← Book details Martabata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 27

Sashe 21

Martabata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Hannunta ya kamo "Xarah kashe fankar nan har ac din sanyi nake ji"
Da sauri ta tashi taje ta karkashe ta dawo wurinsa, "shine kika rufe min bayan ban gama gani ba" ya fada idonshi a lumshe, hannunsa ta matsa,
"Nakira dr ansar yazo ya dubaka?"
Kai ya daga mata alamun ehh, cikin sauri ta tashi taje dakinsa ta dauko wayarsa ta fara kiran dr din amma wayar tasa a kashe,
"Wayarsa akashe dan Allah ka daure kasha maganin"
Kamar wani karamin yaro ya yamutse fuska "bana son magani wlhi"
Kusa dashi tazo ta zauna ta kamo hannunsa ta rike, "kayi hakuri kasha kaga ai baka da lfy sosai"
Idanuwansa ya lumshe,sumar kansa ta shafa "na dauko maka kasha?" Kai ya daga mata, tashi tayi taje ta dauko maganin ta kawo masa,
"To tashi kasha"
"Ki dauko min cock" kallonsa tayi"da cock zaka sha?"
"Uhm" yafada lokacin da yake kokarin tashi, cock din ta dauko masa ta ciro magungunan ta bashi ya karba yasha, yana gama shanyewa ya koma kan doguwar kujera ya mike sai bacci.

Ajiyar zuciya tayi ta kalleshi, "jawad case ace shan magani sai da dabara?" Kujerar da yake kwance ta karasa ta tsugunna agabansa gamida hada fuskarta da tashi, ta dade tana jujjuya fuskarta akan tasa sannan ta tashi taje kitchen ta dora musu abinci, jalop din zallar wake da kifi ta dafa.

Lokacin da ta fito ya farka, da sauri ta karasa gabansa "sannu"
Hannunta ya kamo ya tashi zaune "hada min ruwa nayi wanka zafi nakeji"
"To zo muje" hannunta ya rike yabita har cikin dakinsa ta shiga toilet ta hada masa ruwan ta fito,
"Kashiga kayi wankan"
Kai ya langabar "muje kiyi min" ido ta zaro
"Yi hakuri kayi kaji" shigewa cikin toilet din ya yi batare da yace komai ba.

Falo ta koma ta je ta shirya masa abinci ta zauna tana jiran fitowarsa, daga shi sai farin gajeren wando da farar t shirt mahadin wandon ya fito,
"Sannu na kawo maka abincin ko?" Zama yayi yana kallonta
"Kunna min ac,kadan zaki zubo min" tashi tayi taje ta kunna ta zubo masa faten waken a filet ta kawo masa, janta jikinsa yayi "kibani a baki queen"
Batayi musu ba ta fara bashi,hannunta ya kama "nakoshi bani ruwa nasha"
"Ayya jawad dan kara kadan kaji, dan kara pls" cigaba da bashi tayi har sai da ya cinye tas, tsakiyar falon ya koma ya kwanta akan carpet,
"Queen zo kiji" ya fada yana mika mata hannu,bata yi musu ba ta tashi ta koma kusa dashi ta zauna, janta yayi jikinsa ya kwantar da ita ya fara lalubarta, bata yi masa gardama ba balle tayi kokarin hanashi yau dai ta tayi abun kai wacce rana ya tabata bata yi masa masifa ba.

Yar guntuwar rigarta ya zame, ya kankameta ya fara wasanni ajikinta, idanuwanta kawai ta lumshe tana jin yanda yake bidirinsa a jikinta son ranshi, hannunsa ta rike,
"Kamanta abinda ka fada dazu?

Dazun nan ka gama cewa na rike abinda nake takama dashi"
Dan murmushi yayi wanda ya kawata fuskarsa "ai kawai fada nayi amma ba har zuciyata ba, tayaya zan iya fushi da ke?"
Bakinta ya tsotsa ya ja hancinta, "ni yanzu ma babu abinda zan iya yi saboda jikina ba lafiya" sai a lokacin taji hankalinta ya dan kwanta,jagulata ya fara yi ta kowanne bangare yana wasa da kirjinta wanda shine yafi komai daukar hankalinsa.

Sun jima acikin wannan yanayi kafin ya iya hakura ya kyaleta yana maida numfashi a hankali, rungumeta yayi tsam ajikinsa ya fara sinsina gashin kanta, tana kwance akan kirjinsa a haka bacci ya dauketa, amma shi bai yi baccinba sai ma cigaba da yayi da mammatsa jikinta har lokacin salla yayi.

Zameta yayi ya tashi ya shiga dakinsa dama jira take ya tashi dan haka yana tashi itama tayi gaggawar shigewa dakinta tasa key, toilet ta shiga tayi wanka ta fito tayi salla bayan ta idar ne ta fara kokarin shiryawa, kwalliya ta tsara a fuskarta jikinta kuma ya dauki daddadan kamshi mai tausasa zuciya, wata pink din riga tasa mai zanen lips ajiki, an rubuta KISS ME da manyan harrufa, rigar roba ce sannan bata da nauyi yar shafal take yar karama da ita, bakin wando jeans tasaka iya gwiwarta ta gyara gashin kanta ta daureshi da ribom pink colour.

A hankali ta bude kofar dakin nata ta dan leka, jawad ta gani kwance akan kujera yana waya, fitowa tayi ta shige kitchen daga tsaye ta tsaya ta zuba faten waken dan kadan taci ta dauki juice ta fita,
"Zo kiji pherty na" ya fada yana yi mata murmushi,kusa da kujerar da yake taje ta zauna,
"Yaya aadil sun dawo dazu, yaushe za muje muyi musu sannu da zuwa?"
Dan murmushi tayi ta kurbi lemon dake hannunta,
"Sai ka samu saukin jikinka sai muje"
Gaban rigarta ya kalla, a hankali ya tashi ya matsa kusa da ita,
"Ya akayi?" Tafada tana kallonsa,
"Umarni zan cika na abinda kika nema, gashi nan rubuce jikin rigarki" ya fada yana nuna mata da dan yatsansa, ja da baya tayi
"Nidai gaskiya ba zaka bata min kwalliyata ba, tashi tayi zata gudu yayi saurin riketa ya jawota, kokawa suka fara,akan kujerar ya shimfidar da ita ya matseta,
"Gaskiya jawad nidai ka bari kar ka bata min kwalliya ta" ta fada a shagwabance,
"Idan na bata miki zan sake miki wata kinji my queen"
"A'a nidai ban yarda ba gaskiya" bai barta ta karasa ba ya hade bakinsa da nata, lips dinta na sama ya kama,
"In ciza?" Ya rada mata a kunnenta,
"Ka ciza mana nima in rama" ta fada tana lumshe idonta,dan cizar lip dinta yayi, nan suka fara kokawa ita a dole sai ta rama, kanshi ya cusa a wuyanta, gefen kunnenshi ta samu ta ciza,
"Ahh sai na rama ai ba haka nayi miki ba"
"Kaima da zafi kayi min" a tsakiyar kirjinta ya sake cizonta, yana dagowa ta rike lip dinsa na kasa da hakoranta, kwankwasa kofar da aka fara yine ya katse musu wasannin da suke yi cikin nishadi,dagata yayi yaje ya bude kofar, Sadiya da A'isha ne suka shigo, tana nan kwance inda ya barta ganinsu ya sata daka tsalle taje ta rungumesu,
"Nayi missing dinku yan dakinmu, sannunku da zuwa" akan kujera suka zauna ta shige tsakiyarsu,
"Sai yanzu zaku zo maimakon kuzo tun safe mu wuni"
"We are sorry amarya" suka fada atare suna dariya,
"Yaya jawad ina wuni?

Ya jiki?" Suka fada suna kallon jawad
"Lfy lau jiki yayi sauki" ya fada cikin hausarsa ta yan koyo,
"Kun ganshi nan har yau ya kasa iya hausa, ya iya kowanne yare hausa ne bai iyaba dan rashin kara" pherty ta fada daidai lokacin da ta tashi ta nufi kitchen,
"To ai kece baki koya min ba" ya fada tareda tashi yabi bayanta, a kitchen ya tarar da ita tana yanyanka lemo dasu abarba da sauran fruit akan filet, ta bayanta ya turata ya matseta ajikin lokokin dake jere cikin kitchen din,
"Wash jawad marata, dan Allah kabari"
Matsawa yayi,"kawayenki sunzo shiyasa zaki kyaleni ko?

Wannan ranar ta yau ranace mai mutukar muhimmanci agareni, ranar da pherty ta barni ta sakar min fuska, ta kyaleni nayi wasa da ita"
Murmushi tayi ta dauki katon farantin data zuzzuba kayan zata fita, jawo rigarta yayi "bakiyi comment ba, let me go and write this moment in my diary"
Sakinta yayi ta fita yabi bayanta ya wuce dakinsa, Sadiya da A'isha suka hada ido suka kwashe da dariya,
"A'a bangane bafa, ya zaku tasani gaba kuna dariya?

Yanzu zanyi muku rashin mutunci"
"Mu bake muke yiwa dariya ba" A'isha ta fada tana wata dariyar,
"Ai dama har angane yan dakinmu shiyasa mutane bazasa son zuwa saboda duk wanda yazo sai kunyi masa dariya keda Sadiya"
"Yoh mutum da bakinsa, ai dole muyi dariya" inji Sadiya
"Sai kuyi tayi ai" inji pherty
Kayan da ta hado musu ta gabar musu nan suka shiga hira suna motsa baki sai daf da mangaruba sannan suka tafi.

Dakin jawad ta shiga yana kwance akan gadonshi, a gefenshi ta kwanta, "jawad kayi salla?"
Kai ya daga mata, "to me zaka ci?"
"Fura da nono zansha"
Tashi tayi taje ta damo masa a kofi ta kawo masa, ta koma dakinta ta shiga wanka ta fito tasa sleeping dress kamar tayi kwanciyarta a dakinta sai kuma ta tuna da batun magen rannan, zuruf ta tashi ta nufi dakin jawad, tana shiga taganshi ya fito daga wanka, kan gadon taje ta haye taja blanket ta rufe jikinta ta rufe idanuwanta.

Ummi A'isha🏻
[5/22, 8:28 AM] Ummi A'isha🏻: [5/21, 9:06 PM] Ummi A'isha🏻: 👑👑MARTABA TA👑👑
Na
UMMI A'ISHA
76-78
~~~ Kwanciya tayi ta juya bayanta tana jiran hawowarsa gadon, sai da ya feshe jikinsa da turarruka masu dadin kamshi sannan yasa kayan baccinsa ya kashe wuta ya hau kan gadon, jikinsa ya matso da ita ya rungumeta yana shafa gashin kanta nan da nan bacci ya dauketa, shi dai sai da ya kwashe lokaci mai tsawo kafin yayi baccin.
Chapter 21 · 0% Book details