Sashe 50
Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai lokacin ta bude idonta ta kalleshi shima ita yake kallo ko kiftawa bayayi ita dai tasan kawai yafada ne amma ya za ayi yabata Aryan yace wai sutafi duk inda zataje ai ko giyar wake yakesha bata jin zata yi masa tasiri anan,
Kai ya jijjiga mata alamar tabbacin abinda yafada,daga haka ya saketa daga rikon da yayi mata yawuce yafita yana kokarin gyara necktie dinshi,
Tafi minti biyar tsaye wurin ta kasa koda kwakkwaran motsi har umma barira ta karaso tazo tana mai sake bata hakuri akan karta tafi tunda bada mijinta sukayi fada ba to babu amfanin tabar gidan wai da sunan yaji,
Juyawa tayi ta ja akwatinta ta nufi ciki dakyar ma take jan akwatin saboda kayan da ta loda ba kadan bane sai kace wacce idan ta tafi zatayi shekara agidan,har bedroom dinta umma ta rakata tana sake bata baki tana cemata kowa kagani agidansa hakuri yake yi amma akwai matsalar da take tare dashi,
Bayan fitar umma Data ta kunna awayarta ta hau online saboda tana son ta dan debewa kanta kewa amma acan kasan ranta ta kuduri aniyar itafa bazata cigaba da zama da anty maamy ba sai dai ayi wacce za ayi.
Har Khalil yaje office bai daina mamakin abinda Hanan tayi ba,to wai me zai kira wannan lamarin nata dashi? Kishi ko kuruciya? Gaba daya yarinya ta dage sai ta kori maamy daga gidan,yana shiga office kiran maamy yashigo masa, dauka yayi muryarshi asanyaye kamar kullum,
"Ibrahim ni nagama shirya kayana zan wuce gombe......"
Dan jimm yayi sannan yace,
"Ban gane zaki wuce gombe ba..."
"Ehh zan koma gidan ubana mana,inbanda matarka ta samu dama wai har ni zata yiwa gorin gida? Taje ta tambaya waye ubana,kai kanka kasan ubana yanada gidajen da bazasu lissafu ba,ni kaina inada gidaje sunfi goma mallakina amma wai ni ake yiwa gori akan gida nida gidan mijina akasar turai yake amma wai yau saboda nazo gidanka karamar yarinyar da bata fi sa'ar autar gidanmu ba take kokarin wulakanta ni..... Nagode"
Kitt ta katse wayar,rabuwa yayi da ita bai kara kiranta ba saboda yasan yanzu ranta abace yake ko daga kalaman da take yi yasan akule take maamy kuma badai zuciya ba,rabuwa yayi da ita har zuwa yamma lokacin da zai tashi daga office inyaso sai yabita can gomben ya wanke kansa.
Misalin karfe 6 yatashi daga office kuma direct hanyar gombe suka kama wanda basu suka isa ba sai bayan sallar magriba,salla yafara yi sannan ya karasa gidan Alhaji Idris kanwa mahaifin maamy,bai samu abban agida ba kasancewar baya gari, Jawad yatura yace yayi masa sallama da momyn su nan Jawad din ya ruga da gudu ya nufi can cikin gida,
Maamy tana gaban mirror tana tsala kwalliya tamkar wata budurwa dan ko da wasa bata daukar kanta a matsayin wata babba ta azo agani duk da tana da samarin yaya da budurwar 'ya,
"Mommy kizo inji uncle Khalil...."
"Yana ina?"
"Yana falon abba na kasa"
"Ina zuwa to"
Fita jawad yayi ita kuma ta tashi ta karasa shiryawa cikin doguwar riga ja tasha turare sannan ta dauki dan siririn mayafinta ta fita tana takunta mai cike da nutsuwa da daukar hankali,
Zaune ta sameshi ya dora kafarshi daya akan daya yana duba wayarshi,zama tayi gefenshi bayan tayi masa sallama,
"Haba amarya irin wannan fushi haka kuma? Sai kace dani akayi fadan....."
Wani kallo tayi masa kafin ta rausayar da kanta gefe,
"Ai wannan matar taka sai Kai..... Kasan wani abu? Wallahi bazan zauna gida daya da ita ba, tun wuri ma ni ka sama min gida amma banda wannan..... Ban son rashin kunya"
Murmushi Khalil yayi ya shafi sajensa,
"Kinji tsoro kenan?"
"Ba maganar tsoro anan fa Ibrahim gaskiya ce"
"To Allah dai yabaki hakuri,dan Allah ki dauki abinda yafaru yau amatsayin ba komai ba saboda kinga ita yarinya ce,yanzu ne ma take sanin yaya rayuwar take......"
"Nifa banda case da ita,kawai nidai bukatata awurinka shine karka hadamu gida daya dan bazamu zauna lafiya ba...."
"Baki da matsala a wannan bangaren Maryam,insha Allah zanyi yanda kike so......., Yanzu ina son zan karasa wurin hajiya mu gaisa sai inkoma Abuja,dan nan nafara zuwa"
"Ayya babu matsala,ka gaida min da ita"
"Zata ji insha Allah, shikenan intafi an sallameni?"
Murmushi tayi ta dan fara idanuwanta alamun shagwaba,
"Da ance maka kai mai laifine?"
"Ehh mana ranki yadade..... Za dai muyi waya insha Allah"
"To babu matsala yallabai,muje in taka maka"
Har inda motocinsa ke ajiye ta rakashi aka bude masa yashiga sannan tajuya tawuce cikin gida,shikuma suka nufi gidan hajiya can dinma bai wani zauna ba dan ana kiran sallar ishah yafito bayan sun gabatar da salla suka juya abuja zai koma ya tarar da yar rigama Hanan,karo na farko da yayi tunanin abinda ya shafeta har yayi dariya shi daya,gaskiya yarinyar nan case ce,wai,wayarshi ya ciro ya soma kiran layin Aryan.
Ita kuwa Hanan bayan tafasa tafiya ta mayar da kayanta ciki sai da ta zauna ta sha kukanta sannan tayi shiru wannan dinma zuwan umma ne wacce ta tisata agaba tana ta faman bata hakuri tana cemata shi dama zaman aure gaba dayansa hakurine yafi yawa acikinsa kai bama iya zaman aure ba ita kanta rayuwar gaba dayanta hakuri ce dan haka ta dauki wannan abun da yafaru amatsayin ba komai ba kuma taci gaba da yiwa mijinta biyayya,
Tsamm tayi ta tsaida hankalinta da tunaninta wuri guda tana mai cigaba da jujjuya maganganun umma acikin ranta duk da cewa umman adunkule ta bata maganar bawai zama tayi tai mata ita dalla dalla ba amma akwai alamar tana bukatar tayi wa dukka maganganun duba na tsanaki domin umma cemata tayi taci gaba da kyautatawa mijinta saboda zuciya ahar kullum tana son mai kyautata mata sannan ta guji fushi da bacin ransa,to tayaya zata guji wadannan abubuwan? Dole tana bukatar daura damarar kulla abota da hakuri da gujewa duk wani abu da ka iya bata ransa sannan umma tace duk runtsi duk tsanani karta karaya daga fafutukar yakin neman cikar burinta taci gaba da fadawa Allah dukkan bukatunta haka kuma ta jajurce ta tsaya tsayin daka har sai hakarta ta cimma ruwa,
Murmushi tayi aranta tana tambayar kanta to kodai umma ta fahimce cewa tana son Khalil? Ko umma ta gano sirrin da taketa boyeshi acikin zuciyarta ita kadai wanda bata fatan wani mahaluki ya fahimta baya gashi wanda take yi dominsa? Cigaba tayi da aikinta acikin tamfatsetsen kitchen dinta mai dauke da komai da komai na bukata wurin girke girke,dama tasan bazai dawo da wuriba shiyasa itama bata tarki aikin da wuriba har sai da tabari la'asar tayi liss sannan tafara,tuwon semovita ta dora saboda Aryan yanata damunta da tambayar wai "mommy tuwo zaki dafa mana?" Wannan dalilinne yasata dora tuwon semovita miyar shuwaka, farfesun zabbi da kuma kunun shinkafa. A kitchen magriba tayi mata,agurguje ta karasa aikace aikacenta sannan ta kwashi na umma ta kai mata can ta isketa tana ta drama da mutumin nata Aryan ita dai da yake bata yi salla ba komawa sama tayi taje tayi wanka sannan tayi salla bayan ta idar ta koma k'asa dauke da tuwon da zata bawa Aryan,
Anan umma ke sanar da ita tafiyar anty maamy wadda sam ita Hanan bama tasan cewa ta tafi ba sai yanzu da umma ke bata labari,
"Allah yaraka taki gona......" Shine abinda Hanan ta fada acikin zuciyarta,afili kuwa sai kawai tayi murmushi tana sauraren umma,
Yau sun jima sosai da umma wacce keta yiwa Aryan tatsoniya har saida yayi bacci,daukarshi Hanan tayi a kafadarta ta nufi dakinsa dashi ta kaishi ta kwantar,daga can kuma part dinta ta wuce tana kallon agogon dake kan wayarta karfe 11 na dare harda wasu mintuna,shirin bacci tafara yi itama bayan tagama ta saka dogon hijab ta fita,kanta tsaye sashen oga ta nufa wanda dawowarsa kenan dan ko minti biyar baiyi ba da shigowa cikin gidan,wani abun mamaki kuma wai sai yanzu ne taji tana jin kunyar abunda yafaru da safe sai yanzu take jin kunyar rufe idanuwanta da tayi ta zazzaga masa rashin ta ido,
Tana shiga falon yana fitowa jikinsa sanye da rigar wanka fara, hannunshi rike da charger da alama wayar shi zai saka ajikin chaji, sunkuyar da kanta kasa tayi tana yimasa sannu da zuwa daga bisani ta mike tafita domin kawo masa abinci kamar kuwa tasan dama yunwa yake ji saboda rabonsa da abinci tun wanda yaci da safe. Yana zaune yayi nisa kadan aduniyar tunanin da ya tafi tabbas yana son maamy bawai so irin can mai zurfin nanba amma kuma wani lokacin sai yaji kamar yafasa auren nan domin shi yanzu gaba daya mace bata gabansa bawai dan baya bukatarta ba a'a saboda kawai ruhinsa da tunaninsa gaba daya kacokan suna ga Ramlat,iya gangar jikinsa ce kadai anan ita kanta wannan yarinyar Hanan kawai yana zaune da itane saboda Aryan,amma har gobe Ramlat ce abirnin zuciyarsa, shigowar Hanan bayan tayi masa magana shine yayi sanadiyyar dawowarshi daga tunanin da ya zurfafa acikinsa,
Cikin sanyin jiki da na murya yace ta zubo masa tuwon guda daya,zubo masa tayi sannan ta zuba masa kunu cikin cup da farfesun da tayi agefe takai masa gabansa,samun wuri tayi ta zauna duk da ta dan fara jin bacci sama sama domin 12 ta kusa,lura da gyangyadin da yaga tana yi yasashi fadin,
"Je ki kwanta sai da safe,nagode......"
Tashi tayi tana lullumshe ido ta fita,tana zuwa daki ta fada kan gado tana zare hijabin dake jikinta babu jimawa bacci ya dauketa,
Shi kuwa Khalil yana can yana sakawa da kwancewa yarasa meyasa aduk lokacin da maganar aure ta fara shiga tsakaninsa da wata mace sai yasamu kansa cikin mugun hali sai yaji gaba daya kunci da damuwa sun rufeshi koda yake yasan hakan bai rasa nasaba da tsananin kaunar da yake yiwa Ramlat,lumshe idanuwansa yayi yana mai barwa Allah zabi,idan har aurensa da yar uwarsa maamy alkhairi ne to Allah ya tabbatar idan kuma babu alkhairi Allah ya canja musu da mafi alkhairi.
3:30 AM
Kai ya jijjiga mata alamar tabbacin abinda yafada,daga haka ya saketa daga rikon da yayi mata yawuce yafita yana kokarin gyara necktie dinshi,
Tafi minti biyar tsaye wurin ta kasa koda kwakkwaran motsi har umma barira ta karaso tazo tana mai sake bata hakuri akan karta tafi tunda bada mijinta sukayi fada ba to babu amfanin tabar gidan wai da sunan yaji,
Juyawa tayi ta ja akwatinta ta nufi ciki dakyar ma take jan akwatin saboda kayan da ta loda ba kadan bane sai kace wacce idan ta tafi zatayi shekara agidan,har bedroom dinta umma ta rakata tana sake bata baki tana cemata kowa kagani agidansa hakuri yake yi amma akwai matsalar da take tare dashi,
Bayan fitar umma Data ta kunna awayarta ta hau online saboda tana son ta dan debewa kanta kewa amma acan kasan ranta ta kuduri aniyar itafa bazata cigaba da zama da anty maamy ba sai dai ayi wacce za ayi.
Har Khalil yaje office bai daina mamakin abinda Hanan tayi ba,to wai me zai kira wannan lamarin nata dashi? Kishi ko kuruciya? Gaba daya yarinya ta dage sai ta kori maamy daga gidan,yana shiga office kiran maamy yashigo masa, dauka yayi muryarshi asanyaye kamar kullum,
"Ibrahim ni nagama shirya kayana zan wuce gombe......"
Dan jimm yayi sannan yace,
"Ban gane zaki wuce gombe ba..."
"Ehh zan koma gidan ubana mana,inbanda matarka ta samu dama wai har ni zata yiwa gorin gida? Taje ta tambaya waye ubana,kai kanka kasan ubana yanada gidajen da bazasu lissafu ba,ni kaina inada gidaje sunfi goma mallakina amma wai ni ake yiwa gori akan gida nida gidan mijina akasar turai yake amma wai yau saboda nazo gidanka karamar yarinyar da bata fi sa'ar autar gidanmu ba take kokarin wulakanta ni..... Nagode"
Kitt ta katse wayar,rabuwa yayi da ita bai kara kiranta ba saboda yasan yanzu ranta abace yake ko daga kalaman da take yi yasan akule take maamy kuma badai zuciya ba,rabuwa yayi da ita har zuwa yamma lokacin da zai tashi daga office inyaso sai yabita can gomben ya wanke kansa.
Misalin karfe 6 yatashi daga office kuma direct hanyar gombe suka kama wanda basu suka isa ba sai bayan sallar magriba,salla yafara yi sannan ya karasa gidan Alhaji Idris kanwa mahaifin maamy,bai samu abban agida ba kasancewar baya gari, Jawad yatura yace yayi masa sallama da momyn su nan Jawad din ya ruga da gudu ya nufi can cikin gida,
Maamy tana gaban mirror tana tsala kwalliya tamkar wata budurwa dan ko da wasa bata daukar kanta a matsayin wata babba ta azo agani duk da tana da samarin yaya da budurwar 'ya,
"Mommy kizo inji uncle Khalil...."
"Yana ina?"
"Yana falon abba na kasa"
"Ina zuwa to"
Fita jawad yayi ita kuma ta tashi ta karasa shiryawa cikin doguwar riga ja tasha turare sannan ta dauki dan siririn mayafinta ta fita tana takunta mai cike da nutsuwa da daukar hankali,
Zaune ta sameshi ya dora kafarshi daya akan daya yana duba wayarshi,zama tayi gefenshi bayan tayi masa sallama,
"Haba amarya irin wannan fushi haka kuma? Sai kace dani akayi fadan....."
Wani kallo tayi masa kafin ta rausayar da kanta gefe,
"Ai wannan matar taka sai Kai..... Kasan wani abu? Wallahi bazan zauna gida daya da ita ba, tun wuri ma ni ka sama min gida amma banda wannan..... Ban son rashin kunya"
Murmushi Khalil yayi ya shafi sajensa,
"Kinji tsoro kenan?"
"Ba maganar tsoro anan fa Ibrahim gaskiya ce"
"To Allah dai yabaki hakuri,dan Allah ki dauki abinda yafaru yau amatsayin ba komai ba saboda kinga ita yarinya ce,yanzu ne ma take sanin yaya rayuwar take......"
"Nifa banda case da ita,kawai nidai bukatata awurinka shine karka hadamu gida daya dan bazamu zauna lafiya ba...."
"Baki da matsala a wannan bangaren Maryam,insha Allah zanyi yanda kike so......., Yanzu ina son zan karasa wurin hajiya mu gaisa sai inkoma Abuja,dan nan nafara zuwa"
"Ayya babu matsala,ka gaida min da ita"
"Zata ji insha Allah, shikenan intafi an sallameni?"
Murmushi tayi ta dan fara idanuwanta alamun shagwaba,
"Da ance maka kai mai laifine?"
"Ehh mana ranki yadade..... Za dai muyi waya insha Allah"
"To babu matsala yallabai,muje in taka maka"
Har inda motocinsa ke ajiye ta rakashi aka bude masa yashiga sannan tajuya tawuce cikin gida,shikuma suka nufi gidan hajiya can dinma bai wani zauna ba dan ana kiran sallar ishah yafito bayan sun gabatar da salla suka juya abuja zai koma ya tarar da yar rigama Hanan,karo na farko da yayi tunanin abinda ya shafeta har yayi dariya shi daya,gaskiya yarinyar nan case ce,wai,wayarshi ya ciro ya soma kiran layin Aryan.
Ita kuwa Hanan bayan tafasa tafiya ta mayar da kayanta ciki sai da ta zauna ta sha kukanta sannan tayi shiru wannan dinma zuwan umma ne wacce ta tisata agaba tana ta faman bata hakuri tana cemata shi dama zaman aure gaba dayansa hakurine yafi yawa acikinsa kai bama iya zaman aure ba ita kanta rayuwar gaba dayanta hakuri ce dan haka ta dauki wannan abun da yafaru amatsayin ba komai ba kuma taci gaba da yiwa mijinta biyayya,
Tsamm tayi ta tsaida hankalinta da tunaninta wuri guda tana mai cigaba da jujjuya maganganun umma acikin ranta duk da cewa umman adunkule ta bata maganar bawai zama tayi tai mata ita dalla dalla ba amma akwai alamar tana bukatar tayi wa dukka maganganun duba na tsanaki domin umma cemata tayi taci gaba da kyautatawa mijinta saboda zuciya ahar kullum tana son mai kyautata mata sannan ta guji fushi da bacin ransa,to tayaya zata guji wadannan abubuwan? Dole tana bukatar daura damarar kulla abota da hakuri da gujewa duk wani abu da ka iya bata ransa sannan umma tace duk runtsi duk tsanani karta karaya daga fafutukar yakin neman cikar burinta taci gaba da fadawa Allah dukkan bukatunta haka kuma ta jajurce ta tsaya tsayin daka har sai hakarta ta cimma ruwa,
Murmushi tayi aranta tana tambayar kanta to kodai umma ta fahimce cewa tana son Khalil? Ko umma ta gano sirrin da taketa boyeshi acikin zuciyarta ita kadai wanda bata fatan wani mahaluki ya fahimta baya gashi wanda take yi dominsa? Cigaba tayi da aikinta acikin tamfatsetsen kitchen dinta mai dauke da komai da komai na bukata wurin girke girke,dama tasan bazai dawo da wuriba shiyasa itama bata tarki aikin da wuriba har sai da tabari la'asar tayi liss sannan tafara,tuwon semovita ta dora saboda Aryan yanata damunta da tambayar wai "mommy tuwo zaki dafa mana?" Wannan dalilinne yasata dora tuwon semovita miyar shuwaka, farfesun zabbi da kuma kunun shinkafa. A kitchen magriba tayi mata,agurguje ta karasa aikace aikacenta sannan ta kwashi na umma ta kai mata can ta isketa tana ta drama da mutumin nata Aryan ita dai da yake bata yi salla ba komawa sama tayi taje tayi wanka sannan tayi salla bayan ta idar ta koma k'asa dauke da tuwon da zata bawa Aryan,
Anan umma ke sanar da ita tafiyar anty maamy wadda sam ita Hanan bama tasan cewa ta tafi ba sai yanzu da umma ke bata labari,
"Allah yaraka taki gona......" Shine abinda Hanan ta fada acikin zuciyarta,afili kuwa sai kawai tayi murmushi tana sauraren umma,
Yau sun jima sosai da umma wacce keta yiwa Aryan tatsoniya har saida yayi bacci,daukarshi Hanan tayi a kafadarta ta nufi dakinsa dashi ta kaishi ta kwantar,daga can kuma part dinta ta wuce tana kallon agogon dake kan wayarta karfe 11 na dare harda wasu mintuna,shirin bacci tafara yi itama bayan tagama ta saka dogon hijab ta fita,kanta tsaye sashen oga ta nufa wanda dawowarsa kenan dan ko minti biyar baiyi ba da shigowa cikin gidan,wani abun mamaki kuma wai sai yanzu ne taji tana jin kunyar abunda yafaru da safe sai yanzu take jin kunyar rufe idanuwanta da tayi ta zazzaga masa rashin ta ido,
Tana shiga falon yana fitowa jikinsa sanye da rigar wanka fara, hannunshi rike da charger da alama wayar shi zai saka ajikin chaji, sunkuyar da kanta kasa tayi tana yimasa sannu da zuwa daga bisani ta mike tafita domin kawo masa abinci kamar kuwa tasan dama yunwa yake ji saboda rabonsa da abinci tun wanda yaci da safe. Yana zaune yayi nisa kadan aduniyar tunanin da ya tafi tabbas yana son maamy bawai so irin can mai zurfin nanba amma kuma wani lokacin sai yaji kamar yafasa auren nan domin shi yanzu gaba daya mace bata gabansa bawai dan baya bukatarta ba a'a saboda kawai ruhinsa da tunaninsa gaba daya kacokan suna ga Ramlat,iya gangar jikinsa ce kadai anan ita kanta wannan yarinyar Hanan kawai yana zaune da itane saboda Aryan,amma har gobe Ramlat ce abirnin zuciyarsa, shigowar Hanan bayan tayi masa magana shine yayi sanadiyyar dawowarshi daga tunanin da ya zurfafa acikinsa,
Cikin sanyin jiki da na murya yace ta zubo masa tuwon guda daya,zubo masa tayi sannan ta zuba masa kunu cikin cup da farfesun da tayi agefe takai masa gabansa,samun wuri tayi ta zauna duk da ta dan fara jin bacci sama sama domin 12 ta kusa,lura da gyangyadin da yaga tana yi yasashi fadin,
"Je ki kwanta sai da safe,nagode......"
Tashi tayi tana lullumshe ido ta fita,tana zuwa daki ta fada kan gado tana zare hijabin dake jikinta babu jimawa bacci ya dauketa,
Shi kuwa Khalil yana can yana sakawa da kwancewa yarasa meyasa aduk lokacin da maganar aure ta fara shiga tsakaninsa da wata mace sai yasamu kansa cikin mugun hali sai yaji gaba daya kunci da damuwa sun rufeshi koda yake yasan hakan bai rasa nasaba da tsananin kaunar da yake yiwa Ramlat,lumshe idanuwansa yayi yana mai barwa Allah zabi,idan har aurensa da yar uwarsa maamy alkhairi ne to Allah ya tabbatar idan kuma babu alkhairi Allah ya canja musu da mafi alkhairi.
3:30 AM