← Book details Martabata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 27

Sashe 26

Martabata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dan gutsiren tuwo tasa a plate ta zuba yar miya ta fara ci, sam bata jin dadin tuwon kawai ci take domin rabonta da abinci har ta manta shiyasa duk ta dashe sai uban fari kauu da tayi, kallon jawad tayi sai zira lauma yake kamar zai hadiye kwanon, tana kallonsa ya cinye ya sake karawa ganin haka sai kawai ta fashe da kuka, cikin tashin hankali ya kalleta tareda matsowa kusa da ita,
"Queen menene?"
"Jawad bana jin dadin abinci gashi bakina babu dadi, komai naci bana jin dadinsa sam yanzu bakina babu taste" ta fada tana share hawayen idonta,
"Am sorry dear, tun yaushe?"
"Tunda na koma sch fa, wlhi rabona da abinci har namanta"
Hannunta ya kama ya rike cikin nasa fuskarsa cikeda tausayinta,
"Sorry queen, ko na kaiki kiga dr?"
Girgiza kai tayi
"Why?"
"Nidai basai naje asibiti ba" tafada cikin shagwaba
"Ayya sorry, to na kira miki dr ansar?" Nanma kai ta girgiza, hadata yayi da jikinsa yaci gaba da bata abincin a baki amma dakyar ta yarda ta ci rabin wanda ta zuba, "my pherty sarkin daru" yafada tareda jan hancinta.

Daren ranar kuwa bata yarda ta hada daki da jawad ba saboda wai bata son kamshin turaren da yake yi, juyin duniyar nan yayi taki yarda ya kwanar mata adaki yayi rarrashin har yagaji yayi fushi ya fita daga dakin.

Washe gari da safe kuwa kowa harkar gabansa yake ita fushi jawad fushi, shi jawad fushin da yake na ta hanashi kanta ne alhalin rabonshi da ita anfi sati uku, ita kuma pherty nata fushin na tana fama da lalura ne gashi kuma jawad bai nuna tausayinsa akanta bane,
Wanka tayi ta tsuke cikin riga blue body hug mai kyan gaske an rubuta IT'S YOUR TIME!

Ajiki, da bakin wando mai laushi amma kuma tied ne, bakar hula tasa ta fita baya taje ta soya dankali da kwai tayi yar sos tana yi tana zuwa zubar da yawu da haka har ta gama ta hado kayan ta kawo masa kan dining sannan ta koma ta juyo ruwan zafin data dafa ta kawo masa, yana kallonta babu abinda taci sai aikin zuwa zubar da yawu minti kadan sai ta tashi haka ta kwanta akan doguwar kujera, ganin haka ya sashi sassauto da nashi fushin yazo ya sameta,
"Xarah me kike son ci naje na siyo miki?"
Bude idonta tayi ta kalleshi,
"Jawad babu abinda zan iya ci sai abu me k'uli k'uli"
"Zaki ci indai mai k'uli k'uli ne?"
Kai ta daga alamun ehh, key din motarshi ya dauka ya fita, wayarta ta dauka ta kira su A'isha tana fada musu to yanzu gashi nan mijinta ya tafi samo mata abinda take so tunda su basa nemo mata.

Kasuwa jawad ya shiga nan ya fara neman abinda zai siyo mata, zogale da kuli kuli ya siyo mata sannan yaga gurasa da kuli kuli nanma ya siyo daf da zai fita daga kasuwar yaga agwaluma itama ya tsaya ya siyo.

Lokacin da ya koma tana kwance inda ya barta tana bacci dan haka bai tasheta ba ya ajiye mata kayan ya fita ya nufi gidan ummi, bai dade da fita ba ta tashi, ai tana ganin kayan da ya siyo mata taji yawunta ya tsinke nan ta sauka ta zauna a kasa ta dauki zogalen da guraza ta fara zurawa, ita kuwa agwalumar da ya siyo mata koda yaushe tana tareda ita tana sha.

Ranar asabar da wurwuri ta tashi ta fara shiryawa su mama delicious, fried rice tayi musu mai dadin gaske ta soya musu kaji sannan tayi musu kunun shinkafa duk bata jin kasala yau saboda dokin zuwansu mama, bayan ta gama shirya komai ne taje ta tsalo wanka tasa wata koriyar atamfa dinkin riga da skirt mai tattara rigar ma tasha tattara, bata yi kwalliya ba saboda ko mai bata shafa ba, falo ta fito ta duba agogo lokacin karfe 11 da minti 15,
"Oh nikam mama anya zasu zo?" Ta tambayi kanta, tana nan zaune har 11:30 duk ta kosa da zaman jiran da take, kamar daga sama taji shigowar mota gidan da saurinta taje ta leka window, maman hawy ta hango da mamanta da kuma hawyn, da sauri ta nufi kofa taje ta taro su,dakinta ta kaisu bakinta yaki rufuwa sai murna take, bayan ta gabatar musu da kayan saukar da tayi musu ne suka gaggaisa sannan ta jawo hawy suka koma daya dakin.

"Phertyn mama kinyi fari gashi kin dan rame" Hawy tafada cikeda tausayi akan fuskarta,
"Um hawy ai dole na rame saboda bana cin abinci kwata kwata"
"To ai ga kanzon da kike so can an taho miki dashi"
Tashi pherty tayi taje ta dauki kanzon cikin leda viva ga kuli kuli dakakke, kitchen takai kayan ta debi wani acikin kwano ta jika tun anan taji yawunta ya guda saboda yanda kanzon yake fari tas daga gani na masara ne da shinkafa a hade, kyakkyawan hadi tayi masa tasa man gyada ta yanka kayan miya ta dauki maggi ta nufi wurin hawy,kallonta hawy tayi tana dan murmushi,
"Allah ya bada lfy amma agaskiya ki rinka cin abinci pherty"
Yamutsa fuska pherty tayi "wlh ba laifina bane, bakina ne babu taste in banda bakin shayi babu abinda nake iya sha"
"To Allah ya rabaku lfy dai"
"Amin" nan kuma suka shiga hirarsu har tsawon wani lokaci,suna nan zaune jawad ya leko bayan yaje sun gaisa dasu mama,
"Xarah kawo min abincina daki" zaraf hawy tayi tafara tsokanarsa "kaga ango" murmushi kawai yayi mata suka gaisa ya wuce,
Tiren abinci pherty ta dauka ta nufi dakin jawad kanta tsaye ta wuce cikin dakin ta dora abincin akan dan karamin stool din dake girke gefen gadonsa, ta bayanta taji yazo ya rungumeta,
"Sannu da kokari my queen"
"Yawwa sannu" tafada tana kokarin kwacewa, sakinta yayi ya bata hanya ta wuce ta koma wurin hawy, yinin ranar nan tayi shine cikin farin ciki sai yamma likis sannan su mama suka tafi nan kuma taji hankalinta ya tashi sosai, suna tafiya tasa kuka, rungumeta jawad yayi ya maida ita cikin dakinta.

Ummi Shatu🏻
[6/5, 7:43 PM] Ummi A'isha🏻: [6/2, 6:40 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑
Na
UMMI A'ISHA
84-85
~~~ Dakyar jawad ya iya shawo kan pherty ta daina kukan tafiyar su mama, hannunta ya kama
"Oya taso ki rakani unguwa"
Babu musu ta saka after dress ta gyara fuskarta tabishi, wakar p square ya kunna musu lokacin da suka hau titi, gidan yaya aadil taga ya nufa, dan murmushi tayi mai kayatarwa ta kalleshi shima kallonta yayi yana murmushin har suka isa gidan.

Hannunta rike cikin nashi har tsakiyar falon su yaya aadil, anty Salima na zaune tasaka katon cikinta gaba tana kallo shi kuma yaya aadil yana kitchen yana yi musu girki, pherty ji tayi sun burgeta domin dama can shi yaya aadil tasan mutumne shi mai saukin kai, zama tayi kusa da anty Salima yayinda shi kuma jawad yabi aadil kitchen.

Dakyar yauma ta iya gaida yaya aadil amma tasaki jiki da Salima sosai suna hirarsu, har dare suka kai agidan kafin suka yi musu sallama suka tafi, ahanya saida jawad ya tsaya yayi musu siyayyar kayan makulashe gasasshen kifi dasu ice cream da chocolate sannan suka karasa gida, bayan pherty ta zauna ta tande kayan dadin da jawad ya kawo matane kuma ta mike da niyyar tafiya dakinta, kallonta jawad yayi da kalar tausayi amma ta maze tayi tafiyarta saboda ita yanzu wannan abun duk ya fita aranta.

Washe gari ranar sunday ta shirya zata koma sch jawad dai sai cika yake yana batsewa ya murtuke fuska haka ya kaita ya dawo amma kawai kyaleta yayi saboda yasan idan ya nuna mata karfi dan karamin cikin dake jikinta yana iya zubewa, ko kallonta baiyi ba lokacin da ta fita daga motar ya figi motarsa yayi gaba.

Tun daga wannan ranar ya shareta ba waya ba zuwa haka ya rabu da ita, ita kam pherty hakan yafi mata domin yanzu tana bukatar hutu, satinta biyar cif a sch tsakaninta da jawad babu wani communicating ko ta ganshi online baya kulata itama haka, bayan sallar magrib ta fara kiran wayarsa saboda yau kwadayin kifin da ya taba siyo mata take,wayar tajima tana ringing sannan ya daga a hankali,
"Hello Xarah" ya fada kamar me yin rada,
"Jawad kana inane?"
"Naje hirane wurin kanwarki, lfy?"
Dam taji gabanta ya harba, "hira jawad?

Wacce kanwar tawa?

Wacece?" Ta jero masa wadannan tambayoyin ajere,
"Gata zaku gaisa"
Kafin tayi wata maganar sai jin muryar mace tayi tana yi mata sallama, tabbas wannan koma wacece tayi sa'a da samun zazzakar murya domin muryarta carkwai take nanfa kishi ya motsa pherty ko amsa sallamar da yarinyar tayi mata bata yiba balle ta tsaya amsa mata gaisuwar da take yi yanzu, kit ta kashe wayarta ta tura masa text massage kamar haka...

"Idan ka gama hira da budurwar taka ka siyo min gasasshen kifi ka kawo min"
Tura masa text din tayi duk ranta abace, lallai jawad wato ita yabarta da fama shikuma can yatafi neman aurensa ko?

Haka tayi ta fada cikin zuciyarta,
Bayan sallar isha sai ga text dinsa wai ta fito ta karbi kifin gashi ya kawo mata, ranta a hade ta fice daga cikin dakin su dai su aisha da Sadiya basu san ko me ya bata mata rai ba, tana zuwa inda jawad yake ta tsaya daga waje ta rike kugu, lekowa yayi ya kalleta,
"Ki shigo mana queen"
Cikin bacin rai ta bude kofar motar ta shiga ta zauna fuskarta a daure,
"Malam bani sakon danni ba zama nazo yi ba, kuma wlhi gidanmu ni zan tafi inyaso kai sai ka zauna da amaryarka" tafada hawaye yana sauka akan kumatunta, light din cikin motar ya kunna ya tsura mata ido yanzu kam alamun masu ciki sun gama bayyana a tareda ita ta danyi kumatu fatarta tayi subul gashi cikin nata yadan fito kadan amma ba kowane zai gane ba,
"Queen koda nayi aure ke ta dabance a rayuwata, bazan taba mantawa dake ba, kece first lady"
Kallonsa tayi "dagaske auren zakayi kenan?"
Kai ya daga mata, "aure zanyi amma ba wai dan nadaina sonki ba, kuma kin san wani abu?
Chapter 26 · 0% Book details