Sashe 43
Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari da burin yin aiki ta tashi tana son hada humrah da turaren wanka kuma cikin nasara ta yisu kamar dama can tajima tana yi,gaba daya sashenta gaurayewa yayi da kamshi kamar me ita kanta kamshin take yi saboda kayan hadin da tayi amfani dasu masu kyau ne da tsada sannan ta dan kakkara da wasu turarukan wanda ma hajja hasinah bata saka musu suba, lokacin da ta kammala saida ta yiyyi wa kayan hotuna sannan ta turawa hajja hasinah,kowa na gidan saida ta diba masa ta saka masa acikin toilet daga Aryan har umma har Khalil shi amma Khalil a toilet dinshi na falo ta ajiye masa dan ba taba shiga master bedroom dinshi ma tayiba har yau bata san kalar bedroom dinsa ba ita kuma humrar dama kanta ta hadawa shiyasa bata bawa kowa ba,ji tayi idanuwanta suna yi mata kekayi nan ta sosa kamar kuma dama jira suke suka fara yimata radadi sai kuma hawaye kafin dare itama tuni har ido ya ruruce yahau ciwo ya kada yayi jajur, lokacin da umma tagani cewa tayi to awurin Khalil ta dauka sai akira mata likita itama yadubata, itama tasan awurin nashi ta dauka dama tun lokacin da sukaje falonsa ta kalli kwayar idanuwanshi tafara jin nata kwayar idon suna dan tsikarinta kadan,
Har 12 dare bata yi bacci ba sakamakon ciwon da idanuwanta keyi ganin babu haza yasata yimasa text wai bata da lafiya ciwon ido ke damunta ko zai taimaka ya Kira mata Dr? Reply taga yayi mata da wai tazo,
Tashi tayi ta sauka daga kan gadon ta saka hijabinta da silifas tafita,yana kishingide akan kujera kafarshi daya saman center table yana kallon CNN ta bude kofar ta shiga bakinta dauke da sallama, idanuwanshi akan TV ya amsa batare da ya kalleta ba. Wuri ta samu ta zauna can nesa dashi sosai amma duk da haka sai da hancinsa ya jiyo masa masifaffen kamshin humrar dake tashi jikinta,shiru yayi ya dan lumshe idanuwanshi na dan wani lokaci sannan ya kalleta da lumsassun idanuwanshi wadanda suka kara yin jaa,saurin kawar idonta tayi daga kanshi dan tunda ta zauna take kallonsa kamar zata cinyeshi,
" Me kika ce....?" Taji ya tambayeta bayan ya dauke idonshi daga kanta,
"Idanuwana ke ciwo..." Tabashi amsa tana wasa da bakin hijab din jikinta,
"Me yasamu idon?" Ya sake tambaya,
"Awurinka na dauka..."
Jin abinda tace yasashi daga ido ya kalleta,
"Awurina kuma?"
"Uhmmmm"
Shiru yayi na dan wasu mintuna sannan cikin rashin daga murya taji yace,
"Shiga bedroom dina zaki ga magani ki dauko...."
Har ta mike bata san me ya tuna ba taji yayi saurin cewa,
"Zauna kawai bari in dauko.."
Daga haka yatashi yawuce cikin bedroom dinshi nan tabishi da kallo farar t shirt ce jikinsa da farin wando wanda da kadan yawuce gwiwarsa shima fa ta lura idan yasamu dama akwai gayu idan zai fita ne kullum cikin manyan kaya,
Koda yashiga cikin dakin sai da yatsaya gaban bedside drawer dinshi wanda ke dauke da hoton Aryan da hoton Ramlat cikin wasu frame kanana guda biyu masu kyau,ya dan jima yana duban hoton kamar mai son gano wani abu aciki sannan ya dauki maganin yafita,
Tana zaune inda yatafi ya barta zama yayi saman kujerar da yake zaune tun farko, sannan ya dora mata maganin kan center table din gabanshi,
"Zo ki dauka"
Anutse ta tashi tazo ta dauka tana kallonsa alamun neman karin bayani,
"Ki disa a idon naki idan zaki kwanta"
"To kai kuma fa?" Ta fada muryarta na rawa kamar wacce ke jin tsoron fada,
"Ba matsala kije dashi"
"Nagode,sai da safe"
Kai kurum ya daga mata ta juya ta fita tana jinjina rashin son magana irin na wannan bawan Allah dan idan yana yinta kamar anyi masa dole.
Kamar ciwon idon nasu layi yake bi washe gari shima Aryan yatashi da shi duk idanuwan nashi a like haka suka yita fama har tsawon sati biyu umma ce kadai bata yi wannan ciwon idon nasu ba,
Abangaren abubuwan da take koyo kuwa yanzu tasake bada himma sosai kuma alhamdulillah ta koyi abubuwa masu yawa kuma tana ma kan koyo wani abun burgewa ma shine ta kan jajurce wurin gwada dukkan abun da aka koyar dasu,
Yauma kamar kullum tana zaune falon kasa itada umma kowa yana aikinsa maganin zaman banza,ita umma tana karasa mificin da take sakawa ita kuma Hanan tana sabulun gyaran jiki wanda hajja hasinah ta koyar dasu cikin satin nan,muryar Aryan tajiyo yana ta zuba surutun nashi ko shida waye oho,
"Kinji d'an naki can ko wa ya samo yabaro karatun islamiyyar tashi kuma?" Umma ta fada tana kokarin bantarar goronta,kafin Hanan tayi magana tuni anbude kofa, dukkansu ita da umma d'aga ido sukayi suka mayar da hankalinsu kan wad'anda ke shigowa,Zaid ne rike da trolley yana janta Aryan na biye dashi shida wata kyakkyawar matashiyar mata sai zuba mata surutu yake yi,
Ganinsu yasa umma fadada fara'arta tana fadin lale marhabun da mutanen gombe,itama Hanan ba abarta abaya ba wurin yimusu barka da zuwa,
Kujera duk suka samu suka zazzauna ana kokarin gaisawa,jin muryar matar yasa Hanan dan sake kallonta lokacin da taji umma tace,
"Maamy mutanen London..... Saukar yaushe?"
"Ai zan kai 3 weeks da dawowa.... Koda yaushe Khalil na mitar wai bana zumunci naki zumunci shiyasa shima ya shareni ko Aryan baya kai min to yanzu gani nazo har gida....."
"Allah sarki ai kuwa kin kyauta.... Sannu da zuwa"
"Ina yini?" Hanan ta fada tana kallon ta,dan murmushi maamy tayi sannan ta amsa cikin fara'a,
"Lafiya lau.... Mun sameku lafiya?"
"Lafiya lau" Hanan ta amsa mata tana tattare kayanta tunda dama ta gama,sama ta haura domin kai kayan bayan sun gaisa da zaid, lokacin da take saukowa tana jiyo muryar Zaid yana cewa umma,
"Ai ni umma kasa gane Anty maamy nayi Yaya Khalil ma nasan dakyar idan zai ganeta dan tafi 4 years rabonta da kasar nan"
Dariya maamy tayi ta cire farin glass din dake idonta,
"Zaid kaima fa baka da dama"
Ita dai hanan samun wuri tayi ta zauna tana kallonsu da sauraren hirar da suke yi yayinda ita kuma Aryan yazo ya haye cinyarta. Kasancewar ga dakuna nan reras agidan daki guda aka warewa anty maamy ta shigar da kayanta lokacin anata kiraye kirayen sallar magriba,suma su Hanan basu zauna ba kowa dakinshi yawuce domin gabatar da salla shikuma Aryan suka fita tare da Zaid,
Hanan bata samu fitowa ba sai bayan sallar ishah saboda tana can dakinta tana chaten da su salaha tana tuttura musu abubuwan da ta gwaggwada na daga cikin wad'anda ta koya,bayan sallar ishah tafita domin cikinta yafara kiran ciroma,tana sanye da dark blue din doguwar riga yar kanti da hijab asama,falon babu kowa hatta umma bata fito ba,zama tayi kan dining bayan ta debi abincin da zata ci,tana tsaka da cin abincinta Zaid suka shigo shida Aryan,suna zama saiga umma itama tafito nan suka cigaba da hirar su suna cin abinci,
K'arfe 9 tabar falon takoma sashenta bata sake fitowa ba sai 11 saura lokacin Khalil yadawo suna can falonshi gaba dayansu harda umma,sashen nashi itama ta nufa jikinta na fitar da wani kamshi mai sanyi,cikin nutsuwa ta bude kofar falon ta shiga abinda idanuwanta suka gane mata shine yasanya ta taji jikinta yayi sanyi cikin rashin kwarin gwiwa ta juya zata koma...........................âœðŸ?
_Book din mijin matacciya na kudine game bukatar siya sai atura 200 ta account din Aisha Ibrahim, 3112877210 first bank,sai atura shaidar biya ta WhatsApp number dina 07044644433 ko kuma atura recharge card da shaidar biya ta number din._
*_Ummi Shatu_*👌ðŸ»
8/14/20, 10:13 AM - Ummi Tandama: *Book din mijin matacciya na kudine game bukatar siya sai atura 200 ta account din Aisha Ibrahim, 3112877210 first bank,sai atura shaidar biya ta WhatsApp number dina 07044644433 ko kuma atura recharge card da shaidar biya ta number din.*
*39*
***Muryar umma tajiyo tana kiranta lokacin da take kokarin komawa,
"Sa'adatu ina kuma zakije.....? Ki karaso mana ayi dake"
Babu musu tafasa fita ta shiga,kujera ta samu ta zauna tana kallon kowa, Khalil ne zaune kan doguwar kujera shida Aryan wanda ke bacci akusa dashi sai Anty maamy dake kujerar kusa dashi tana sanye cikin brown colour din doguwar riga sai Zaid dake kujerar kusa da ita amma shi gaba daya hankalinsa yana ga wayar dake hannunsa yana daddannawa ita kuma na zaune opposite dinsu tana kallonsu,akusa da umma Hanan ta zauna tana yiwa Khalil sannu da zuwa sannan tana sake kallon Anty maamy dan sai yanzu ne ma tayi mata kallon tsaf,doguwa ce sosai dan idanma Khalil zai fita tsayi to da kadan zai fita, fatarta mai haske ce sosai wadda hutu da jin dadi suka sake haskaka ta, siririya ce Sam bata da kiba amma fa kuma tana da masifar kyau kamar ita tayi kanta tana da diri da sura,
Hanan wani abu taji ya tsaya mata arai sakamakon murmushin da taga Khalil nayi lokacin da suke yin hira da Mami,
"Maamy uwar son girma.... Wai dan Allah har yanzu baki daina son girman nan ba? Lokacin da kina yarinya fa har kuka kike yi idan akace kece karama acikinmu...."
Wata dariya mai kayatarwa maamy tayi sannan cikin murmushi tace,
"Woohhh Khalil ka iya bada mutane wallahi,yanzu da girmana kake fada min haka agaban Zaid..... Kana gani na kusa diban surukai,sahla fa jss 3 take Jawad jss 2 faruk ne kadai a primary school"
"To kuma shine me? Kaji yarinyar nan da wata magana,to nida Khalid da ace da wuri mukayi aure da ba tuni mun aurar da 'yaya ba....."
"To wai Khalil da kai da Khalid din da me kuka fini? How many years kuka ban? Da me kwado yafi gaya ne wai?"
Dariya Khalil yayi yasake kishingida jikin kujera alamar yana jin dadin wannan hirar,
"Wai dan Allah shekararki nawa? Fada min"
"Am 39 by the way...."
"Lallai maamy kina da son shekaru,to yarinya ai ko mu bamuyi 39 ba 38 muke har yanzu.... Ke ai ba zaki fi 36 ba ko 35..."
"Haba haba Ibrahim....haba Ibrahim ya zaka fadi haka? Nice 35 ko 36? Gaskiya nafi haka"
"Au wai ko dan kinga kin hayayyafa kin tara yara shine kike karawa kanki shekaru? Saboda kinga su sahla sun fara girma ko.... To ai ba anan takeba"
Har 12 dare bata yi bacci ba sakamakon ciwon da idanuwanta keyi ganin babu haza yasata yimasa text wai bata da lafiya ciwon ido ke damunta ko zai taimaka ya Kira mata Dr? Reply taga yayi mata da wai tazo,
Tashi tayi ta sauka daga kan gadon ta saka hijabinta da silifas tafita,yana kishingide akan kujera kafarshi daya saman center table yana kallon CNN ta bude kofar ta shiga bakinta dauke da sallama, idanuwanshi akan TV ya amsa batare da ya kalleta ba. Wuri ta samu ta zauna can nesa dashi sosai amma duk da haka sai da hancinsa ya jiyo masa masifaffen kamshin humrar dake tashi jikinta,shiru yayi ya dan lumshe idanuwanshi na dan wani lokaci sannan ya kalleta da lumsassun idanuwanshi wadanda suka kara yin jaa,saurin kawar idonta tayi daga kanshi dan tunda ta zauna take kallonsa kamar zata cinyeshi,
" Me kika ce....?" Taji ya tambayeta bayan ya dauke idonshi daga kanta,
"Idanuwana ke ciwo..." Tabashi amsa tana wasa da bakin hijab din jikinta,
"Me yasamu idon?" Ya sake tambaya,
"Awurinka na dauka..."
Jin abinda tace yasashi daga ido ya kalleta,
"Awurina kuma?"
"Uhmmmm"
Shiru yayi na dan wasu mintuna sannan cikin rashin daga murya taji yace,
"Shiga bedroom dina zaki ga magani ki dauko...."
Har ta mike bata san me ya tuna ba taji yayi saurin cewa,
"Zauna kawai bari in dauko.."
Daga haka yatashi yawuce cikin bedroom dinshi nan tabishi da kallo farar t shirt ce jikinsa da farin wando wanda da kadan yawuce gwiwarsa shima fa ta lura idan yasamu dama akwai gayu idan zai fita ne kullum cikin manyan kaya,
Koda yashiga cikin dakin sai da yatsaya gaban bedside drawer dinshi wanda ke dauke da hoton Aryan da hoton Ramlat cikin wasu frame kanana guda biyu masu kyau,ya dan jima yana duban hoton kamar mai son gano wani abu aciki sannan ya dauki maganin yafita,
Tana zaune inda yatafi ya barta zama yayi saman kujerar da yake zaune tun farko, sannan ya dora mata maganin kan center table din gabanshi,
"Zo ki dauka"
Anutse ta tashi tazo ta dauka tana kallonsa alamun neman karin bayani,
"Ki disa a idon naki idan zaki kwanta"
"To kai kuma fa?" Ta fada muryarta na rawa kamar wacce ke jin tsoron fada,
"Ba matsala kije dashi"
"Nagode,sai da safe"
Kai kurum ya daga mata ta juya ta fita tana jinjina rashin son magana irin na wannan bawan Allah dan idan yana yinta kamar anyi masa dole.
Kamar ciwon idon nasu layi yake bi washe gari shima Aryan yatashi da shi duk idanuwan nashi a like haka suka yita fama har tsawon sati biyu umma ce kadai bata yi wannan ciwon idon nasu ba,
Abangaren abubuwan da take koyo kuwa yanzu tasake bada himma sosai kuma alhamdulillah ta koyi abubuwa masu yawa kuma tana ma kan koyo wani abun burgewa ma shine ta kan jajurce wurin gwada dukkan abun da aka koyar dasu,
Yauma kamar kullum tana zaune falon kasa itada umma kowa yana aikinsa maganin zaman banza,ita umma tana karasa mificin da take sakawa ita kuma Hanan tana sabulun gyaran jiki wanda hajja hasinah ta koyar dasu cikin satin nan,muryar Aryan tajiyo yana ta zuba surutun nashi ko shida waye oho,
"Kinji d'an naki can ko wa ya samo yabaro karatun islamiyyar tashi kuma?" Umma ta fada tana kokarin bantarar goronta,kafin Hanan tayi magana tuni anbude kofa, dukkansu ita da umma d'aga ido sukayi suka mayar da hankalinsu kan wad'anda ke shigowa,Zaid ne rike da trolley yana janta Aryan na biye dashi shida wata kyakkyawar matashiyar mata sai zuba mata surutu yake yi,
Ganinsu yasa umma fadada fara'arta tana fadin lale marhabun da mutanen gombe,itama Hanan ba abarta abaya ba wurin yimusu barka da zuwa,
Kujera duk suka samu suka zazzauna ana kokarin gaisawa,jin muryar matar yasa Hanan dan sake kallonta lokacin da taji umma tace,
"Maamy mutanen London..... Saukar yaushe?"
"Ai zan kai 3 weeks da dawowa.... Koda yaushe Khalil na mitar wai bana zumunci naki zumunci shiyasa shima ya shareni ko Aryan baya kai min to yanzu gani nazo har gida....."
"Allah sarki ai kuwa kin kyauta.... Sannu da zuwa"
"Ina yini?" Hanan ta fada tana kallon ta,dan murmushi maamy tayi sannan ta amsa cikin fara'a,
"Lafiya lau.... Mun sameku lafiya?"
"Lafiya lau" Hanan ta amsa mata tana tattare kayanta tunda dama ta gama,sama ta haura domin kai kayan bayan sun gaisa da zaid, lokacin da take saukowa tana jiyo muryar Zaid yana cewa umma,
"Ai ni umma kasa gane Anty maamy nayi Yaya Khalil ma nasan dakyar idan zai ganeta dan tafi 4 years rabonta da kasar nan"
Dariya maamy tayi ta cire farin glass din dake idonta,
"Zaid kaima fa baka da dama"
Ita dai hanan samun wuri tayi ta zauna tana kallonsu da sauraren hirar da suke yi yayinda ita kuma Aryan yazo ya haye cinyarta. Kasancewar ga dakuna nan reras agidan daki guda aka warewa anty maamy ta shigar da kayanta lokacin anata kiraye kirayen sallar magriba,suma su Hanan basu zauna ba kowa dakinshi yawuce domin gabatar da salla shikuma Aryan suka fita tare da Zaid,
Hanan bata samu fitowa ba sai bayan sallar ishah saboda tana can dakinta tana chaten da su salaha tana tuttura musu abubuwan da ta gwaggwada na daga cikin wad'anda ta koya,bayan sallar ishah tafita domin cikinta yafara kiran ciroma,tana sanye da dark blue din doguwar riga yar kanti da hijab asama,falon babu kowa hatta umma bata fito ba,zama tayi kan dining bayan ta debi abincin da zata ci,tana tsaka da cin abincinta Zaid suka shigo shida Aryan,suna zama saiga umma itama tafito nan suka cigaba da hirar su suna cin abinci,
K'arfe 9 tabar falon takoma sashenta bata sake fitowa ba sai 11 saura lokacin Khalil yadawo suna can falonshi gaba dayansu harda umma,sashen nashi itama ta nufa jikinta na fitar da wani kamshi mai sanyi,cikin nutsuwa ta bude kofar falon ta shiga abinda idanuwanta suka gane mata shine yasanya ta taji jikinta yayi sanyi cikin rashin kwarin gwiwa ta juya zata koma...........................âœðŸ?
_Book din mijin matacciya na kudine game bukatar siya sai atura 200 ta account din Aisha Ibrahim, 3112877210 first bank,sai atura shaidar biya ta WhatsApp number dina 07044644433 ko kuma atura recharge card da shaidar biya ta number din._
*_Ummi Shatu_*👌ðŸ»
8/14/20, 10:13 AM - Ummi Tandama: *Book din mijin matacciya na kudine game bukatar siya sai atura 200 ta account din Aisha Ibrahim, 3112877210 first bank,sai atura shaidar biya ta WhatsApp number dina 07044644433 ko kuma atura recharge card da shaidar biya ta number din.*
*39*
***Muryar umma tajiyo tana kiranta lokacin da take kokarin komawa,
"Sa'adatu ina kuma zakije.....? Ki karaso mana ayi dake"
Babu musu tafasa fita ta shiga,kujera ta samu ta zauna tana kallon kowa, Khalil ne zaune kan doguwar kujera shida Aryan wanda ke bacci akusa dashi sai Anty maamy dake kujerar kusa dashi tana sanye cikin brown colour din doguwar riga sai Zaid dake kujerar kusa da ita amma shi gaba daya hankalinsa yana ga wayar dake hannunsa yana daddannawa ita kuma na zaune opposite dinsu tana kallonsu,akusa da umma Hanan ta zauna tana yiwa Khalil sannu da zuwa sannan tana sake kallon Anty maamy dan sai yanzu ne ma tayi mata kallon tsaf,doguwa ce sosai dan idanma Khalil zai fita tsayi to da kadan zai fita, fatarta mai haske ce sosai wadda hutu da jin dadi suka sake haskaka ta, siririya ce Sam bata da kiba amma fa kuma tana da masifar kyau kamar ita tayi kanta tana da diri da sura,
Hanan wani abu taji ya tsaya mata arai sakamakon murmushin da taga Khalil nayi lokacin da suke yin hira da Mami,
"Maamy uwar son girma.... Wai dan Allah har yanzu baki daina son girman nan ba? Lokacin da kina yarinya fa har kuka kike yi idan akace kece karama acikinmu...."
Wata dariya mai kayatarwa maamy tayi sannan cikin murmushi tace,
"Woohhh Khalil ka iya bada mutane wallahi,yanzu da girmana kake fada min haka agaban Zaid..... Kana gani na kusa diban surukai,sahla fa jss 3 take Jawad jss 2 faruk ne kadai a primary school"
"To kuma shine me? Kaji yarinyar nan da wata magana,to nida Khalid da ace da wuri mukayi aure da ba tuni mun aurar da 'yaya ba....."
"To wai Khalil da kai da Khalid din da me kuka fini? How many years kuka ban? Da me kwado yafi gaya ne wai?"
Dariya Khalil yayi yasake kishingida jikin kujera alamar yana jin dadin wannan hirar,
"Wai dan Allah shekararki nawa? Fada min"
"Am 39 by the way...."
"Lallai maamy kina da son shekaru,to yarinya ai ko mu bamuyi 39 ba 38 muke har yanzu.... Ke ai ba zaki fi 36 ba ko 35..."
"Haba haba Ibrahim....haba Ibrahim ya zaka fadi haka? Nice 35 ko 36? Gaskiya nafi haka"
"Au wai ko dan kinga kin hayayyafa kin tara yara shine kike karawa kanki shekaru? Saboda kinga su sahla sun fara girma ko.... To ai ba anan takeba"