Sashe 61
Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"A'a sa'adah,wahala ai mai wucewa ce insha Allah bazaki sake shan wahala kamar wannan ba wurin haihuwa..... " Dakyar yasamu ya rarrasheta ta yi shiru ta daina kukan nan aka cigaba da lallaba ta su umma na kulawa da ita,shi kuwa jariri dayake yana samun abincinsa yana koshi nan da nan yasake zama kato dan ko Aryan baya iya daukarsa sai dai idan yana zaune abashi shi,itama mai jegon ba abarta abaya ba wurin murmurewa da sake kara samun kumari domin itama ta cika tayi kiba kamar ba itaba sai yanzu ta yarda da batun mutane da suke cewa kudi na gyara mutum haka duk muninka yana kara maka kyau,kafin arba'in tasamu ta warke tayi fess da ita amma duk da haka bata sakin jiki da khalil kuma shima baya takurawa saboda yana son ta huta sosai,kullum da daddare dai yana kasancewa dasu itada Aryan da Ayaan su raba dare a sashensa suna hira,anty salaha kuwa ganin Hanan ta warke yasata tattarawa ta tafi saboda tabar yara agida duk hankalinta yana garesu,
Tunda anty salaha ta tafi kuma Hanan ta koma sashen Khalil da kwana itada jararinsu can suke tafiya suyi baccinsu cikin nutsuwa da kulawa domin ko tashin dare Ayaan yayi zaiyi rigima khalil ke daukarsa ya rarrasheshi. Watan Ayaan biyu Hanan ta shirya ta tafi gida kuma itace har gombe domin ziyara tayi ba kadanba saida tayi sati biyu taje nan taje can duk wasu danginta da na Khalil lungu da sako babu inda bata je ba takai Ayaan anganshi wanda kamarsu daya da Aryan saboda duk Khalil suka debo,
Kafin ta baro gombe saida aka yimata kunshi da kitso sannan Zaid ya mayar da ita, lokacin da ta koma bata samu Khalil ba domin yatafi k'asar chairo wanda bata san dalili ba,gyara jikinta taci gaba dayi har izuwa ranar da zai dawo,bayan dawowarta da kwana biyu shima ya sauka amma office yawuce bai karaso gida ba sai dare,
Kwalliya taci sosai cikin doguwar riga ta material tasha turare mai sanyin kamshi,yana dauke da Ayaan a kafadarsa wanda ya karbeshi hannun umma Aryan na biye dashi,
A sashensa ya sameta tana shirya masa table ganin irin adon da ta caba yasashi yin murmushi ya nemi wuri ya zauna,
"Sannu da zuwa uncle...."
"Yawwa.... Irin wannan kwalliya haka? Ko anshirya karbata ne yau?"
Murmushi tayi ta karasa kusa dasu,
"Kai uncle....."
"Ai tambaya nayi,kuma shiyasa nayi miki da yaren da Aryan bazai ganeba, anshirya karbata yau?"
Kafada ta makale tace "A'a"
"Karya kike yau dai dole akarbeni tunda ai anhuta kuma zafin haihuwar yatafi...."
Dariya tayi ta mika hannu ta karbi Ayaan tana fadin,
"Zo nan mubar uncle yaje ya shirya yazo yaci abinci..."
Tare suka rankaya zuwa dakin nasa banda Aryan wanda yakoma wurin umma,ita ta taimaka masa yayi wanka sannan ya shirya cikin kayan shan iska saboda shi mutumne mai jin zafi gashi baida wata kiba ta azo agani amma sai jin zafi,falo suka koma ta bashi abinci yaci daga nan tatafi sashenta domin yin shirin bacci. Yau kam tayi shirin da Khalil bazai kirata da yar kauye ba itama yar birni ta zama domin rigar baccin da ta saka kadai ta isa tabbatar masa da haka kuma kalar da yafi murada ce wato fari,
Yana zaune rike da wani littafi a hannunsa kishingide saman sofa acikin bedroom dinsa ta shiga,bayan ta kwantar da Ayaan ta nufeshi,acikin jikinsa ta zauna tana cire hijabin dake jikinta,
"Wow....... Kinyi kyau" yafada yana shafa kitson kanta,tun anan labari yasoma canjawa har suka dangana ga gadon barcinshi amma kuma yau sam ta lura kamar baida kuzari kai kamar ma dan ita yake jagorantar tafiyar bawai dan kanshi ba,
"Uncle ko inkawo maka coffee din ne?"
"No"
Ita dai yau ganinsa take yi kamar wani marar lafiya kuma duk zumudinsa yau kam jikinsa asanyaye yake,
Bayan wani dogon lokaci tayi bacci ta farka ta ganshi zaune ya tallafe kumatunsa da hannunshi abin yayi mutukar bata mamaki, cike da bacci ta tashi zaune,
"Uncle wai lafiya kuwa? Meke damunka ne?"
Kamata yayi suka kwanta ya kwantar da kanshi a kirjinta bayan ya rungume ta,
"Babu abinda ke damuna,muyi bacci..."
"A'a uncle wallahi da akwai abinda ke damunka..."
"Babu"
Jin yaki fada mata yasata tureshi ta mike zata bar dakin tana masifa,
"Tunda baka daukeni abokiyar shawararka ba,kuma baka kallona a abokiyar tayaka farin ciki ko sabanin haka...."
Tashi yayi ya rikota dakyar ya kwantar da ita tana ta zizzillewa,binta yayi ya saka mata nauyinsa ta yadda bazata iya tashiba,
"Nifa bazan kwana adakin nanba...."
Dariya yayi sannan ya shafi kumatunta,
"Kwana kuma na nawa sa'adah? Jiya kam ai kin kwana saura yau kuma..."
"To ba ka ki ka fada min damuwarka ba"
"Sa'adah banda lafiya......... Insha Allah zan koma chairo next month zasuyi min surgery....."
Tashi zaune tayi yunkurin yi ya hanata babu bata lokaci tafara hawaye tana ta tambayar rashin lafiyar dake damunsa amma yaki fada kawai dai yace mata wai wani abune shima bai san menene ba zasu yimasa aiki,dakyar ya lallaba ta suka koma bacci,tun daga ranar hankalinta yaki kwanciya duk tabi ta damu dan gani takeyi kamar mutuwa zaiyi yabarta,shima kuma komai nashi cikin sanyin jiki yake gudanar dashi dan daga karshe ma cewa yayi zaiyi resigning yabar aiki hajiya ta hanashi,haka dai yaci gaba da fita aiki kusan kullum yana fama da zazzabi mai zafi,
Lokacin da zai koma chairo din tare da Hanan suka tafi kuma aranar da suka je aranar aka yimasa aikin,yasha wahala ba kadan ba amma kuma anyi cikin nasara nan tayita zaman jinyarsa har yafara samun lafiya,kullum cikin amsa wayar yan uwa daga gida Nigeria take,satinsu uku acan ya warke garau kuma yaji sauki sai lokacin yake sanar da ita wai cancer ce ta kamashi amma bata girmama ba ita aka cire masa,
Gida suka koma yaci gaba da al'amuransa gefe daya kuma yana kulawa da iyalinsa, itama dagewa tayi tana kulawa dashi domin bata son wata ta kwace mata shi bugu da kari kuma mijin matacciya take aure idan batayi da gaske ba zaiyita kewar matarsa da tunaninta, abinda bata saniba shi yanzu baida lokacin kara aure ko kula mace awaje saboda atsarinshi mace guda daya ta isheshi rayuwa.
Ganin wanda takeyi dominsa baya ta kowacce mace sai iya ita kadai yasata sakin jikinta nan tafara kasuwancinta tabude restaurant da boutique mai hadeda wurin saloon da gyaran jiki da kwalliya duk na manyan mata,idan Khalil ya tsareta da tambayar wai me zatayi da kudi sai tayi dariya tace abunda akeyi dasu nan kuwa iyayenta take taimakawa wanda bata da kamarsu kuma duk da Khalil na iya bakin kokarinsa amma itama gara tayi nata haka kuma sauran yan uwa da abokan arziki ai basai tazo tana cemasa bani bani ba lokuta da dama da nata take yin amfani.
Rana tsaka kuma Khalil ya daukesu ya mayar dasu k'asar Paris saboda karatun yaransa itama ba abarta abaya ba ta fada tata makarantar inda taci gaba da karatu kuma su basu cika zuwa bama sai shine ke zuwa,amma wannan karon saida yayi 3 months bai jeba,kuka Hanan tasaka masa awaya washe garin ranar sai gashi yazo lokacin dama har ta yaye Ayaan,
A bedroom dinta ya sauka tunda dama 2 bedrooms ne daya nata daya nasu Aryan,
"Wai sai yaushe za abawa su Aryan kani ne..."
"Hum um babu rana,garinsa da nisa...."
"Garinsa akusa yake ai kuwa saboda saida nataro gajiya ta gaba daya sannan nataho"
Turo baki tayi tana harararshi,
"Muda ka manta ma damu kaje kayi zamanka...."
"No,ni na isa mantawa da zuciyata......... Zo kiji wani abu"
Janyota yayi ya rungume ta yana fada mata irin girman matsayinta cikin zuciyarshi daga karshe kuma yashiga nuna mata a bayyane da bakinsa da hannayensa da dukkan gangar jikinsa gaba daya yana kara jaddada mata shi nata ne ita daya haka kuma ta daina kiransa da mijin matacciya shi mijin rayayyiya ne domin tuni ya maye gurbin Ramlat da Hanan tsakaninsa da Ramlat addu'a ce amma Hanan itace abokiyar rayuwarsa har gaban abada zai cigaba da kulawa da ita da nuna mata kauna da soyayya har tsufansu, wannan karon akasar Paris tasamu ciki kuma acan ta haihu cikin kulawar doctors da Khalil wanda ya tayata nakuda ta haifo yaronta santalele wanda gaba daya su Aryan suka tare masa kyau domin tamkar balarabe haka yake nan Khalil yayi masa huduba da Abubakar saddiq yana tsokanar Hanan wai wannan karon babu kukan dinki to sai muce Allah yaraya yakaro kazantar daki.
ALHAMDULILLAH
Godiya ta tabbata ga ubangiji Allah madaukakin sarki wanda yabani ikon kammala wannan littafi mai suna mijin matacciya, Allah ya yafe mana kuskuren dake ciki ya hadamu acikin ladan gaba daya tare daku masu karatu,kamar yadda nafada book dina na kudine duk wadda ta karanta batare da ta biya ba to yar uwa kisani Allah yana kallonki,bawai book dina kadai ba duk book din da akace na kudine yakamata mu kiyaye daukar hakkin wani domin Allah yana gafarta abinda ke tsakaninka dakai bawa amma baya yafe hakkin wani murinka tunawa da wannan,ina mutukar godiya ga masoyana wadanda ke nuna min kauna kuma suke tare dani koda yaushe Allah yabarmu tare,sai mun hadu acikin labari nagaba,taku ahar kullum kuma akoda yaushe Ummi A'isha nagode.
_*Ummi Shatu*_👌ðŸ»
Tunda anty salaha ta tafi kuma Hanan ta koma sashen Khalil da kwana itada jararinsu can suke tafiya suyi baccinsu cikin nutsuwa da kulawa domin ko tashin dare Ayaan yayi zaiyi rigima khalil ke daukarsa ya rarrasheshi. Watan Ayaan biyu Hanan ta shirya ta tafi gida kuma itace har gombe domin ziyara tayi ba kadanba saida tayi sati biyu taje nan taje can duk wasu danginta da na Khalil lungu da sako babu inda bata je ba takai Ayaan anganshi wanda kamarsu daya da Aryan saboda duk Khalil suka debo,
Kafin ta baro gombe saida aka yimata kunshi da kitso sannan Zaid ya mayar da ita, lokacin da ta koma bata samu Khalil ba domin yatafi k'asar chairo wanda bata san dalili ba,gyara jikinta taci gaba dayi har izuwa ranar da zai dawo,bayan dawowarta da kwana biyu shima ya sauka amma office yawuce bai karaso gida ba sai dare,
Kwalliya taci sosai cikin doguwar riga ta material tasha turare mai sanyin kamshi,yana dauke da Ayaan a kafadarsa wanda ya karbeshi hannun umma Aryan na biye dashi,
A sashensa ya sameta tana shirya masa table ganin irin adon da ta caba yasashi yin murmushi ya nemi wuri ya zauna,
"Sannu da zuwa uncle...."
"Yawwa.... Irin wannan kwalliya haka? Ko anshirya karbata ne yau?"
Murmushi tayi ta karasa kusa dasu,
"Kai uncle....."
"Ai tambaya nayi,kuma shiyasa nayi miki da yaren da Aryan bazai ganeba, anshirya karbata yau?"
Kafada ta makale tace "A'a"
"Karya kike yau dai dole akarbeni tunda ai anhuta kuma zafin haihuwar yatafi...."
Dariya tayi ta mika hannu ta karbi Ayaan tana fadin,
"Zo nan mubar uncle yaje ya shirya yazo yaci abinci..."
Tare suka rankaya zuwa dakin nasa banda Aryan wanda yakoma wurin umma,ita ta taimaka masa yayi wanka sannan ya shirya cikin kayan shan iska saboda shi mutumne mai jin zafi gashi baida wata kiba ta azo agani amma sai jin zafi,falo suka koma ta bashi abinci yaci daga nan tatafi sashenta domin yin shirin bacci. Yau kam tayi shirin da Khalil bazai kirata da yar kauye ba itama yar birni ta zama domin rigar baccin da ta saka kadai ta isa tabbatar masa da haka kuma kalar da yafi murada ce wato fari,
Yana zaune rike da wani littafi a hannunsa kishingide saman sofa acikin bedroom dinsa ta shiga,bayan ta kwantar da Ayaan ta nufeshi,acikin jikinsa ta zauna tana cire hijabin dake jikinta,
"Wow....... Kinyi kyau" yafada yana shafa kitson kanta,tun anan labari yasoma canjawa har suka dangana ga gadon barcinshi amma kuma yau sam ta lura kamar baida kuzari kai kamar ma dan ita yake jagorantar tafiyar bawai dan kanshi ba,
"Uncle ko inkawo maka coffee din ne?"
"No"
Ita dai yau ganinsa take yi kamar wani marar lafiya kuma duk zumudinsa yau kam jikinsa asanyaye yake,
Bayan wani dogon lokaci tayi bacci ta farka ta ganshi zaune ya tallafe kumatunsa da hannunshi abin yayi mutukar bata mamaki, cike da bacci ta tashi zaune,
"Uncle wai lafiya kuwa? Meke damunka ne?"
Kamata yayi suka kwanta ya kwantar da kanshi a kirjinta bayan ya rungume ta,
"Babu abinda ke damuna,muyi bacci..."
"A'a uncle wallahi da akwai abinda ke damunka..."
"Babu"
Jin yaki fada mata yasata tureshi ta mike zata bar dakin tana masifa,
"Tunda baka daukeni abokiyar shawararka ba,kuma baka kallona a abokiyar tayaka farin ciki ko sabanin haka...."
Tashi yayi ya rikota dakyar ya kwantar da ita tana ta zizzillewa,binta yayi ya saka mata nauyinsa ta yadda bazata iya tashiba,
"Nifa bazan kwana adakin nanba...."
Dariya yayi sannan ya shafi kumatunta,
"Kwana kuma na nawa sa'adah? Jiya kam ai kin kwana saura yau kuma..."
"To ba ka ki ka fada min damuwarka ba"
"Sa'adah banda lafiya......... Insha Allah zan koma chairo next month zasuyi min surgery....."
Tashi zaune tayi yunkurin yi ya hanata babu bata lokaci tafara hawaye tana ta tambayar rashin lafiyar dake damunsa amma yaki fada kawai dai yace mata wai wani abune shima bai san menene ba zasu yimasa aiki,dakyar ya lallaba ta suka koma bacci,tun daga ranar hankalinta yaki kwanciya duk tabi ta damu dan gani takeyi kamar mutuwa zaiyi yabarta,shima kuma komai nashi cikin sanyin jiki yake gudanar dashi dan daga karshe ma cewa yayi zaiyi resigning yabar aiki hajiya ta hanashi,haka dai yaci gaba da fita aiki kusan kullum yana fama da zazzabi mai zafi,
Lokacin da zai koma chairo din tare da Hanan suka tafi kuma aranar da suka je aranar aka yimasa aikin,yasha wahala ba kadan ba amma kuma anyi cikin nasara nan tayita zaman jinyarsa har yafara samun lafiya,kullum cikin amsa wayar yan uwa daga gida Nigeria take,satinsu uku acan ya warke garau kuma yaji sauki sai lokacin yake sanar da ita wai cancer ce ta kamashi amma bata girmama ba ita aka cire masa,
Gida suka koma yaci gaba da al'amuransa gefe daya kuma yana kulawa da iyalinsa, itama dagewa tayi tana kulawa dashi domin bata son wata ta kwace mata shi bugu da kari kuma mijin matacciya take aure idan batayi da gaske ba zaiyita kewar matarsa da tunaninta, abinda bata saniba shi yanzu baida lokacin kara aure ko kula mace awaje saboda atsarinshi mace guda daya ta isheshi rayuwa.
Ganin wanda takeyi dominsa baya ta kowacce mace sai iya ita kadai yasata sakin jikinta nan tafara kasuwancinta tabude restaurant da boutique mai hadeda wurin saloon da gyaran jiki da kwalliya duk na manyan mata,idan Khalil ya tsareta da tambayar wai me zatayi da kudi sai tayi dariya tace abunda akeyi dasu nan kuwa iyayenta take taimakawa wanda bata da kamarsu kuma duk da Khalil na iya bakin kokarinsa amma itama gara tayi nata haka kuma sauran yan uwa da abokan arziki ai basai tazo tana cemasa bani bani ba lokuta da dama da nata take yin amfani.
Rana tsaka kuma Khalil ya daukesu ya mayar dasu k'asar Paris saboda karatun yaransa itama ba abarta abaya ba ta fada tata makarantar inda taci gaba da karatu kuma su basu cika zuwa bama sai shine ke zuwa,amma wannan karon saida yayi 3 months bai jeba,kuka Hanan tasaka masa awaya washe garin ranar sai gashi yazo lokacin dama har ta yaye Ayaan,
A bedroom dinta ya sauka tunda dama 2 bedrooms ne daya nata daya nasu Aryan,
"Wai sai yaushe za abawa su Aryan kani ne..."
"Hum um babu rana,garinsa da nisa...."
"Garinsa akusa yake ai kuwa saboda saida nataro gajiya ta gaba daya sannan nataho"
Turo baki tayi tana harararshi,
"Muda ka manta ma damu kaje kayi zamanka...."
"No,ni na isa mantawa da zuciyata......... Zo kiji wani abu"
Janyota yayi ya rungume ta yana fada mata irin girman matsayinta cikin zuciyarshi daga karshe kuma yashiga nuna mata a bayyane da bakinsa da hannayensa da dukkan gangar jikinsa gaba daya yana kara jaddada mata shi nata ne ita daya haka kuma ta daina kiransa da mijin matacciya shi mijin rayayyiya ne domin tuni ya maye gurbin Ramlat da Hanan tsakaninsa da Ramlat addu'a ce amma Hanan itace abokiyar rayuwarsa har gaban abada zai cigaba da kulawa da ita da nuna mata kauna da soyayya har tsufansu, wannan karon akasar Paris tasamu ciki kuma acan ta haihu cikin kulawar doctors da Khalil wanda ya tayata nakuda ta haifo yaronta santalele wanda gaba daya su Aryan suka tare masa kyau domin tamkar balarabe haka yake nan Khalil yayi masa huduba da Abubakar saddiq yana tsokanar Hanan wai wannan karon babu kukan dinki to sai muce Allah yaraya yakaro kazantar daki.
ALHAMDULILLAH
Godiya ta tabbata ga ubangiji Allah madaukakin sarki wanda yabani ikon kammala wannan littafi mai suna mijin matacciya, Allah ya yafe mana kuskuren dake ciki ya hadamu acikin ladan gaba daya tare daku masu karatu,kamar yadda nafada book dina na kudine duk wadda ta karanta batare da ta biya ba to yar uwa kisani Allah yana kallonki,bawai book dina kadai ba duk book din da akace na kudine yakamata mu kiyaye daukar hakkin wani domin Allah yana gafarta abinda ke tsakaninka dakai bawa amma baya yafe hakkin wani murinka tunawa da wannan,ina mutukar godiya ga masoyana wadanda ke nuna min kauna kuma suke tare dani koda yaushe Allah yabarmu tare,sai mun hadu acikin labari nagaba,taku ahar kullum kuma akoda yaushe Ummi A'isha nagode.
_*Ummi Shatu*_👌ðŸ»