Sashe 24
Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
***Khalil na kwance kan gadonshi adakin hotel din da yasauka yana kallon pics din birthday din Aryan duk da baya nan aka gabatar da party din amma zaid yayi kokari kamar yana nan saboda yanda aka shirya abin cikin kyau da tsari bugu da kari kuma gashi yaga fuskar Aryan cikin farin ciki sosai hakan kadai da yagani yaji inama shima yana wurin ko kuma inama zai iya yin fuffuke yatashi da yaje anyi dashi,har yagama kallon pics din baiga Hanan ba koda yake ai ba saninta yayiba kuma ta yuyuma babu ita awurin.
Hanan kam har washe gari ma bata samu fitaba dan har lokacin bata jin dadin jikinta tadai shirya Aryan ta hada masa komai yatafi school,kuma har yaje yadawo tana kwance a bedroom dinta tana kallon hotunanshi dake cikin wayarshi wadanda sunfi dari,kuma duka nashi ne shi kadai bata ga na babanshi ba duk shi kadai ne akasashe daban daban gaskiya yaron nan ya zagaya duniya domin tun baifi shekara biyu ba ta ga uban yafiffitar dashi manya manyan k'asashen labarawa da na turawa dan wasu hotunan ga larabawa nan wani kuma turawa zaka gani gasu nan dai burjik wani kuma a saudiyya ne dan ga ka'aba nan da sauran kyawawan wurare dake cikin birnin k'asar,ta shagala sosai da kallon hotunan shiyasa har Aryan yadawo bata saniba tana ta kallon hotunanshi shida wasu yara kyawawa suma guda biyu kamarshi mace da namiji taji shigowar Aryan yana zuwa ya haye kanta kamar yadda yasaba, rikeshi tayi tana murmushi,
"Welcome back my Cutie..."
Kankameta yayi suna dariya pic dinshi da yaran nan ta nuna masa tana tambayarshi suwaye wadannan sai yace mata wai nawwar ne da Naina yaran Abba Khalid wai yan uwanshi ne, lallabawa tayi ta tashi taje tayi masa wanka bayan ta cire masa uniform dinshi tabashi abinci yaci sannan yafita islamiyya wurin malaminsa.
Bayan birthday din Aryan da kwana biyu Zaid yakoma gombe yanzu gida yarage sai iya Hanan da Aryan da umma barira,duk wani abu da yashafi Aryan yanzu Hanan ce keyi masa itama shagwabashi yanzu takeyi sosai wanda har Khalil yasan da haka dan komai sai Aryan yace masa wai mommyn shi ce tayi masa idan abinci ne sai yace itace tabashi shi kansa yasan tana kulawa da yaron Sosai ba kadan ba.
***
Har yanzu sumayya bata samu ta shawo kan mujahid ba domin kullum cikin wulakantata yake yauma hakance tafaru tana daki tana ta sharbar kuka mami ta shigo ta zauna gefenta,cikin lallashi tace,
"Sumayya daina kuka kinji,yi hakuri,ki daina sakawa kanki damuwa akan mujahid kedai kawai kici gaba da addu'a idan har mijinki ne babu makawa sai ya aureki....kiyi shiru kinji"
Kai ta daga alamun to,haka mami taci gaba da rarrashinta daga karshe ta tashi tafita,tana fita ta dauki wayarta ta kira k'awarta muhibba ta zayyane mata dukkan abunda yake faruwa sannan cikin kuka ta karasa maganar tata da fadin,
"Muhibba da me Hanan tafini da yake wulakanta ni akanta bayan ma tayi aurenta ita ta manta dashi amma shi kullum cikin kallon hotonta yake...."
"Babu da abinda tafiki sumy,ki kwantar da hankalinki kiji abinda zan fada miki....."
"Ina jinki muhibba"
"Yawwa kema ki shareshi ki fita harkarsa kuma ki daina kulashi,ki nuna masa idan dashi ko babu shi zaki iya rayuwa,ki shareshi fa sosai dan shima yana sonki bawai ke kadai ke haukan sonshi ba saboda duk wanda kake so wallahi shima yana sonka sai dai ko wani dalili ya hanashi bayyanawa amma dan so shima yana sonki,ki danne zuciyarki ki shareshi shi da kansa zai sauko"
Shawarwari sosai muhibba tabata kan yanda zata share ya mujahid har sai yakawo kansa da kanshi,ita dai sumayya ji take yi kamar bazata iya ba saboda irin yanda a kullum wutar son mujahid ke ruruwa a cikin zuciyarta gashi shi kuma yayita disgata agaban kowaye babu ruwansa dazu fa agaban yan aikin gidan yayi mata rashin mutunci dan kawai tashiga dakinsa abinda yasata kuka kenan amma insha Allah zata danne zuciyarta tabata hakuri ta gwada aiki da shawarar muhibba.
***
Bayan birthday din Aryan da sati daya Khalil yadawo nan yakawowa Aryan tsaraba mai tarin yawa ta takalma da jeans da t shirts masu tsada,
Kullum baya shiga gidan sai cikin dare misalin karfe 1 ko 2 wani lokacinma har 3 dan sai kowa yayi bacci agidan,bai jima da dawowa ba yasake komawa k'asar Italy amma kullum suna makale awaya shida Aryan wanda ada yamakale masa wai sai yabishi dakyar ya shawo kansa ta hanyar cemasa ankusa yin hutun makaranta ana yin hutu zai fita dashi duk k'asar da yake so.
Khalil baifi sati daya da tafiya ba Aryan yawayi gari da wani zazzabi mai zafi ga tari da ciwon kirji babu shiri aka kira Dr Al'amin yana zuwa da yadubashi yace su tafi asibiti dan dole sai ya kwantar dashi,
Asibitin suka tafi dukkaninsu cike da damuwa da tashin hankali ita kam umma ma kashe wayarta tayi dan kar Khalil yakirata haka ta Aryan dinma arufe take,kwantar dashi Dr Al'amin yayi yafara bashi taimakon gaggawa,
Aranar da yamma sai ga Zaid yazo kamar yanada masaniyar abinda ke faruwa,can asibitin yabisu dan ajikinsa ma aka debi jinin da aka karawa Aryan din,
Khalil shi bai san abinda yake faruwa ba amma haka kawai yaji jikinsa duk babu dadi kamar irin baida lafiya dinnan alhalin kuma shi lafiyar sa kalau amma dai jikinsa yayi masa wani irin sanyi kalau haka dai ya daure yaci gaba da al'amuransa wadanda suka kaishi,
Yana ta kiran Aryan awaya kuma baya samunshi haka itama wayar umma bata shiga daga karshe sai Zaid ya nema dan jin meke faruwa amma sai Zaid ya ce masa wai babu komai da ya tambayi Aryan sai yace bacci yake yi,cewa yayi to ya gaidashi shida umma sukayi sallama,
Duk dangi kuwa babu wanda bai san rashin lafiyar Aryan ba Khalil kadai aka boyewa saboda ba ason afada masa saboda kar hawan jininsa ya motsa,tun a washe garin ranar da aka kai Aryan asibiti hajiya tazo Abuja suna tare a asibitin suna kula dashi,
Zaid kuwa sai hanya hanya yake yiwa Khalil idan ya kirashi yace ya hadashi da Aryan sai yace yana toilet ko yace yana bacci ko kuma yace wai yana makaranta,da Khalil ya tambayeshi to me yasamu wayar Aryan din da yasa baya samu idan yakira sai yace wai ai swimming pool tafada a hannun Aryan shiyasa ta daina yi nan Khalil yace masa to idan yadawo ya daukeshi suje wurin siyar da wayoyi ya siyo mishi duk wacce yakeso komai tsadarta da toh Zaid ya amsa masa sukayi sallama suna yin sallama yakashe shima tashi wayar gaba daya.
Yau kam tashin hankalinsu yafi na kullum domin tunda garin Allah yawaye Aryan yake ta faman suma daga safe zuwa yamma ya suma yafi sau biyar,shi kansa Dr Al'amin yagama shiga tashin hankali saboda yanda jikin Aryan yarikice Sosai,
Hanan shawara tayi da zuciyarta bata sanarwa da kowaba aranta tace gara ta fadawa Khalil abinda ke faruwa tunda boyewar bata da amfani da afada masa mutuwar dansa gara afada masa rashin lafiyarsa yazo ya ganshi kar aje yamutu,
Text massage ta tura masa tana turawa ta kashe wayarta itama, Khalil na kwance yakasa bacci dan a yan kwanakin nan sam baya iya bacci gashi dai lafiyarshi kalau amma kamar baida lafiya yake jinsa,jin shigowar sako yasashi kallon agogo,karfe 3 da kusan kwata dan asubah ma ta kusa,daukar wayar yayi yabude sakon nan yaganshi kamar haka,
_Abban Aryan kazo gida domin Aryan ba lafiya muna asibitin Dr Al'amin._
Yana gama karantawa yaji yashiga cikin tashin hankali,acikin wannan daren yafita akayi cuku cukun jirgin da zai tashi da asubah zuwa Nigeria,bai dauki komai ba sai wayoyinshi yanufi Nigeria.
Kamar yadda babu wanda yasanar dashi rashin lafiyar Aryan shima babu wanda ya fadawa cewa yabaro Florence yataho Nigeria har saida jirginsu ya sauka sannan yakira PA yace yazo ya d'aukeshi,
Kai tsaye asibitin suka wuce PA ne agaba sai securities dinshi abaya shi kuma yana tsakiyarsu,
"Ni wallahi bana son yaron nan Khalil yaji maganar nan saboda hawan jininsa" umma barira tafada cikin damuwa domin dukkansu suna waje su hudun zaune kofar dakin da Aryan ke ciki kan wasu kujerun karfe wadanda aka tanada awurin domin zama,
"Ai gashi nan ma dan halak" Zaid yafada yana mikewa tsaye,
Hanan kam kanta asunkuye yake ta dunkufar dashi bayan tasha kukanta ta more dan har idanuwanta sunyi jajur ga shi sunyi luhu luhu,wani arnan kamshi ne yafara kaiwa kofofin hancinta sumame wanda ya tilastata ta dago kanta domin ganin mamallakin wannan kamshi,
Hanan kam har washe gari ma bata samu fitaba dan har lokacin bata jin dadin jikinta tadai shirya Aryan ta hada masa komai yatafi school,kuma har yaje yadawo tana kwance a bedroom dinta tana kallon hotunanshi dake cikin wayarshi wadanda sunfi dari,kuma duka nashi ne shi kadai bata ga na babanshi ba duk shi kadai ne akasashe daban daban gaskiya yaron nan ya zagaya duniya domin tun baifi shekara biyu ba ta ga uban yafiffitar dashi manya manyan k'asashen labarawa da na turawa dan wasu hotunan ga larabawa nan wani kuma turawa zaka gani gasu nan dai burjik wani kuma a saudiyya ne dan ga ka'aba nan da sauran kyawawan wurare dake cikin birnin k'asar,ta shagala sosai da kallon hotunan shiyasa har Aryan yadawo bata saniba tana ta kallon hotunanshi shida wasu yara kyawawa suma guda biyu kamarshi mace da namiji taji shigowar Aryan yana zuwa ya haye kanta kamar yadda yasaba, rikeshi tayi tana murmushi,
"Welcome back my Cutie..."
Kankameta yayi suna dariya pic dinshi da yaran nan ta nuna masa tana tambayarshi suwaye wadannan sai yace mata wai nawwar ne da Naina yaran Abba Khalid wai yan uwanshi ne, lallabawa tayi ta tashi taje tayi masa wanka bayan ta cire masa uniform dinshi tabashi abinci yaci sannan yafita islamiyya wurin malaminsa.
Bayan birthday din Aryan da kwana biyu Zaid yakoma gombe yanzu gida yarage sai iya Hanan da Aryan da umma barira,duk wani abu da yashafi Aryan yanzu Hanan ce keyi masa itama shagwabashi yanzu takeyi sosai wanda har Khalil yasan da haka dan komai sai Aryan yace masa wai mommyn shi ce tayi masa idan abinci ne sai yace itace tabashi shi kansa yasan tana kulawa da yaron Sosai ba kadan ba.
***
Har yanzu sumayya bata samu ta shawo kan mujahid ba domin kullum cikin wulakantata yake yauma hakance tafaru tana daki tana ta sharbar kuka mami ta shigo ta zauna gefenta,cikin lallashi tace,
"Sumayya daina kuka kinji,yi hakuri,ki daina sakawa kanki damuwa akan mujahid kedai kawai kici gaba da addu'a idan har mijinki ne babu makawa sai ya aureki....kiyi shiru kinji"
Kai ta daga alamun to,haka mami taci gaba da rarrashinta daga karshe ta tashi tafita,tana fita ta dauki wayarta ta kira k'awarta muhibba ta zayyane mata dukkan abunda yake faruwa sannan cikin kuka ta karasa maganar tata da fadin,
"Muhibba da me Hanan tafini da yake wulakanta ni akanta bayan ma tayi aurenta ita ta manta dashi amma shi kullum cikin kallon hotonta yake...."
"Babu da abinda tafiki sumy,ki kwantar da hankalinki kiji abinda zan fada miki....."
"Ina jinki muhibba"
"Yawwa kema ki shareshi ki fita harkarsa kuma ki daina kulashi,ki nuna masa idan dashi ko babu shi zaki iya rayuwa,ki shareshi fa sosai dan shima yana sonki bawai ke kadai ke haukan sonshi ba saboda duk wanda kake so wallahi shima yana sonka sai dai ko wani dalili ya hanashi bayyanawa amma dan so shima yana sonki,ki danne zuciyarki ki shareshi shi da kansa zai sauko"
Shawarwari sosai muhibba tabata kan yanda zata share ya mujahid har sai yakawo kansa da kanshi,ita dai sumayya ji take yi kamar bazata iya ba saboda irin yanda a kullum wutar son mujahid ke ruruwa a cikin zuciyarta gashi shi kuma yayita disgata agaban kowaye babu ruwansa dazu fa agaban yan aikin gidan yayi mata rashin mutunci dan kawai tashiga dakinsa abinda yasata kuka kenan amma insha Allah zata danne zuciyarta tabata hakuri ta gwada aiki da shawarar muhibba.
***
Bayan birthday din Aryan da sati daya Khalil yadawo nan yakawowa Aryan tsaraba mai tarin yawa ta takalma da jeans da t shirts masu tsada,
Kullum baya shiga gidan sai cikin dare misalin karfe 1 ko 2 wani lokacinma har 3 dan sai kowa yayi bacci agidan,bai jima da dawowa ba yasake komawa k'asar Italy amma kullum suna makale awaya shida Aryan wanda ada yamakale masa wai sai yabishi dakyar ya shawo kansa ta hanyar cemasa ankusa yin hutun makaranta ana yin hutu zai fita dashi duk k'asar da yake so.
Khalil baifi sati daya da tafiya ba Aryan yawayi gari da wani zazzabi mai zafi ga tari da ciwon kirji babu shiri aka kira Dr Al'amin yana zuwa da yadubashi yace su tafi asibiti dan dole sai ya kwantar dashi,
Asibitin suka tafi dukkaninsu cike da damuwa da tashin hankali ita kam umma ma kashe wayarta tayi dan kar Khalil yakirata haka ta Aryan dinma arufe take,kwantar dashi Dr Al'amin yayi yafara bashi taimakon gaggawa,
Aranar da yamma sai ga Zaid yazo kamar yanada masaniyar abinda ke faruwa,can asibitin yabisu dan ajikinsa ma aka debi jinin da aka karawa Aryan din,
Khalil shi bai san abinda yake faruwa ba amma haka kawai yaji jikinsa duk babu dadi kamar irin baida lafiya dinnan alhalin kuma shi lafiyar sa kalau amma dai jikinsa yayi masa wani irin sanyi kalau haka dai ya daure yaci gaba da al'amuransa wadanda suka kaishi,
Yana ta kiran Aryan awaya kuma baya samunshi haka itama wayar umma bata shiga daga karshe sai Zaid ya nema dan jin meke faruwa amma sai Zaid ya ce masa wai babu komai da ya tambayi Aryan sai yace bacci yake yi,cewa yayi to ya gaidashi shida umma sukayi sallama,
Duk dangi kuwa babu wanda bai san rashin lafiyar Aryan ba Khalil kadai aka boyewa saboda ba ason afada masa saboda kar hawan jininsa ya motsa,tun a washe garin ranar da aka kai Aryan asibiti hajiya tazo Abuja suna tare a asibitin suna kula dashi,
Zaid kuwa sai hanya hanya yake yiwa Khalil idan ya kirashi yace ya hadashi da Aryan sai yace yana toilet ko yace yana bacci ko kuma yace wai yana makaranta,da Khalil ya tambayeshi to me yasamu wayar Aryan din da yasa baya samu idan yakira sai yace wai ai swimming pool tafada a hannun Aryan shiyasa ta daina yi nan Khalil yace masa to idan yadawo ya daukeshi suje wurin siyar da wayoyi ya siyo mishi duk wacce yakeso komai tsadarta da toh Zaid ya amsa masa sukayi sallama suna yin sallama yakashe shima tashi wayar gaba daya.
Yau kam tashin hankalinsu yafi na kullum domin tunda garin Allah yawaye Aryan yake ta faman suma daga safe zuwa yamma ya suma yafi sau biyar,shi kansa Dr Al'amin yagama shiga tashin hankali saboda yanda jikin Aryan yarikice Sosai,
Hanan shawara tayi da zuciyarta bata sanarwa da kowaba aranta tace gara ta fadawa Khalil abinda ke faruwa tunda boyewar bata da amfani da afada masa mutuwar dansa gara afada masa rashin lafiyarsa yazo ya ganshi kar aje yamutu,
Text massage ta tura masa tana turawa ta kashe wayarta itama, Khalil na kwance yakasa bacci dan a yan kwanakin nan sam baya iya bacci gashi dai lafiyarshi kalau amma kamar baida lafiya yake jinsa,jin shigowar sako yasashi kallon agogo,karfe 3 da kusan kwata dan asubah ma ta kusa,daukar wayar yayi yabude sakon nan yaganshi kamar haka,
_Abban Aryan kazo gida domin Aryan ba lafiya muna asibitin Dr Al'amin._
Yana gama karantawa yaji yashiga cikin tashin hankali,acikin wannan daren yafita akayi cuku cukun jirgin da zai tashi da asubah zuwa Nigeria,bai dauki komai ba sai wayoyinshi yanufi Nigeria.
Kamar yadda babu wanda yasanar dashi rashin lafiyar Aryan shima babu wanda ya fadawa cewa yabaro Florence yataho Nigeria har saida jirginsu ya sauka sannan yakira PA yace yazo ya d'aukeshi,
Kai tsaye asibitin suka wuce PA ne agaba sai securities dinshi abaya shi kuma yana tsakiyarsu,
"Ni wallahi bana son yaron nan Khalil yaji maganar nan saboda hawan jininsa" umma barira tafada cikin damuwa domin dukkansu suna waje su hudun zaune kofar dakin da Aryan ke ciki kan wasu kujerun karfe wadanda aka tanada awurin domin zama,
"Ai gashi nan ma dan halak" Zaid yafada yana mikewa tsaye,
Hanan kam kanta asunkuye yake ta dunkufar dashi bayan tasha kukanta ta more dan har idanuwanta sunyi jajur ga shi sunyi luhu luhu,wani arnan kamshi ne yafara kaiwa kofofin hancinta sumame wanda ya tilastata ta dago kanta domin ganin mamallakin wannan kamshi,