← Book details Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 61

Sashe 15

Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai bayan da tayi salla sannan tashiga wanka tafito,make up kit dinta ta bude ta dan shafa lotion tasaka powder sai kwalli shikenan ta saka kayanta shadda brown colour da sarka da dan kunne ta dan fesa turare sama sama sannan ta bude kofa tafita domin wata lafiyayyar yunwa take ji duk hanjin cikinta sun sarke da juna,tamkar sakaliya yau haka ta zama sakamakon ganin haduwar da falonta yayi yasha purple colour din furnitures hatta wallpaper din dake bangon falon purple colour ne amma mai dan haske sannan ga wata tangamemiyar plasma ajiye wacce ke barazanar cinye bangon da take,agaskiya gidan yayi kyau ya hadu kuma ya tsaru sannan ankashe miliyoyin kudi wurin shiryashi, ita kanta cikin falon nata wurin bedrooms hudu ne aciki banda kitchen da store da dining area haka dayan part dinma dake opposite da nata,daga tsakiya kuma akwai wani dan corridor mai dauke da wasu hadaddun kujeru kai daga ganin wurin kasan anyi ne domin shakatawa dan ga flowers nan masu kamshi shuke agefe cikin tukwanen kasa wacce aka yiwa fenti da golden gashi yadda aka you roofing din wurin dabanbanci da sauran domin wannan anyishi ne da wani style mai ban sha'awa sosai ya burgeta dan daga nan inda kake ma kana iya hango cikin unguwar ta glasses din dake zagaye da wurin kana iya hango kyau da tsari irin na unguwar wacce ke dauke da manya manyan gidaje kerarru ga korayen ciyayi da shuke shuke da suka yiwa unguwar kawanya, gaba kadan kuma wata kyakkyawar kofa ce katuwa mai dauke da security code ajiki amma ita arufe take balle taga abinda ke ciki dan haka tajuya ta nufo kasa, babban falon dake kasa shima yana dauke da kitchen da store da dining room sannan ga guest room, atakaice dai gidan yakai part 4 waje waje ko ina kuma a tsare wani wurinma bata san dashi ba. Babu kowa cikin falon sai sanyi da kamshi dake ta faman tashi ta ko ina, kan dining ta duba abinci ne reras cikin warmers mai kyau kala kala wanda ita abinma har yaso bata tsoro to ina za akai wannan abincin sai kace wanda mutane goma zasu ci bayan bata ji motsin kowa ba? Lallai masu kudi suna shagalinsu a duniyar nan ta Allah,

Zama tayi ta debi dankali da kwai sai farfesun kayan cikin saniya dan su kadai zata iya ci,tana ci tana sake karewa falon kallo wanda yake kamar baza amutu ba dan tsabar haduwa tab irin wannan gidan idan mutum ba mai cikakken imani bane ai sai yamanta da mutuwa domin zai shagaltar dashi shi kansa dining area din abun kallo ne kujerunshi na karfe ne milk colour sai wani show glass mai fadi da girma glass da glass anzuba kwanukan cin abinci duk na tangaran plates, spoons, cups da sauran kayan amfani irinsu dinner set. Bayan tagama ci ta mike ta dauraye hannunta da bakinta awurin wanke hannu wanda aka tanada a dining area din dan hadda sabulun wanke hannu ajiye awurin nan ta matsa ruwa yafito ta wanke hannunta sannan ta leka cikin kitchen din wanda ke tafare da kayan amfani na wuta dan gaba daya electric ne kayan ciki gashi kuma babba dashi ba karami ba kayan ciki kuwa yaci ayiwa yanmata biyar aure dashi cikin wadata kuma,mayar da kofar tayi ta rufe takoma sama tana mai sake jinjina wannan gida acikin ranta,da ace wanda ta aura take so ko yaro ba tsoho ba ai zata fantama ta wataya to amma ina k'addara tariga fata.

Rasa abinda zatayi tai daga karshe tasaka wayarta a charge tabi lafiyar kujera ta hakimce tana sake bin falon nata da kallo to kenan ma har kayan dakin shi minister dinne yayi amma dai zata iya yuyuwa shima abbanta yayi mata,to aure ne babu shiri dududu ko wata daya fa ba ayiba da maganar akayi aure shiyasa komai babu shiri,

Dan sakin ranta tayi sakamakon kiranta da mutane keta faman yi awaya suna yimata Allah yasanya alkhairi wasu kuma suna yimata korafin kin sanar dasu bikin nata da batai ba ita dai bata cewa komai sai dai tayi shiru ko ance Allah yabada zaman lafiya bata cewa amin, su Khadija kuwa wadanda sukayi zaman camp tare sunce insha Allah zata gansu tunda dai tana Abuja.

Wuni guda ta kwashe tana shan baccinta salla kawai ke tada ita,bayan tayi sallar la'asar ta yi wanka ta sake shiryawa cikin atamfa exclusive irin na cikin lefenta,dinkin riga da zani ne pieces simple daurin dan kwali tayi sannan ta shafa turare,tun safe rabonta da abinci shiyasa ta nufi downstairs domin cin abinci ai kuwa gashi nan jere an ajiye wurin kala biyar,shinkafa fara da plantain sauce,sai amala da miyar yauki,ga gasasshen kifi wanda yaji vegetables washa washa ga jalop cous cous,sai farfesun kaza da wasu ganyayyaki wadanda bata gane Wadanne bane,

Shinkafar ta diba a plate tafara ci tana hadawa da gasasshen kifin,wato daga safe zuwa yanzu shine har aka kara zuba wasu abubuwan cikin show glass dinnan domin da safe iya dishes ne da ire irensu aciki amma yanzu harda kayan hada shayi irinsu madara, corn flakes, golden moon,da biskit kala kala wanda ake hadasu da tea asha,

Tana daf da gamawa taji karar kararrawa abakin kofar falon wato door bell,tana yunkurin tashi aka sake dannawa,mikewa tayi ta nufi bakin kofar dan ganin waye dukda babu hijabi ko mayafi ajikinta amma tasan kayan jikinta basu da matsala.................✍�

*_Ummi A'isha_*👌🏻
8/14/20, 10:07 AM - Ummi Tandama: *Book din mijin matacciya na kudine game bukatar siya sai atura 200 ta account din Aisha Ibrahim, 3112877210 first bank,sai atura shaidar biya ta WhatsApp number dina 07044644433 ko kuma atura recharge card da shaidar biya ta number din.*

*15*

***Cikin nutsuwa take takawa har ta isa bakin kofar daidai lokacin aka sake dannawa, budewa tayi ta dan ja baya,umma barira ce da nura PA yana dauke da Aryan a kafadarshi da alama ma Aryan dinne ke ta faman daddanna door bell din,

Kasancewar ita ba saninsu tayiba yasa ta dan saki fuska tana yimusu sannu da zuwa, Aryan kuwa sauka yayi daga hannun PA ya ruga jikinta ya rungume ta, bata da zabin da yawuce itama ta rungumeshi din amma bawai dan son ranta ba,

Kaya aka rinka shigowa dashi wanda yake mallakin su umma bariran da Aryan,sai lokacin ta fahimci ko suwaye domin dama taji Zaid yana waya yana fadar cewa zasu dawo gidan da zarar sun kammala shirya kayansu nan suka sake sabuwar gaisuwa da umma barira ta tsugunna har kasa ta gaida umman,

Suna zaune a falo PA nata shigarwa da umma kayanta cikin daya daga cikin bedroom din dake kasa bayan angama kaiwa Aryan nasa dake sama,

Sosai take ankare da yaron wato Aryan wanda yayi dare dare kan cinyar umma barira sai game din Angry run yake ta faman yi awata waya hadaddiya wacce bata da masaniyar ko ta waye,

"Umma kema akai miki kayanki upstairs....." Taji Aryan din yafada yana turo baki alamun shagwaba,

"A'a Aryan ni ina kasa yaushe zan hau sama intakura muku"

Jin abinda tace yayi wurgi da wayar yasoma rigima shi ala dole itama umma sai ta hau sama,wani irin haushin yaron Hanan keji gaba daya anbi anbata yaro an sangartashi dan kawai uwarshi ta mutu? Yaro sai tabarar tsiya duk anbarshi babu gwaba?

Dan karamin tsaki taja tana kallonsu umma nata kokarin rarrashinsa amma yana ta botsarewa,cigaba tayi da kallon dramar tasu amma fa yaron akwai masifar kyau ko tantama batayi tasan mahaifiyar shi ya iyo dan wallahi kamar dan larabawa yake ko turawa,

Dakyar umma ta rarrasheshi ya hakura ita dai Hanan haushi ne ya hanata magana domin dama haushinsa take ji tunda ta sanadiyyar shi ne ubansa yaje ya aurota har da su kafa mata dokoki akansa. Har lokacin sallar magriba yayi suna babban falon kasa zaune lokaci zuwa lokaci suna dan taba hira shikuma Aryan na kwance yayi pillow da cinyar umma yanata game dinshi,ganin lokacin salla na neman wucewa yasa umma barira fadin,

"To kai sulaimanu dagani inje daki inyi salla karka karasa min k'afar"

Mikewa umma tayi domin shiga daki shikuma Aryan yana cewa,

"Ni bazan bikiba mommy zanbi"

"Ehh kuje umma ta gaida Aysha" umma tafada tana wucewa daki,ita kam Hanan bata kulashi ba da taga zai biyota ma harara ta zabga masa jikinsa yana rawa yabi bayan umma yafasa binta,sama ta hau tana ta faman mita,

"Haka kawai kunbi duk kun bata yaro kamar shi kadaine maraya mtswwww nidai wallahi bazanyi tolerating wannan nonsense dinba"

Bedroom dinta ta shiga tayi alwala tafito aranta tana cewa idan uban naka yaji haushi ya sallame ni inbar muku gidanku sai yaci gaba da lallaba ka yana tattalinka. Aryan kuwa da kuka yashiga dakin umma wacce ke kan rug din salla tana yi,shi tunda yafado duniya bai san wani abu waishi takura ko kiyayya ba,kowa cikin nuna masa so yake da kauna ko harara bai santa ba sai yau da yaga Hanan tayi masa shiyasa tun daga lokacin yafara jin tsoronta,saida umma ta idar da salla sannan tasoma rarrashinsa daga karshe taci nasara bayan tace masa suje tabashi tuwo yaci dama akwai shi da son tuwo yana mutukar kaunar tuwo yaron yafi sonshi fiyeda komai adangin cima,

Saida umma ta sake masa kayan jikinsa daga jeans da t shirt zuwa riga armless da gajeren wando sannan suka fita,akasa suka zauna bayan umma ta zubo tuwon nan tafara bashi abaki yana ci tana hada masa da ruwa amma shi hankalinsa gaba daya yana kan wayar dake hannunshi,ahaka Hanan ta sauko ta samesu tana sanye da babban hijabi hannunta rike da casbaha tana ja ahankali,zama tayi akan kujera tana kallonsu kamar tasamu tv domin sai umma ta dan rarrashesa sannan yake yarda yana karbar tuwon,

Kamar a mafarki kuma sai taga yana murna yana dariya yana fadin,

"Papa..... Daddy"

"Yes son how you? Me kaka cine haka?" Khalil yafada wanda ke kwance kan gado yana kallon Aryan da umma agefenshi ta video call din da yakira,

"Daddy tuwo umma take bani.... Kuma da dad'i"

Dariya Khalil yayi yana kallon fuskar Aryan Sosai,

"Boy meyasa kayi kuka? Waye ya taba min kai?"
Chapter 15 · 0% Book details