Sashe 46
Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
***Tafi mintuna goma zaune batare da tasan ta ina yadace tafara ba ganin wankin hula na shirin kaita tsakar dare yasata mikewa daga zaunen da take ta cire hijabin jikinta tafita tamkar kazar da kwai ya fashewa aciki, kitchen dinta da ke makare da kaya wanda musamman aka tanada dominta a matsayinta na matar gida tayiwa tsinke, to yanzu ita me zata dafa tunda takamaimai bata da masaniyar me yafi so yaci da safe? Amma dai wallahi hajja hasinah ta hadata da assignment me zafi,
Tana nan tsaye harabar kitchen din tana tunanin me yadace dabara ta fado mata,gwara kawai tayi abincin kala biyu daya na gargajiya daya kuma na zamani inyaso duk wanda taga yaci to shi yafi so,
Hakan kuwa tayi nan ta zage ta soma girkinta cikin jin dadi da farin ciki domin girki yana daya daga cikin abubuwan da ke sakata nishadi a lokacin da take gabatar dashi,wainar semovita tayi za aci da suga kuma abarta tayi kyau kamar ta shinkafa tayi laushi libis sai kunun gyada da ta dama haka kuma ta soya dankali da sos wadda taji kwai nasha nasha,
Agaugauce ta je ta shirya Aryan bayan tagama aikin danma dai ba wani mai yawa tayiba shiyasa bai dauki dogon lokaci ba,tana gama shirya Aryan ta kamo hannunshi suka sauko kasa wanda tuni kuku yajima da shirya table, breakfast ta bashi yaci sannan ta shirya masa lunch box dinsa yatafi,yana tafiya takoma sama ta shiga wanka shima bata zauna tajima acikiba tayi tafito aranta tana jinjina kokarin iyaye mata musamman wadanda suka tara 'yaya ko kuma haihuwar tayi musu sammako,ka kula da yara sannan ka kula da ubansu kai gaskiya isn't easy,shiryawa tayi batare da bata lokaci ba cikin orange colour din atamfa mai bala'in kyau,dinkin fitted ne shiyasa yayi mata tsantsam ajikinta,bata yi wani dogon lissafi ba wurin kalmasa dan kwalinta ba kawai dan cokara shi tayi tafita kuma hakan sai yabada style mai kyau,
Yau kam ta shirya baiwa Khalil surprise dan duk abubuwan da ta dafa kwasarsu tayi ta kai sashensa ta jejjera bisa table din cin abinci sannan ta nemi wuri ta zauna nan cikin falon, agogon hannunta ta kalla bayan ta zauna karfe 8 saura mintuna biyar,kai amma gaskiya tayi kokari kuma aikin nata ma yayi sauri sosai,yau kam sai dai anty maamy tazo ta isketa duk sammakonta ehe.
Bata jima zaune afalon ba taji alamun bude kofa, kamshinsa ne yafara sanar da ita fitowarshi kafin shi din ya bayyana,sanye yake cikin farin yadi na maza dandakeke mai mutukar kyau mai laushi shara shara, yana tafe yana kokarin balle hannun rigarshi,mamaki yaji ya kamashi kwarai da gaske sakamakon ganinta da yayi zaune cikin falon,mikewa tsaye tayi daga zaunen da take alamar girmamawa,
Da idonsa yake neman karin bayanin ganinta da yayi a daidai wannan lokaci,kasa tayi da kanta ta dan duka ta gaisheshi,
"Ina kwana?"
"Lafiya lau..."
Ya amsa mata idanuwanshi na kaiwa kan dining, warmers yagani jere akai da sauran kayan karin kumallo,agogon hannunshi ya kalla sannan ya dan yi guntun tsakin da bata san dalilinsa ba,
"Waye ya kawo wancan abincin?" Ya bukata batare da ya kalleta ba domin hankalinsa na kan wayar dake hannunsa,
"Nice....." Ta bashi amsa cike da kwarin gwiwa domin ta dauri aniyar canja komai a tsakaninsu,
Bai kara magana ba ya nufi saman kujera ya zauna yana ta danne dannen waya da alama wani yake nema amma wayar taki shiga dan sai dan guntun tsaki yake ta ja yana kara wayar a kunnensa,zuwa caan taji yafara magana fada fada,
"Wai ina kaje ne inata kiran wayarka tun asubah amma taki shiga?........ Kana jina...... Ya isa...... Yanzu yanzun nan katashi kaje store ka dauki abinci ka kai gidan yaran nan........ Abincinsu yakare tun jiya....... Kawai ka wani kashe waya tun 11 ana ta nemanka wayarka akashe........ Ka tashi yanzu kaje karka bata min lokaci...."
Daga haka ya cire wayar daga kunnenshi yana jin kamar an dauke masa wani nauyi dake kansa, haba har ya dan ji sanyi amma ace anbar yara marayu babu abinci ai akwai matsala,ita dai hanan ba gane kan zancen nashi tayi ba saboda bata san da wanda yake wayar ba kuma bata san akan wanene ba,
Ta glass ta hango anty maamy na tahowa hannunta rike da karamin flask din coffee zata kawowa Khalil mikewa tsamm Hanan tayi ta koma kusa dashi aranta tana cewa ai kuwa yau sai dai ayi wacce za ayi amma Khalil bazai sha wannan coffee dinba breakfast din da ta kawo masa zai ci,
"Ga breakfast din can kar ya huce......." Ta fada cikin marereta, baice komai ba kuma bai tashi ba yaci gaba da danne dannen wayarshi, falon shiru baka jin sautin komai sai kukan dawisu dake tashi daga bayan dakin baccinsa,ahaka anty maamy tashigo nan Hanan ta dan sake matsawa dab dashi wanda har sai da hakan yaso batawa anty maamy rai,
Fuskarta babu yabo babu fallasa ta karasa cikin falon tana dan basarwa,sanye take da doguwar riga ta material multi colour rigar mai burmemen hannu ta yafa siririn bakin mayafi akanta, karasawa tayi ta zauna kujerar gefensu,
"Ibrahim har kafito kenan....."
Daga ido yayi ya kalleta,
"Maamy..... Kin tashi lafiya.... Wallahi nafito..... Zanje kwara state ne"
"Allah ya kiyaye hanya...."
Ajiye masa flask din tayi agabansa,
"Ga coffee din..."
"Ok thank you.... Sai dai ma nafita dashi office nasha acan"
Hanan na jinsu batace ko uffan ba kuma da yake yau yan rashin kirkin na kusa ko gaida anty maamy bata yiba sai wani daddauke kai take yi ita ala dole ankula mijinta,
"Me da me aka kawo kan table din can?" Taji Khalil yana tambayar ta,wata irin mikewa tayi babu zato yaji ta kamo hannunsa mai tsananin taushi,
"Uncle kazo ka gani mana....... Kai fa na dafawa"
Ba Khalil ba ita kanta anty maamy saida taji mamakin wannan lamari,jingina tayi jikin kujera yanda zata cigaba da kallon scene din da kyau,
Duk da baya wani sakar mata fuska mikewa yayi yabi bayanta zuwa kan dining din wanda har lokacin tana rike da hannunshi,wani irin shock take ji kamar anjona mata electric amma ta kasa sakinsa har sai da ya zauna saman table din,
Tea yace ta hada masa rabin cup amma ganin kunun gyadar da tayi sai yace tabar tea din ta zuba masa kunun,da kunun da waina ta saka masa yaci sai wani kwarkwasa take yi wanda hakan ke baiwa anty maamy dariya, lallai yaro yaro ne,yaran yanzu akwai rawar kai da feleke ita ala dole mai miji sai wani karairaya take yi mijin da ba ma lallai ta burgeshi ba,mikewa tsaye anty maamy tayi domin ta gaji da kallon dramar tasu,
"Ibrahim bari naje na kwanta.... Zamuyi waya anjima"
"Ok mammy thank you"
Fita tayi Hanan tabita da harara aranta tana cewa ai wayar ma insha Allah baza ayita ba,shi kam har ga Allah yaji dadin waina da kunun da yasha haba amma ace kullum tea tea babu wani canji,mikewa yayi yawuce cikin bedroom dinshi tana ganin haka tayi wuff ta mike taje ta dauki flask din coffee din da anty maamy ta kawo taje ta tuttuleshi cikin sink din dake dinning area din,
Fitowa yayi tsaf cikin shirinsa na fita sai zuba kamshi yake yi,tsaye take hannuwanta abaya tana wasa dasu,
"Amm........ Am nace...... Maganar mai gyaran targaden da kace....."
Shiru ya dan yi na dan wani lokaci kafin ya daga ido ya kalli side din da take,
"Za aturo shi...."
"Nagode..... Adawo lafiya, Allah ya kiyaye hanya...."
"Amin,nagode" Ya fada a takaice sannan yawuce zai fita har yaje bakin kofa yajiyo,
"Yawwa bani wannan flask din wanda maamy ta kawo min coffee"
Dauka tayi ta nufeshi ta mika masa batare da ta nuna wata alama ba wacce zai sa ya zargi tana da masaniya akai,hannu yasa ya karba sai kuma yaji empty,dan jijjigawa yayi yana son ya tabbatar da abinda yaji nan kuwa yaji wayam babu komai,
"Ya najishi empty??" Ya fada ahankali amma kasancewar akusa take dashi taji abinda yace,
"To ko dai dama bata saka maka komai ciki ba?" Ita kanta ta san wannan tambayar da tayi masa ta rainin hankali ce, baice mata komai ba ya mika mata flask din yawuce yafita tana biye dashi abaya kamar wata bodyguard,sai da ta rakashi har kasa suka gaisa da umma barira sannan yafita,sai lokacin tajuya ta koma sama saboda dama bata son ya hadu da anty maamy ne a kasa shiyasa ta zame masa jela,
Falonshi ta gyara masa ta tsaftace shi tas amma bata yi garajen shigar masa cikin bedroom ba,sai dai amma abinda yakama tun daga kan falonshi zuwa bathroom din dake cikin falon da sauran lungu da sako dake harabar sashen nasa duk ta samu nasarar kalkalesu tsaf,
Bayan ta gama gyara nata sashen kasa ta sauka wurin umma wacce ke kishingide a d'akinta,anty maamy kuma na falo tana rike da novel na turanci tana karantawa, tsaki Hanan tayi aranta tace to ko me anty maamy din take jira da taki tafiya ta share daki ta zauna? Shifa Zaid kwata kwata ma kwananshi biyu ya tafi amma ita anty maamy taki tafiya koda yake ai gidan dan uwanta ne ta sake fadin hakan acikin ranta,dakin umma ta shiga bayan ta shigar musu da sauran kayan breakfast din da Khalil yarage,
Zama tayi suka fara cin wainar da ta yiwa Khalil itada umma,umma na sake kara mata haske akan irin kalolin girke girken da Khalil yafi so wanda shi yafi son abincin gargajiya dan bai ki ya yi breakfast da dumamen tuwo ba ko koko da kosai watikil wannan ne dalilin da yasa bai cika cin abinci ba yake zama da yunwa saboda su ma'aikatan gidan sunfi maida hankali wurin girke girken zamani,murna tayi sosai saboda jin wannan daddadan labari daga bakin umma.
Bayan mai gyaran targade yazo yayi mata sama ta koma ta shiga dakinta ta samu dan karamin littafinta da biro ta soma tsara jaddawalin girke girken da zata rinka yi asati duk na gargajiya amma zata dan rinka hadawa da na zamani shima ba wani mai yawa ba,bayan tagama kwanciyar ta tayi ta huta har azahar tana kwance,bayan ta idar da salla sai maganar anty maamy ta fado mata wacce tayiwa Khalil da safe wai sai sunyi waya,
Tana nan tsaye harabar kitchen din tana tunanin me yadace dabara ta fado mata,gwara kawai tayi abincin kala biyu daya na gargajiya daya kuma na zamani inyaso duk wanda taga yaci to shi yafi so,
Hakan kuwa tayi nan ta zage ta soma girkinta cikin jin dadi da farin ciki domin girki yana daya daga cikin abubuwan da ke sakata nishadi a lokacin da take gabatar dashi,wainar semovita tayi za aci da suga kuma abarta tayi kyau kamar ta shinkafa tayi laushi libis sai kunun gyada da ta dama haka kuma ta soya dankali da sos wadda taji kwai nasha nasha,
Agaugauce ta je ta shirya Aryan bayan tagama aikin danma dai ba wani mai yawa tayiba shiyasa bai dauki dogon lokaci ba,tana gama shirya Aryan ta kamo hannunshi suka sauko kasa wanda tuni kuku yajima da shirya table, breakfast ta bashi yaci sannan ta shirya masa lunch box dinsa yatafi,yana tafiya takoma sama ta shiga wanka shima bata zauna tajima acikiba tayi tafito aranta tana jinjina kokarin iyaye mata musamman wadanda suka tara 'yaya ko kuma haihuwar tayi musu sammako,ka kula da yara sannan ka kula da ubansu kai gaskiya isn't easy,shiryawa tayi batare da bata lokaci ba cikin orange colour din atamfa mai bala'in kyau,dinkin fitted ne shiyasa yayi mata tsantsam ajikinta,bata yi wani dogon lissafi ba wurin kalmasa dan kwalinta ba kawai dan cokara shi tayi tafita kuma hakan sai yabada style mai kyau,
Yau kam ta shirya baiwa Khalil surprise dan duk abubuwan da ta dafa kwasarsu tayi ta kai sashensa ta jejjera bisa table din cin abinci sannan ta nemi wuri ta zauna nan cikin falon, agogon hannunta ta kalla bayan ta zauna karfe 8 saura mintuna biyar,kai amma gaskiya tayi kokari kuma aikin nata ma yayi sauri sosai,yau kam sai dai anty maamy tazo ta isketa duk sammakonta ehe.
Bata jima zaune afalon ba taji alamun bude kofa, kamshinsa ne yafara sanar da ita fitowarshi kafin shi din ya bayyana,sanye yake cikin farin yadi na maza dandakeke mai mutukar kyau mai laushi shara shara, yana tafe yana kokarin balle hannun rigarshi,mamaki yaji ya kamashi kwarai da gaske sakamakon ganinta da yayi zaune cikin falon,mikewa tsaye tayi daga zaunen da take alamar girmamawa,
Da idonsa yake neman karin bayanin ganinta da yayi a daidai wannan lokaci,kasa tayi da kanta ta dan duka ta gaisheshi,
"Ina kwana?"
"Lafiya lau..."
Ya amsa mata idanuwanshi na kaiwa kan dining, warmers yagani jere akai da sauran kayan karin kumallo,agogon hannunshi ya kalla sannan ya dan yi guntun tsakin da bata san dalilinsa ba,
"Waye ya kawo wancan abincin?" Ya bukata batare da ya kalleta ba domin hankalinsa na kan wayar dake hannunsa,
"Nice....." Ta bashi amsa cike da kwarin gwiwa domin ta dauri aniyar canja komai a tsakaninsu,
Bai kara magana ba ya nufi saman kujera ya zauna yana ta danne dannen waya da alama wani yake nema amma wayar taki shiga dan sai dan guntun tsaki yake ta ja yana kara wayar a kunnensa,zuwa caan taji yafara magana fada fada,
"Wai ina kaje ne inata kiran wayarka tun asubah amma taki shiga?........ Kana jina...... Ya isa...... Yanzu yanzun nan katashi kaje store ka dauki abinci ka kai gidan yaran nan........ Abincinsu yakare tun jiya....... Kawai ka wani kashe waya tun 11 ana ta nemanka wayarka akashe........ Ka tashi yanzu kaje karka bata min lokaci...."
Daga haka ya cire wayar daga kunnenshi yana jin kamar an dauke masa wani nauyi dake kansa, haba har ya dan ji sanyi amma ace anbar yara marayu babu abinci ai akwai matsala,ita dai hanan ba gane kan zancen nashi tayi ba saboda bata san da wanda yake wayar ba kuma bata san akan wanene ba,
Ta glass ta hango anty maamy na tahowa hannunta rike da karamin flask din coffee zata kawowa Khalil mikewa tsamm Hanan tayi ta koma kusa dashi aranta tana cewa ai kuwa yau sai dai ayi wacce za ayi amma Khalil bazai sha wannan coffee dinba breakfast din da ta kawo masa zai ci,
"Ga breakfast din can kar ya huce......." Ta fada cikin marereta, baice komai ba kuma bai tashi ba yaci gaba da danne dannen wayarshi, falon shiru baka jin sautin komai sai kukan dawisu dake tashi daga bayan dakin baccinsa,ahaka anty maamy tashigo nan Hanan ta dan sake matsawa dab dashi wanda har sai da hakan yaso batawa anty maamy rai,
Fuskarta babu yabo babu fallasa ta karasa cikin falon tana dan basarwa,sanye take da doguwar riga ta material multi colour rigar mai burmemen hannu ta yafa siririn bakin mayafi akanta, karasawa tayi ta zauna kujerar gefensu,
"Ibrahim har kafito kenan....."
Daga ido yayi ya kalleta,
"Maamy..... Kin tashi lafiya.... Wallahi nafito..... Zanje kwara state ne"
"Allah ya kiyaye hanya...."
Ajiye masa flask din tayi agabansa,
"Ga coffee din..."
"Ok thank you.... Sai dai ma nafita dashi office nasha acan"
Hanan na jinsu batace ko uffan ba kuma da yake yau yan rashin kirkin na kusa ko gaida anty maamy bata yiba sai wani daddauke kai take yi ita ala dole ankula mijinta,
"Me da me aka kawo kan table din can?" Taji Khalil yana tambayar ta,wata irin mikewa tayi babu zato yaji ta kamo hannunsa mai tsananin taushi,
"Uncle kazo ka gani mana....... Kai fa na dafawa"
Ba Khalil ba ita kanta anty maamy saida taji mamakin wannan lamari,jingina tayi jikin kujera yanda zata cigaba da kallon scene din da kyau,
Duk da baya wani sakar mata fuska mikewa yayi yabi bayanta zuwa kan dining din wanda har lokacin tana rike da hannunshi,wani irin shock take ji kamar anjona mata electric amma ta kasa sakinsa har sai da ya zauna saman table din,
Tea yace ta hada masa rabin cup amma ganin kunun gyadar da tayi sai yace tabar tea din ta zuba masa kunun,da kunun da waina ta saka masa yaci sai wani kwarkwasa take yi wanda hakan ke baiwa anty maamy dariya, lallai yaro yaro ne,yaran yanzu akwai rawar kai da feleke ita ala dole mai miji sai wani karairaya take yi mijin da ba ma lallai ta burgeshi ba,mikewa tsaye anty maamy tayi domin ta gaji da kallon dramar tasu,
"Ibrahim bari naje na kwanta.... Zamuyi waya anjima"
"Ok mammy thank you"
Fita tayi Hanan tabita da harara aranta tana cewa ai wayar ma insha Allah baza ayita ba,shi kam har ga Allah yaji dadin waina da kunun da yasha haba amma ace kullum tea tea babu wani canji,mikewa yayi yawuce cikin bedroom dinshi tana ganin haka tayi wuff ta mike taje ta dauki flask din coffee din da anty maamy ta kawo taje ta tuttuleshi cikin sink din dake dinning area din,
Fitowa yayi tsaf cikin shirinsa na fita sai zuba kamshi yake yi,tsaye take hannuwanta abaya tana wasa dasu,
"Amm........ Am nace...... Maganar mai gyaran targaden da kace....."
Shiru ya dan yi na dan wani lokaci kafin ya daga ido ya kalli side din da take,
"Za aturo shi...."
"Nagode..... Adawo lafiya, Allah ya kiyaye hanya...."
"Amin,nagode" Ya fada a takaice sannan yawuce zai fita har yaje bakin kofa yajiyo,
"Yawwa bani wannan flask din wanda maamy ta kawo min coffee"
Dauka tayi ta nufeshi ta mika masa batare da ta nuna wata alama ba wacce zai sa ya zargi tana da masaniya akai,hannu yasa ya karba sai kuma yaji empty,dan jijjigawa yayi yana son ya tabbatar da abinda yaji nan kuwa yaji wayam babu komai,
"Ya najishi empty??" Ya fada ahankali amma kasancewar akusa take dashi taji abinda yace,
"To ko dai dama bata saka maka komai ciki ba?" Ita kanta ta san wannan tambayar da tayi masa ta rainin hankali ce, baice mata komai ba ya mika mata flask din yawuce yafita tana biye dashi abaya kamar wata bodyguard,sai da ta rakashi har kasa suka gaisa da umma barira sannan yafita,sai lokacin tajuya ta koma sama saboda dama bata son ya hadu da anty maamy ne a kasa shiyasa ta zame masa jela,
Falonshi ta gyara masa ta tsaftace shi tas amma bata yi garajen shigar masa cikin bedroom ba,sai dai amma abinda yakama tun daga kan falonshi zuwa bathroom din dake cikin falon da sauran lungu da sako dake harabar sashen nasa duk ta samu nasarar kalkalesu tsaf,
Bayan ta gama gyara nata sashen kasa ta sauka wurin umma wacce ke kishingide a d'akinta,anty maamy kuma na falo tana rike da novel na turanci tana karantawa, tsaki Hanan tayi aranta tace to ko me anty maamy din take jira da taki tafiya ta share daki ta zauna? Shifa Zaid kwata kwata ma kwananshi biyu ya tafi amma ita anty maamy taki tafiya koda yake ai gidan dan uwanta ne ta sake fadin hakan acikin ranta,dakin umma ta shiga bayan ta shigar musu da sauran kayan breakfast din da Khalil yarage,
Zama tayi suka fara cin wainar da ta yiwa Khalil itada umma,umma na sake kara mata haske akan irin kalolin girke girken da Khalil yafi so wanda shi yafi son abincin gargajiya dan bai ki ya yi breakfast da dumamen tuwo ba ko koko da kosai watikil wannan ne dalilin da yasa bai cika cin abinci ba yake zama da yunwa saboda su ma'aikatan gidan sunfi maida hankali wurin girke girken zamani,murna tayi sosai saboda jin wannan daddadan labari daga bakin umma.
Bayan mai gyaran targade yazo yayi mata sama ta koma ta shiga dakinta ta samu dan karamin littafinta da biro ta soma tsara jaddawalin girke girken da zata rinka yi asati duk na gargajiya amma zata dan rinka hadawa da na zamani shima ba wani mai yawa ba,bayan tagama kwanciyar ta tayi ta huta har azahar tana kwance,bayan ta idar da salla sai maganar anty maamy ta fado mata wacce tayiwa Khalil da safe wai sai sunyi waya,