← Book details Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 61

Sashe 23

Mijin Matacciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fruits da drinks ta jera cikin farantin silver ta dauka ta nufi sashen oga,suna daga ciki suna hangota tana tahowa amma ita bata ganosu sakamakon daga waje glass din mai duhu ne taciki kuma mai haske ne sosai kana kallon na waje tsaff,riga da zani ne ajikinta na atamfa tasaka hijabi,hanan taso tayi kauyanci domin bata san ta yanda zata bude kofar falon nashi ba tana tsaye da faranti a hannunta yataso da kansa yazo ya bude mata bata hanya yayi tawuce ciki sannan ya rufe kofar yabi bayanta,agaban abbanta ta dire farantin tana jin wani farin ciki yana mamaye ta tare da kaunar mahaifin ta wanda tasan har duniya tatashi banda Allah babu wanda zaiyi mata ko rabin gatan da yayi mata,tashi tayi tanufi kofar fita tana zuwa ta danyi tsamm da ranta tana kallon madannan dake gefen kofar bawai dan ta saniba kawai tayi shahada ta danna green din nan take taga kofar ta bude,kasa ta sauka taje ta harhado abinci kala daban daban wadanda John ya dafa saida ta dauko komai sannan ta sake komawa, yanzun ma shine yataso yasake bude mata sannan ta shiga, fruits din da ta kai musu ta iske suna sha da fork kowannensu,

Sunkuyar da kai tayi ta soma gaida abbanta wanda fuskarshi ta cika da fara'a dan bakinsa yaki rufuwa,

"Lafiya kalau uwar masu gida,mun sameku lafiya ko? Ya jikin yaron naki? Allah yabashi lafiya, Allah yasa takin arzikine"

"Amin Abba"

Magungunan da yazo dasu yafirfito dasu wadanda yawancinsu da zuma da zaitun da habbatussauda aka hada yana yimusu bayanin yanda zasu yiwa Aryan amfani dasu,sai bayan da yagama yimusu bayanin sannan ya kalli Khalil wanda ke sanye da farin yadi tsadadde dinkin boda yace,

"Dama ahar kullum ina fada maka yaron nan sai shima ka kula dashi da addu'o'i da zikirin safiya da maraice,wani abun idan kai anyi maka aka ga bai sameka ba to za a iya komawa ayiwa danka,kai kam bani da jaa akanka kana da kariya sosai atare dakai saboda duk wanda yayi riko da ibada ya tsaida salla kuma ya kiyayeta sannan yake yawaita tsayuwar dare da sadaka kuma yabi iyayensa to babu mahalukin da zaiyi nasara akansa sai dai makiya su gaji su barshi dan yafi karfinsu to amma shi sulaimanu ai kaga yarone dole sai ankula dashi, Allah yabashi lafiya kuma insha Allah nasamo bakin zaren,insha Allah zai samu waraka,sihiri ne akayi masa kuma mace ce tayi amma idan nace gata to nayi karya,amma tabbas mace ce dan naganta acikin mafarki,wato kasan wani sihirin akwai addu'ar da akeyi ayi salla raka'a biyu to Allah yana haskawa mutum inda aka yimasa sihirin idanma binnewa akayi duk za anuna maka wurin...."

Daga Hanan har Khalil jikinsu ne yayi sanyi Sosai, Hanan aranta cewa takeyi wannan wanne irin rashin imani ne da mutum zai nemi halaka dan tahalikin yaron da baiyi masa laifin komai ba? Ita kuwa wannan matar me Khalil yayi mata da har take kokarin hucewa akan dansa? Kwalla taji ta ciko mata ido bata gogeba saida tabarta ta sauka,

Shi kam Khalil shiru yayi yana tunanin to wacece wannan? Zuwa caan ya sauke ajiyar zuciya ya tankwashe kafafuwanshi yana lankwasa yan yatsun kafarshi domin yagano ko wacece, Abba ne ya kalli Hanan sannan yace,

"Yanzu kiyi azamar zuwa kibashi magungunan nan yasha sannan ki shafe masa jikinsa da wadannan mayukan,insha Allah zai samu waraka"

"Toh Abba"

Tashi tayi ta dauki maganin tafita,sai bayan da ta fita sannan Khalil ya kalli Abba yace,

"Nagode madallah malam, Allah yasaka maka da alkhairi,kuma ba dan kar kace nayi zargi ba wallahi har nagano wadda tayi min wannan abun...., bazai wuce yesmin ba,tajima tana bibiyata kuma ita ba da aure take sona ba a'a da sabon Allah nikuma ba halina bane,babu wanda bai san zaman kanta take yiba...., Yanzu last zuwan da nayi Denmark sai da tabini hotel din da nasauka....."

"Ai shiyasa nake fada maka dole sai ka dage da addu'a da rokon Allah saboda mata iri iri zasuyi ta kawo maka farmaki sai dai Allah ya tsareka ya kareka daga kaidinsu...."

"Amin" yafada yana sunkuyar da kanshi kasa,shi dai Abba cigaba da bashi shawarwari yayi ta yi yanda zai cigaba da neman tsari daga kowacce irin mace. Hanan na zuwa dakin Aryan ta samu hajiya da umma atare dashi,sune suka taimaka mata tabawa Aryan magungunan yasha sannan ta shafe masa jikinsa da wadanda abba yace mata na shafawa ne,kuma sauki kam ana samu sai godiyar Allah dan ko minti 20 baiyi da shan maganin ba yace zaici abinci wanda rabon da yaci anjima,abinda yake son ci Hanan ta tambayeshi yace shinkafa dama akwai shinkafa acikin abubuwan da John yadafa yau dan haka ta sauka da sauri taje ta zubo masa a plate ta kawo,itace ta zauna ta bashi abaki kuma babu laifi ya dan ci dayawa daga nan bacci yakoma ita kuma tafita taje d'akinta tayi wanka sannan tayi sallar la'asar,wurin Aryan ta sake komawa tasamu suma su umma har lokacin suna tare dashi yatashi daga baccin da yake yi yanata game a wayarshi, gefenshi ta samu ta zauna ta dora kanshi saman cinyarta tana tofa masa addu'a ahaka Khalil yabude kofa yashigo ya samesu ganin Aryan yana game yaji dan sanyi sanyi acikin ransa,hannu yakai saman goshin Aryan yace,

"Sannu abba na,jiki yafara sauki ko?"

Kai Aryan ya daga sannan yace,

"Uncle zaka tafi dani Italy ko?"

"Zanje dakai duk inda kake so abbana, Allah dai yabaka lafiya"

Daga haka yajuya yafita yakoma wurin Abban Hanan wanda ke can yana jiranshi, ita kuwa Hanan tana wurin Aryan har magriba tayi dan anan ma dakin Aryan tayi sallah tana idarwa taji shigowar text cikin wayarta,

_Kizo abbanki na kiranki._

Shine abinda taga minister yaturo mata tashi tayi tafita saida tafara shiga bedroom dinta ta shafa turare sannan tafita tana sanye da doguwar riga yar kanti da farin hijab ajikinta, tsayawa tayi bakin kofar tana wurwurga ido shin ina zata taba? Jan ta danna sai kuwa kofa tabude,ahankali cikin nutsuwa take takawa har zuwa cikin hadadden falon nashi wanda yafi kowanne falo dake gidan haduwa,komai nashi farine tas babu sirki,hatta Rug din dake shimfide a tsakiyar falon farine sai dai an diddiga masa kalar baki dan sake fito dashi,falon tafkeke ne na gaske amma sai dai babu tarkace masu yawa acikinsa,iya kujeru ne wato (Turkish Sofas) farare guda biyar sai glass tables manya da kanana an a'ajjiye su a muhallin da yadace dasu sannan ga kayan kallo manya manya sai fridge acan gefe daya sannan ga dining table da yan kujerunsa kwaya hudu shima farare acan gefen dama,daga gefen hagu kuma wasu fararen kujerunne kwaya biyu masu laushi an ajiyesu da farin Rug dan karami a tsakiyar su sai center table atsakiya,kai falon dai yayi ba karya kuma ya hadu karshen haduwa,ga toilet nan aciki sannan sai kofar bedroom dinshi agefe ta can bangare daya kuma kofar da zata sadaka da valcony ce wadda aka shiryata domin hutawa dan yanzun ma haka su abba acan suke suna hira,

Hanan tsaye tayi domin bata san inda zata nufaba, maganar su tajiyo suna kokarin shigowa,

"A'a ashe ma ga mai babban sunan har ta karaso"

Tajiyo muryar Abba yana fada cikin raha shi dai minister bata ji me yace ba, Abban ne yafara shigowa ya nemi wuri ya zauna sannan itama ta zauna akasa tana sunkuyar da kanta,

Sake sabuwar gaisuwa sukayi da abba sannan suka cigaba da hirar gida wanda ba karamin dadin hakan Hanan tajiba shi kuwa Khalil har har lokacin yana valcony yana shan iska daga Allah bai shigo falonba sai da yaji ana kiran sallar ishah, Hanan tasake sosai da abbanta yashigo,dan satar kallonsa tayi taganshi sanye cikin wasu kayan wadanda ba na dazu ba saboda yanzu milk colour din shadda ce ajikinsa sai kyalli takeyi dinkin half jamfa yayi kyau yayi kyau har ya gaji,

"Bari muyi salla ko..." Taji abbanta yafada,tashi tayi tana fadin,

"To Abba,bari naje na kawo muku abinci"

Fita tayi sukuma nan cikin falon suka tada kabbarar sallarsu ita kuma tawuce kitchen taje ta zuzzubo musu abincin da aka shirya na dare,suna salla duk ta kawo ta ajiye musu sannan tafita.

Bata sake komawa sashen minister ba sai wurin karfe 9 shi lokacin ma yana d'akin Aryan tare dashi dasu hajiya yadora Aryan din asaman cinyarsa yana yin game awayarsa,bata ga abbanta ba sai kayan kawai ta debo ta fito dasu tasan watakila abban yana masaukinsa dan dakyar ma ya yarda zai kwana da cewa yayi ayau zai koma,

Dakin Aryan ta shiga inda su hajiya ke ciki itada umma dakin gauraye da kamshin turaren Khalil na no 1 wanda ya mamaye dakin gaba daya,sai bayan da ta rufe kofar dakin sannan idanuwanta sukayi arangama dashi zaune dare dare bisa kan gadon Aryan ga kuma Aryan din akan cinyarshi,zama tayi gefen umma tana satar kallon Khalil wanda ke cikin blue din riga ta polo sai dogon blue din wando mai santsi,kamar lokacin da tafara ganinsa yanzu ma shagala tayi da kallonsa yana ta yiwa Aryan wasa wanda ke yin game,

"Mommy zan sha ruwa..." Taji Aryan yafada,

Tashi tayi ta dauko masa ruwan maganinsa wato ruwan addu'a taje ta mika masa,karba yayi yatashi zaune yasha sannan yakoma ya kwanta,ayanda ta lura Khalil ba mai yawan magana bane domin idan aka bata dama tsaf zata kirge adadin maganarsa tun shigowar ta dakin,iya umma da hajiya ne kawai ke ta hirarsu. Sai da Aryan yayi bacci sannan Khalil yafita,bayan fitarsa da yan mintuna itama tafita ta nufi bedroom dinta,shirin bacci tayi ta kwanta tana lumshe idanuwanta cike da begen Khalil....................✍️

*_Ummi Shatu_*👌🏻
8/14/20, 10:08 AM - Ummi Tandama: *Book din mijin matacciya na kudine game bukatar siya sai atura 200 ta account din Aisha Ibrahim, 3112877210 first bank,sai atura shaidar biya ta WhatsApp number dina 07044644433 ko kuma atura recharge card da shaidar biya ta number din.*

*21*
Chapter 23 · 0% Book details