← Book details Sarauniyar Kyau Takun Farko Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 95 OF 96

Sashe 95

Sarauniyar Kyau Takun Farko Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Tahoo zoo garenii Yakai wannan masoyina, mai wahalar da zuciyata da bahamaƙiyar ƙauna, kazo ina jiran ka, kaji kuwa tahoo zoo garenii Yakai kyakyawan ƙayataccen saurayi Wanda Ya sace heart ɗita da masifar qaunar sahhh."🤭

😇😇😇

Shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya na dogon numfashin da Taja sannan ta ce "YaYa Maleek, Yaya Maleek to yah kaji wannan tayi kuwa?."

Maleek dake faman tiqan dariya ƙasa ƙasa tunda ta fara Ya yi murmushi sannan yana faɗin

"It's Nice, 🙂 it's Very Amazing,😂 ae ina faɗa miki wannan waƙar taki ko Shakirah mawaƙiya ba zata gwada miki iya waƙa ba."

Ya yi maganar yana kuma ɓoye Dariyar sah.

Washe Baki Husnee tayi Sannan tana cewa

"YaYa Maleek ko kana so na ƙarayi maka wata kalar ce? Kaji salon iya saloh na burgewa da saka nishaɗi?."😘

Da sauri Maleek ya bata amsa da cewa

"A'a Doctor a ɓangaren waƙa Husnee na gode sosai. Yanzu abin da nakeso dake ki kashe wayar sannan kiyi addu'a ki kwanta kinji?."

Husnee tana dariyar nishaÉ—i ta amsa masa da
"Toh amma Yaya Maleek idan na kashe kiran, gobe zaka kirani kuwa?."

"Eh," Ya bata amsa sannan tayi masa sallama kana ta kashe wayar ta.

Ajiyar zuciya Maleek ya sauke yana kallon wayar. Yayin da Fuskar sa take ɗauke da ƙayataccen murmushi na musamman cike yake da nishaɗi. Wanda shirmen Husnee ya jefasa ciki.

A fili ya furta

"Ina ƙaunar ki Husnee SARAUNIYATAH I Love You, For The All My Heart My Lucky Girlfriend..GN."👋💃

*KANO-STATE*

Misalin ƙarfe uku da rabi na ranar washe Garin zuwan su Afeefah Kano ita ma Nainarh tabi jirgin etritea domin komawa ƙasar Aurenta. Yayin da ta sama rakiyar Afeefah da Lailah da kuma Mah'eesha sai Deejarh.

Horn driver ya buga da ƙarfi ganin Mai gadi bai zo ba, da sauri gate man ɗin tare da da wasu securities suka wangale gate na gidan da sauri.

Sannan Driver ya cinna Hancin Motar cikin Katafaren Gidan na Uncle Sagir, sai da ya kammala parking a wurin da aka tanadar domin yin parking na motocin Gidan, sannan suka buɗe Motar suka fiffito a tare suka nufa ƙofar palon Gidan.

Afeefah tana shirin kai hannu ta buɗe ke nan saiga Hameeda ta fito daga ɓangaren su na yaran gidan mata.

Murmushi Afeefah tayi Hango Hameeda sannan tana cewa, Bayan Hameedar ta ƙariso wurin da suke tsaye

"Yauwa Auntie Hameeda dama fa ke nake nema, na ɗauka ma kina ɓangaren Auntie Suwaiba ne ae."

"A'a sauke kawai domin kuwa ina nan a ɓangaren mu yanzu ma da kika ganni Gidan su Juwairiya Jabir Bici nah nufa dama Allah, Allah nake na same ki kafin ki fito raka Auntie Nainarh sai kuma kafin na fito harkin tafi, Yanzu dai zance Ya ƙare sai mu ɗunguma muje Gidan kawai tunda kince zakije ko?."

Hameeda ta ƙare doguwar maganar tana saɓa backpack nata irin na ƴan Jarida masu neman Bayanai.

Murmushi Afeefah tayi sannan tana faÉ—in

"Okay muje kawai babu damuwa don a shirye nake."

Kallon Lailah da Mah'eesha da kuma Deejarh tayi sannan ta ce

"Bari muje wani guri mu dawo."

Cikin sauri har suna haÉ—a baki suka ce

"A'a ae koh ina ne muma zamuje domin Yawo muke ji highly."

Lailah ta ƙara da cewa badai wannan Yarinyar da ta faɗi wajen gasar SARAUNIYAR KYAU na wannan Jahar Ba, aikuwa indai ita ce zani domin kuwa jiya da dare naga Labarin a Facebook."

Hameeda ta ce

"Ita ce badai Juwairiya Jabir Bici ba, ae wannan Labarin Ya zagaye duniya sosai."

Mah'eesha ta ce

"Ah gaskiya nima za biku saboda ina so na ganta ido da ido, domin kuwa sai da nayi Hawaye da jin labarinta."

Ita ma Deejarh ganin haka yasa ita ma da sauri ta ce.

"Nima zan biku."

"It's okay tunda na fahimci kowa ma so yake yi yaje, kawai kuzo mu tafi kawai tun kafin wasu su ƙaru, domin kuwa naji ita ma Haseeya tana cewa zataje."

Hameeda tayi maganar tana nufar hanyar parking, gaba É—aya É—unguma suka yi suma suka nufa parking lot É—in, Afeefah na faÉ—in

"Aikuwa dai Haseeya ba zata sama damar zuwa ba tunda Auntie Raheemarh ta riƙeta da aiki."

Hameeda dake shirin buÉ—e mota ta ce
"Ke nan dai kun biya ta gidanta daga Airport É—in ko, no wonder naji kun daÉ—e sosai, ashe akwai wurin da kuka biya ne."

Tayi maganar tana tayar da Motar sannan ta karya kwana ta nufa gate Lailah tana bata amsa da

"Ae dan ma Afeefah ce ta wani ce mu dawo Gida akwai wurin da take so taje, badan haka ba, ae dama har Gidan Yaya Shahid sai munje."

Mah'eesha ce wannan karon tayi magana Bayan gate man ya wangale musu gate sun fita ta ce

"Ae wallahi da sai dai kuje ku kaɗai domin kuwa ni babu inda zani, saboda wannan baƙar matar tasa ba tasan Menene mutunci ba sam."

Lailah ta kuma cewa
"Ae badan ita zamuje ba, saboda Yaya Shahid zamu je, kuma tunda naji kince Haka toh wallahi sai naje bari mu dawo daga nan inda zamu, sai naga ƙarshen rashin mutunci mu da muke siyan rigima da kuɗin mu ma."

Murmushi kawai Afeefah tayi sannan ta ce
"Ah gaskiya Dangin miji su nada matsala tasu ta musamman, wani lokacin zata iya Yiwuwa Mah'eesha kune baku biyo ma ta ta inda zata dinga muku kirki da mutun taku ba."

Hameeda dake ƙoƙarin karya kwanar da kai tsaye zai sa dasu da Street na Yankin da unguwan su Juwairiya Jabir Bici yake. Tayi murmushi tana faɗin

"Hehehh Afeefah ke nan bazaki fahimta bane kawai, domin kuwa wannan matar Yaya Shahid ɗin tafi ƙarfin duk tunanin ki Allah kuwa."

Afeefah mayar ma ta da martani ta hanyar faÉ—in

"Kune dai bazaku fahimta ba, domin kuwa mafi yawan samun rashin fahimta da ake yi tsakanin dangin miji ko kuma ƙannin sa da matar sa. Tofa mafi Yawa Laifin su waɗannan Dangin mijin ne fa, amma fa a Tunanina aha."😁

"Hahaha feefah mai kyau ke dai kawai tunda bazaki fahimci abin da ake so ah ganar dake ba, Bari kawai nayi shiru, duk Ranar da tsautsayi yakai ki zuwa Gidan zaki fahimta gaskiyar Mah'eesha ne."

"Toh Allah ya kaimu Gobe ni kuma zan biku zuwa Gidan domin nah ganewa ido na komai."

Cewar Afeefah daga haka kuma motar ta ɗauki shiru suka ci gaba da tafiya dama ita Deejarh ciwo sama sama da taji mararta tana yi ne yasa ko tsunduma Bakinta cikin firar tasu ba tayi ba.😌

"Dakata ina ga wannan ne, Gidan tsayawa driver na a daidaita ɗin Ya yi a ƙofar gate na wani makeken Gida, sannan suka fito.
Miƙa masa kuɗinsa tayi sannan ta juya tana kallon ɗayar Budurwar wacca suka zo tare tana faɗin.

"Mu shiga ciki ko."

Murmushi tayi sannan ta ce "Muje tohm."

Kwankwasa ƙaramar ƙofar gate ɗin tayi Sannan gate man ya buɗe Suka shiga ciki.

Sai da suka isa dai dai ƙofar palon Gidan sannan budurwar ta kalla ƴar uwan tafiyarta ta tana cewa

"Yanzu Humaira idan muka shiga mai zamuce ne?."

Murmushi Humaira tayi tana bata amsa da cewa

"Kawai zamu ce ne munzo ganin Juwairiya Jabir Bici domin mu tayata jaje, ko kuwa dai ke Jiddarh ba zaki iya faÉ—ar Hakan ba ne?."

Ajiyar zuciya Jiddarh ta sauke tana shirin magana aka buɗe ƙofar palon saboda haka basu tsaya jiran komai bah
suka shiga ciki.

Nuna musu kujera budurwar da ta buɗe ƙofar tayi, sannan bayan sun zauna ta ce

"Wurin Auntie Juwairiya ku ka zo ko?."

Tayi musu tambayar daga inda take miƙe.

Murmushi Jiddarh tayi sannan ta ce "Eh wurinta mukazo fatan dai tana nan?."

Murmushi ita ma budurwar tayi sannan ta ce

"Eh tana nan barima na kira muku ita kawai."

Tayi maganar tana nufar staircases.

Ya ye Niƙab ɗin da ta rufe kyakyawar fuskarta dashi, Jiddarh tayi tana faɗin

"Zufa wallahi sosai."

Dariya Humaira dake latsa wayarta tayi tana faÉ—in

"Ni dama ban san gulmar da ya saka kika wani sanya Niƙab ba sai kace wata ɓarauniya, ba sarauniya ba.🥰

"Kedai kawai Humaira Ba za ki fahimta bane, kawai saboda tsaro na sanya fa badan tsoro ba."

Ta ƙarishe maganar tana kallon kyakyawar budurwar da ta sauko palon da suke zaune ita da wannan budurwar da ta buɗe musu ƙofar.

"Sannun ku fatan kuna lafiya. Ya Hanya."

Budurwar tayi musu maganar a lokacin da take zama a kujerar dake fuskantar nasu. Yayin da ita ma ɗayar da alama ƙanwarta ce ta zauna kusa da ita.

Fuska washe Jiddarh ta amsa da cewa

"Lafiya qalau wallahi,bFatan kema Hakan, sannan kuma ya jiki, ya aka ji da al'amuran?."

Tayi maganar tana ƙarewa Budurwar kallo ta cikin Niƙab ɗin fuskarta, ta fahimci ba wata Babba bace cancan domin iya Lissafinta zasu iya zuwa sa'anni da ita.

"Jiki kam Alhamdulillah, Ina Godiya sosai da nuna kulawar ku a gareni."

Cewar Budurwar cike da fara'a.

"Aunty's please ga abin taɓawa fa, Bismillanku fa."

Budurwar tayi maganar tana musu nuni da saman center table na Palon.

"Mun gode sosai."

Cewar Jiddarh still bata cire Niƙab dake fuskarta ba.

Ƙarisawa Humaira tayi Sannan ta ɗauki Juice a cup daga saman tray dake kan center table ɗin, sannan ta koma ta zauna suna ɗan taɓa fira sama sama kai daga ganin Yanayin da suke kasan ba wani sabo ne a tsakanin su ba.

Knocking ɗin ƙofar palon da suka ji ne. Yasa budurwar da ta buɗewa su jiddarh ƙofar palon.
Nufar ƙofar tana faɗin
"Mudai Gidan nan muna shan baƙi sosai, gashi kuma Mamy bata nan."

Ta ƙari sa maganar a daidai lokacin da ta buɗe ƙofar tana kallon kyawawan Ƴan matan da suke tsai tsai ye bakin ƙofar su Biyar, mace ɗaya ta gane cikin su.

Da sauri ta matsa gefe domin basu Hanya tana faÉ—in

"Lah Auntie Hameeda kece?, barkan ku dai ku shigo Please."

Ƙari sa shiga palon suka yi gaba ɗaya sannan suka zazzauna.

Kallon su Humaira bayi babu shiri ta waro idanu tana faÉ—in
"Kaga wani katari Hameeda Sagir kece dai ko kuwa gizo ne?."
Chapter 95 · 0% Book details