Sashe 25
Martabata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi Shatu🏻
[6/2, 10:11 AM] Ummi A'isha🏻: [5/31, 9:07 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑
Na
UMMI A'ISHA
82
~~~ Kara wayar tayi ajikin kunnenta ta soma yin magana a hankali,
"Jawad ya kaje gida?"
"Bayan kin manta dani" ya fada a shagwabance,
"Kayi hakuri yanzu nake son kiranka dama"
"Haka dai kikace, yau kin manta dani saboda kin samu su mama ko?"
Girgiza kai tayi kamar yana kallonta,
"A'a kana raina kaima ban manta da kai ba"
Sun dan taba hira kadan sannan suka yi sallama ta kashe wayar, ta karasa raka hawy,
"Um soyayya, yanzu kina sonshi kenan?" Inji Hawy,
"Da ance miki bana sonshi ne?" Pherty ta fada tana hararar hawy,
"Ato idan ke kin manta to ni ban manta ba" hawy tafada tana murmushi,
"Kinga malama sai da safe wanka nake son zuwa inyi yanzu yanzu" tana fadin haka ta juya ta nufi gida tana yiwa hawy dariya.
Wanka tayi bayan ta koma gida, shiryawa tayi ta dawo falo wurinsu mama nan suka bude sabon babin hira har karfe 10 tayi sai a lokacin kowa ya tashi ya nufi makwancinsa, kan gadon mama taje ta dale tana fadin,
"Mama yaushe rabona da hawa gadonki?
Yau akai zan kwana"
"Kema ai kin samu naki gadon ja'ira" mama ta fada daidai lokacin da take fita daga cikin dakin, murmushi pherty tayi ta lumshe idonta.
Tunda pherty taje gida kullum suna tareda hawy suna hira, jawad kuwa kyaleta yayi har sai da tayi kwana biyar sannan yazo ya dauketa suka tafi bayan su mama sun hada musu goma ta arziki.
Dawowarsu gida sunyi rayuwa mai dadi kuma jawad ya nuna mata yayi missing dinta over, kwananta 6 ya hado mata provision ta koma sch bayan su Sadiya sunce mata suma sun koma, tsarabarsu ta saudiyya ta fiddo musu ta basu kowaccensu riga da wando na pakistan da takalmi flat mai tsada ta siyo musu, sunyi murna mutuka tareda addu'ar Allah yasa sun kusa shan suna ai kuwa kamar sun fada a bakin "yan amin domin ko sati daya ba ayi ba pherty tafara jin wani irin yanayi a tattare da ita.
Babu rashin lfy babu amai babu komai sai dai tana jin tashin zuciya ga yawu da yake taruwa a bakinta, tana zaune agefen gadonta da zani daurin kirji tana tsifar kai, sadiya kuma tana rubutu akan gadonta itama yayinda A'isha take kwalliya wani man shafawa A'isha ta ciro da niyyar shafawa tashi pherty tayi ta fita waje taje ta zubar da yawun bakinta ta dawo gefen gadonta ta zauna,
"A'isha man nan naki tayar min da zuciya yake wlhi" pherty tafada tana yamutsa fuska,
"Ke kuma naki cikin haka yake?" Sadiya tafada tana dariya,
"Ni ba cikine dani ba kawai son ganin man nata ne banayi" pherty ta mayar mata da amsa,
"To idanma cikin ne menene?
Dama ai tunda akayi aure ai an san za ayi haihuwa" A'isha tafada tana dariya, tsaki pherty tayi,
"Ku kuka sani dai"
Tashi tayi ta dauki cumb da kibiyarta ta fice tabar dakin ta nufi wani dakin ba ita ta dawo ba sai wurin bayan awa hudu, tana shiga ta samu sun kunna risho sun dora musu abinci,ji tayi zuciyarta ta tashi sakamakon warin rishon da taji ta shaka,
"Dan Allah ku rinka kunna rishon nan awaje" kallonta suka yi,
"Saboda?" A'isha ta tambayeta,
"Saboda bana son warin risho"
Dariya sadiya tayi harda kwalla sannan tace "sai ance kinada ciki kice ke bakida ciki to meye warin risho?
Ba wani wari da rishon nan keyi kece kike ji"
"Sai kiyi kuma" pherty ta fada tareda saka kayanta ta fita ta nufi captaria domin samowa cikinta abinda zata saka masa domin yanzu bata sha'awar abinci totally, abinci ta gani da kayan ciye ciye kala kala lokacin da taje captaria amma duk basu yi mata ba sai ma tashin zuciya da take ji, a wurin wata mata mai siyar da abinci ta hango awara acikin farin bokiti, awarar taje ta siyo ta dari biyu ta sai coke mai sanyi ta koma hostel.
A inda ta tafi ta barsu ta dawo ta samesu suna zaune suna cin abinci, kan gadonta taje ta zauna ta kalli abincin da suke ci, taliya da wake jallop, idonta ta dauke saboda yanzu duk abubuwan da take so da ta tsanesu,
"Zo kici abinci ga naki nan a flask" Sadiya ta fada,
"Ba zan ciba ku cinye" tafada cikin sanyin murya,
"Meyasa?" A'isha ta tambayeta,
"Awara zanci gata na siyo"
"Ashe zamuci awara yau" inji Sadiya
"Dai dai zan san muku wlhi wannan shine abincina har dare" ta fada tareda mika musu awarar guda biyu, yaji ta dauko ta fara dandana tana cin awarar har ta ci rabi sannan ta daure sauran ta ajiye ta dauki coke ta kora ta sauka kasa ta zauna tana jiran Sadiya tayi mata kitso, koda aka zo kitson ma wai ba za asa man kitso ba bata son kamshin man haka akayi kitson suna yi suna fada da sadiya har suka gama.
Yau rabonta da jawad sati uku kenan saboda tun dawowarta sau 1 yazo mata hira shiyasa ta shirya tafiya weekend acikin wannan satin, tana zaune tayi zugum tana tunanin abin yi saboda kwadon kanzo take son ci yau domin yanzu ta tsani awarar da ta zama abincinta da, tun ranar da tayi aman awarar taji ta fita daga cikin ranta,
"Pherty me zan dafa mana?" A'isha ta tambayeta lokacin da take kokarin fitar da rishon da zatayi girkin waje,
"A'isha wallahi kanzo nake son ci, nidai jawad ya hadani da lalura" takarasa maganar acikin zuciyarta,
"Kanzo?" Sadiya ta fada cikin mamaki,
"Yanzu a ina za asamu kanzo?
Indai ba son wahalar da kai ba kin san dai duk hostel dinnan ba za asamu kanzo ba" A'isha ta bata amsa,
Kallonsu tayi daya bayan daya kawai sai ganinta suka yi ta fara hawaye,
"Yi hakuri zamu samo miki, ai dole mu samowa dan baba kanzo" Sadiya ta fada tana dariya tareda tashi ta fita, itama A'isha fitar tayi suka tafi yawon neman kanzo duk kuwa da cewar sun san abune mai wahala samun kanzo acikin hostel.
Ita kam pherty suna fita ta shafa cikinta tana goge kwallar idonta, "yanzu jawad shi babu abinda ya dameshi yana can yana zamansa lfy ni kuma nan ya barni da laulayi" haka ta fada acikin ranta, tana nan zaune suka dawo basu samo kanzon ba nanfa taji hankalinta ya tashi wani kukan tafara kokarin yi amma shigowar Ummi Hambali yar department dinsu yasa ta hadiye kukan,
"Pherty ga wainar fulawa na kawo miki" ummin tafada tana mika mata wani flask karba tayi fuskarta dauke da murmushi,
"Nagode ummi kamar kuwa kin san yau babu abinda naci" da sauri ta dauko yaji ta fara ci ko sadiya da A'isha bata barwa ba sai da taji tayi dam sannan hankalinta ya dawo jikinta.
Harararta Sadiya tayi "malama ki kira mijinki ya kawo miki kanzo saboda kar kizo kina tashinmu cikin dare kina cewa ke kanzo kike so"
Dariya A'isha ta saka "wlhi kar kisa yau naki kwanan dakin nan"
Murmushi pherty tayi "idan kunyi hakuri ma gobe zan tafi gidana wurin mijina"
"Dakyau dan Allah idan kinje kar ki dawo sai kin samo kanzon" Sadiya ta mayar mata da amsa, murmushi kawai tayi ta dauki wayarta ta soma kiran mamanta suna gaisawa ta fara yi mata zancen kanzo take so akawo mata,
"Kanzo kuma pherty?"
"Eh mama dan Allah ki kawo min dama kinga fa baki taba zuwa gidana ba mama, dan Allah kizo" ta fada cikin shagwaba
"To shikenan bari mahaifinki yazo zan sanar masa idan ya yarda zanzo ranar asabar idan kuma bai yarda ba to zan taso hawwa kawarki ta kawo miki"
"Mama dan Allah Ku taho tare dan Allah"
"To shikenan phertyma sai ranar asabar din"
Kashe wayar tayi tana murna nan ta tsiri shirin tafiya gida.
Washe gari da yamma kuwa jawad yazo ya dauketa, sai kallonshi take cikin burgewa komanshi tsaf tsaf amma ita ya hadata da aiki bata da aiki sai tara yawu ta zubar, shi kam jawad bai ma san tana da cikin ba.
Suna zuwa gida ta fita daga motar taje ta zubar da yawun bakinta,
"Jawad murhun karfe da itace zaka siyo min kasa min acan baya dan bazan iya girki a gas ba" ta fada tana yatsina fuska, hannunta ya kama suka shiga cikin falo ya zaunar da ita akan cinyarsa, zumbur ta tashi saboda kamshin turarensa da ta shaka nan taji cikinta ya soma juyawa zuciyarta ta fara tashi.
Ummi A'isha🏻
[6/3, 7:27 AM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑
Na
UMMI A'ISHA
83
~~~ Zumbur ta tashi saboda kamshin turarensa da ta shaka nan taji cikinta ya soma juyawa zuciyarta tafara tashi, yawune ya cika mata baki da sauri ta shiga dakinta nan dinma babu dadi domin kamshin da dakin yake yi shima baiyi mata ba, toilet ta shiga ta zubar da yawun bakinta ta koma falo wurin jawad,
"Queen wai meke faruwa ne?" Ya tambayeta
"A inafa?" Itama ta tambayeshi
"To naji kince na siyo miki murhu, me zai hana ki rinka girkin a electric stove tunda kince baki son yin girki a gas"
Zama tayi nesa dashi ta yatsina fuska,
"Nifa gaba daya warin girkin ma da warin rishonne bana so har warin gas din duk bana so murhu nake son ka samo min da fire wood"
"Angama ranki ya dade" mikewa yayi ya fita dan siyo mata murhun, tashi itama tayi ta shiga dakinta tana tottoshe hanci nan ta tattara kayan da zata bukata ta koma daya dakin kuma cikin sa'a sai taji nan din babu kamshin da bata so din.
Kamar yadda tace haka jawad ya siyo mata murhu guda biyu da itace ya kawo mata, acan bayan kitchen dinta ta ajiye murhun ta kunna wuta ta dora abinci, tuwon shinkafa miyar wake da busasshen kifi tayi, lokacin data gama jawad yana kishingide a falo,gabansa ta kawo abincin ta jere tashiga dakinta taje tayi wanka ko mai bata shafa ba saboda shi kansa man tayar mata da zuciya yake, yar doguwar riga ta shan iska ta zira tafito falo inda jawad yake zaune yana cin abinci.
[6/2, 10:11 AM] Ummi A'isha🏻: [5/31, 9:07 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑
Na
UMMI A'ISHA
82
~~~ Kara wayar tayi ajikin kunnenta ta soma yin magana a hankali,
"Jawad ya kaje gida?"
"Bayan kin manta dani" ya fada a shagwabance,
"Kayi hakuri yanzu nake son kiranka dama"
"Haka dai kikace, yau kin manta dani saboda kin samu su mama ko?"
Girgiza kai tayi kamar yana kallonta,
"A'a kana raina kaima ban manta da kai ba"
Sun dan taba hira kadan sannan suka yi sallama ta kashe wayar, ta karasa raka hawy,
"Um soyayya, yanzu kina sonshi kenan?" Inji Hawy,
"Da ance miki bana sonshi ne?" Pherty ta fada tana hararar hawy,
"Ato idan ke kin manta to ni ban manta ba" hawy tafada tana murmushi,
"Kinga malama sai da safe wanka nake son zuwa inyi yanzu yanzu" tana fadin haka ta juya ta nufi gida tana yiwa hawy dariya.
Wanka tayi bayan ta koma gida, shiryawa tayi ta dawo falo wurinsu mama nan suka bude sabon babin hira har karfe 10 tayi sai a lokacin kowa ya tashi ya nufi makwancinsa, kan gadon mama taje ta dale tana fadin,
"Mama yaushe rabona da hawa gadonki?
Yau akai zan kwana"
"Kema ai kin samu naki gadon ja'ira" mama ta fada daidai lokacin da take fita daga cikin dakin, murmushi pherty tayi ta lumshe idonta.
Tunda pherty taje gida kullum suna tareda hawy suna hira, jawad kuwa kyaleta yayi har sai da tayi kwana biyar sannan yazo ya dauketa suka tafi bayan su mama sun hada musu goma ta arziki.
Dawowarsu gida sunyi rayuwa mai dadi kuma jawad ya nuna mata yayi missing dinta over, kwananta 6 ya hado mata provision ta koma sch bayan su Sadiya sunce mata suma sun koma, tsarabarsu ta saudiyya ta fiddo musu ta basu kowaccensu riga da wando na pakistan da takalmi flat mai tsada ta siyo musu, sunyi murna mutuka tareda addu'ar Allah yasa sun kusa shan suna ai kuwa kamar sun fada a bakin "yan amin domin ko sati daya ba ayi ba pherty tafara jin wani irin yanayi a tattare da ita.
Babu rashin lfy babu amai babu komai sai dai tana jin tashin zuciya ga yawu da yake taruwa a bakinta, tana zaune agefen gadonta da zani daurin kirji tana tsifar kai, sadiya kuma tana rubutu akan gadonta itama yayinda A'isha take kwalliya wani man shafawa A'isha ta ciro da niyyar shafawa tashi pherty tayi ta fita waje taje ta zubar da yawun bakinta ta dawo gefen gadonta ta zauna,
"A'isha man nan naki tayar min da zuciya yake wlhi" pherty tafada tana yamutsa fuska,
"Ke kuma naki cikin haka yake?" Sadiya tafada tana dariya,
"Ni ba cikine dani ba kawai son ganin man nata ne banayi" pherty ta mayar mata da amsa,
"To idanma cikin ne menene?
Dama ai tunda akayi aure ai an san za ayi haihuwa" A'isha tafada tana dariya, tsaki pherty tayi,
"Ku kuka sani dai"
Tashi tayi ta dauki cumb da kibiyarta ta fice tabar dakin ta nufi wani dakin ba ita ta dawo ba sai wurin bayan awa hudu, tana shiga ta samu sun kunna risho sun dora musu abinci,ji tayi zuciyarta ta tashi sakamakon warin rishon da taji ta shaka,
"Dan Allah ku rinka kunna rishon nan awaje" kallonta suka yi,
"Saboda?" A'isha ta tambayeta,
"Saboda bana son warin risho"
Dariya sadiya tayi harda kwalla sannan tace "sai ance kinada ciki kice ke bakida ciki to meye warin risho?
Ba wani wari da rishon nan keyi kece kike ji"
"Sai kiyi kuma" pherty ta fada tareda saka kayanta ta fita ta nufi captaria domin samowa cikinta abinda zata saka masa domin yanzu bata sha'awar abinci totally, abinci ta gani da kayan ciye ciye kala kala lokacin da taje captaria amma duk basu yi mata ba sai ma tashin zuciya da take ji, a wurin wata mata mai siyar da abinci ta hango awara acikin farin bokiti, awarar taje ta siyo ta dari biyu ta sai coke mai sanyi ta koma hostel.
A inda ta tafi ta barsu ta dawo ta samesu suna zaune suna cin abinci, kan gadonta taje ta zauna ta kalli abincin da suke ci, taliya da wake jallop, idonta ta dauke saboda yanzu duk abubuwan da take so da ta tsanesu,
"Zo kici abinci ga naki nan a flask" Sadiya ta fada,
"Ba zan ciba ku cinye" tafada cikin sanyin murya,
"Meyasa?" A'isha ta tambayeta,
"Awara zanci gata na siyo"
"Ashe zamuci awara yau" inji Sadiya
"Dai dai zan san muku wlhi wannan shine abincina har dare" ta fada tareda mika musu awarar guda biyu, yaji ta dauko ta fara dandana tana cin awarar har ta ci rabi sannan ta daure sauran ta ajiye ta dauki coke ta kora ta sauka kasa ta zauna tana jiran Sadiya tayi mata kitso, koda aka zo kitson ma wai ba za asa man kitso ba bata son kamshin man haka akayi kitson suna yi suna fada da sadiya har suka gama.
Yau rabonta da jawad sati uku kenan saboda tun dawowarta sau 1 yazo mata hira shiyasa ta shirya tafiya weekend acikin wannan satin, tana zaune tayi zugum tana tunanin abin yi saboda kwadon kanzo take son ci yau domin yanzu ta tsani awarar da ta zama abincinta da, tun ranar da tayi aman awarar taji ta fita daga cikin ranta,
"Pherty me zan dafa mana?" A'isha ta tambayeta lokacin da take kokarin fitar da rishon da zatayi girkin waje,
"A'isha wallahi kanzo nake son ci, nidai jawad ya hadani da lalura" takarasa maganar acikin zuciyarta,
"Kanzo?" Sadiya ta fada cikin mamaki,
"Yanzu a ina za asamu kanzo?
Indai ba son wahalar da kai ba kin san dai duk hostel dinnan ba za asamu kanzo ba" A'isha ta bata amsa,
Kallonsu tayi daya bayan daya kawai sai ganinta suka yi ta fara hawaye,
"Yi hakuri zamu samo miki, ai dole mu samowa dan baba kanzo" Sadiya ta fada tana dariya tareda tashi ta fita, itama A'isha fitar tayi suka tafi yawon neman kanzo duk kuwa da cewar sun san abune mai wahala samun kanzo acikin hostel.
Ita kam pherty suna fita ta shafa cikinta tana goge kwallar idonta, "yanzu jawad shi babu abinda ya dameshi yana can yana zamansa lfy ni kuma nan ya barni da laulayi" haka ta fada acikin ranta, tana nan zaune suka dawo basu samo kanzon ba nanfa taji hankalinta ya tashi wani kukan tafara kokarin yi amma shigowar Ummi Hambali yar department dinsu yasa ta hadiye kukan,
"Pherty ga wainar fulawa na kawo miki" ummin tafada tana mika mata wani flask karba tayi fuskarta dauke da murmushi,
"Nagode ummi kamar kuwa kin san yau babu abinda naci" da sauri ta dauko yaji ta fara ci ko sadiya da A'isha bata barwa ba sai da taji tayi dam sannan hankalinta ya dawo jikinta.
Harararta Sadiya tayi "malama ki kira mijinki ya kawo miki kanzo saboda kar kizo kina tashinmu cikin dare kina cewa ke kanzo kike so"
Dariya A'isha ta saka "wlhi kar kisa yau naki kwanan dakin nan"
Murmushi pherty tayi "idan kunyi hakuri ma gobe zan tafi gidana wurin mijina"
"Dakyau dan Allah idan kinje kar ki dawo sai kin samo kanzon" Sadiya ta mayar mata da amsa, murmushi kawai tayi ta dauki wayarta ta soma kiran mamanta suna gaisawa ta fara yi mata zancen kanzo take so akawo mata,
"Kanzo kuma pherty?"
"Eh mama dan Allah ki kawo min dama kinga fa baki taba zuwa gidana ba mama, dan Allah kizo" ta fada cikin shagwaba
"To shikenan bari mahaifinki yazo zan sanar masa idan ya yarda zanzo ranar asabar idan kuma bai yarda ba to zan taso hawwa kawarki ta kawo miki"
"Mama dan Allah Ku taho tare dan Allah"
"To shikenan phertyma sai ranar asabar din"
Kashe wayar tayi tana murna nan ta tsiri shirin tafiya gida.
Washe gari da yamma kuwa jawad yazo ya dauketa, sai kallonshi take cikin burgewa komanshi tsaf tsaf amma ita ya hadata da aiki bata da aiki sai tara yawu ta zubar, shi kam jawad bai ma san tana da cikin ba.
Suna zuwa gida ta fita daga motar taje ta zubar da yawun bakinta,
"Jawad murhun karfe da itace zaka siyo min kasa min acan baya dan bazan iya girki a gas ba" ta fada tana yatsina fuska, hannunta ya kama suka shiga cikin falo ya zaunar da ita akan cinyarsa, zumbur ta tashi saboda kamshin turarensa da ta shaka nan taji cikinta ya soma juyawa zuciyarta ta fara tashi.
Ummi A'isha🏻
[6/3, 7:27 AM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑
Na
UMMI A'ISHA
83
~~~ Zumbur ta tashi saboda kamshin turarensa da ta shaka nan taji cikinta ya soma juyawa zuciyarta tafara tashi, yawune ya cika mata baki da sauri ta shiga dakinta nan dinma babu dadi domin kamshin da dakin yake yi shima baiyi mata ba, toilet ta shiga ta zubar da yawun bakinta ta koma falo wurin jawad,
"Queen wai meke faruwa ne?" Ya tambayeta
"A inafa?" Itama ta tambayeshi
"To naji kince na siyo miki murhu, me zai hana ki rinka girkin a electric stove tunda kince baki son yin girki a gas"
Zama tayi nesa dashi ta yatsina fuska,
"Nifa gaba daya warin girkin ma da warin rishonne bana so har warin gas din duk bana so murhu nake son ka samo min da fire wood"
"Angama ranki ya dade" mikewa yayi ya fita dan siyo mata murhun, tashi itama tayi ta shiga dakinta tana tottoshe hanci nan ta tattara kayan da zata bukata ta koma daya dakin kuma cikin sa'a sai taji nan din babu kamshin da bata so din.
Kamar yadda tace haka jawad ya siyo mata murhu guda biyu da itace ya kawo mata, acan bayan kitchen dinta ta ajiye murhun ta kunna wuta ta dora abinci, tuwon shinkafa miyar wake da busasshen kifi tayi, lokacin data gama jawad yana kishingide a falo,gabansa ta kawo abincin ta jere tashiga dakinta taje tayi wanka ko mai bata shafa ba saboda shi kansa man tayar mata da zuciya yake, yar doguwar riga ta shan iska ta zira tafito falo inda jawad yake zaune yana cin abinci.