ka haƙura, ta faɗi hakan a ranta a fili kuma sai ta ce
"Allah sarki Alhajina nima bana jin daɗin halin da kake kasancewa wallaho saidai dan ba yadda zan yi ne, amma ka yi haƙuri zaka daina watarana"
"To Hajiya Suwaida shi sa nake alfahri da kasancewarki mata ta"
"Ni ma ina alfahri da kasancewarka miji a gareni"
A haka ta lallaɓashi ya shiga wanka ya shirya suka sakko ƙasan tare, lokacin ma'aikatan gidan na ta hidima kowa ya kama aikinsa.