Sashe 14
Martabata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Saboda kina son kasheni?"
Kallonsa tayi ya dan rame kadan kamar wani marar lafiya
"Kaine marar imani marar tausayi jawad, kaine kake shirin kisan kai sai kuma Allah ya juya maka al'amarinka da mummunan kudurinka kanka, na dade da fada maka bana sonka yanzu na tsaneka, ni bakai nake so ba yayanka nake so kuma shi zan aura, da shi zan rayu"
Tsugunnawa yayi ya dafe kirjinsa, kanta ta dauke amma koda ta jiyo sai taga jini yana fita daga bakinsa, da sauri ta kalleshi amma ba tayi magana ba, da kyar ya mike bakinsa duk jini ya kalleta
"Nagode pherty, tabbas kinyi min sakayya kuma nagani sannan nagode, zan tafi da sonki kuma zan mutu dashi, ina muku fatan alkairi keda mijinki masoyinki sannan Allah ya baku zuri'a dayyaba" yana kaiwa nan ya juya yana dingisawa idonsa cikeda kwalla bakinsa duk jini ya shiga motarsa, sai da yayi kamar minti biyar yana zaune yana kuka sannan ya iya fara tuka motar yana tafe yana aman jini yana kuka, ita kanta phertyn ta dade a tsaye kafin ta shiga gida tana zuwa daki kuma ta zauna ta fara kuka wanda ita kanta bata san ko na menene ba, matsowa kawayen nata suka yi suka fara tambayarta meya faru amma bata iya basu amsa ba.
******
Allah ne kadai yakai jawad gida lfy domin yayi mutukar galabaita wani irin harbawa zuciyarsa take yi masa kamar zata faso kirjinsa ta fito waje gashi aman jinin da yake sai karuwa yake, yana shiga gida yayi packing ya fito yana dafe da kirjinsa, tafiya kadan kuma ya fara wani irin tari mai sarke kirji nan ya fara aman jini sosai, ahaka ya mike jiri yana daukarsa ya nufi side dinsa, sharafff ya fadi akasa sumamme daidai lokacin maigadi ya nufo wurinsa yana ganinsa kwance cikin jini ya nufi part din Ummi da gudu "hajiya, hajiya fito jawad ba lafiya" haka mai gadin ya fada daidai lokacin da ya shiga falon ummin, zuruf ta mike
"Yana ina?"
"Yana waje"
Dagudu Ummi ta fita ta nufi tsakar gidan, tana zuwa ta ganshi kwance bakinsa duk jini gashi ko alamun numfashi babu a tattare dashi, salati ta fara daidai lokacin motar dad dinsu ta shigo gidan, da sauri ya fito yana tambayar meke faruwa ganin jawad acikin wannan hali yasa yabawa driver da maigadi umarni su saka jawad a mota, dagudu Ummi taje ta dauko mayafinta ta shiga motar suka nufi asibiti.
Wani private hospital suka kaishi, nan likitoci suka nufi wani daki dashi, kuka Ummi kawai takeyi dad yana bata hakuri.
Kimanin awanni uku doctors din suka shafe suna kokarin ceto ran jawad amma abun yaci tura har lokacin bai farfado ba sai daf da sallar magrib sannan ya fara motsi nan kuma yafara tari yana aman jini, dakin Ummi ta fada ganin halin da yake ciki yasata sake fashewa da kuka.
Wani babban doctor ne ya shigo hannunsa rikeda fayil ja, "ba kuka za kuyi ba, addu'a za kuyi masa, agaskiya abun nasa yayi worst, yana dauke da ciwon hawan jini, jininsa ya hau sosai irin hawan da ba aso, sannan kuma a halin yanzu yana fama da ciwon zuciya"
Wani kuka Ummi ta fasa mai ban tausayi tana fadin "jawad wacce damuwa kasa aranka haka?
Haba jawad?
Tashi dad yayi yabi bayan likitan zuwa office dinsa bayan sun zauna ne likitan ya fara yi masa bayani
"Am Alhaji yaron nan naka yana cikin wani hali gaskiya, yanzu babbar matsalar itace idan yatashi farkawa kila zai tashi da ciwon shanyewar rabin jiki saboda irin wannan faduwar dama itace ke haddasa wannan matsalar, amma za muyi iya bakin kokarinmu sai dai idan hakan bai samu ba sai a fitar dashi kasar waje"
Wani gumine yaketa tsattsafowa dad din baice komai ba ya tashi ya fita ya koma dakin da jawad yake.
Kwanansu uku a asibitin amma jawad ko motsi bai yi ba yana nan kwance kamar gawa, aranar aadil yazo garin koda yaje gidan bai samu kowa ba sai maigadin ne yayi masa bayani, wayar dad ya fara kira ya tambayeshi sunan asibitin yana fada masa yakarawa motarsa wuta ya isa asibitin, har a lokacin jawad bai motsa kai idan ka ganshi ba zaka taba tsammanin zai kara awa daya a raye ba saboda gaba dayansa acikin wasu karafa yake gashi ansaka masa abun numfashi wato oxygen tube, gefe kuma ana yi masa karin ruwa, Ummi na zaune fuskarta ta gama kumburewa saboda kuka, tayi jawur abunku da farar mace,
Ahankali ya karasa kusa da Ummi, "sannu Ummi, ya mai jiki?"
Cikin hawaye Ummi ta juyo tana ganin aadil sai ta sake fashewa da kuka mai ban tausayi
Riketa aadil yaje yayi nan shima ya fara hawayen, doctor dinne ya bude kofa ya shigo ya kallesu "kuyi hakuri kudaina kukan nan domin patient dinku baya son hayaniya asali ma isolating din masu irin lalurar su ake yi asauran hospitals nan dinma saboda kune shiyasa muka barku kuke tare dashi" kallon dad yayi
"Alhaji muna da bukatar jini domin akara masa"
Mikewa aadil yayi fuskarsa cikeda kwalla yace "muje a dibi nawa a kara masa"
Fita sukayi da doctor din suka nufi lab anan aadil din yake tambayarsa me yake damun dan uwan nasa, hawan jini da ciwon zuciya itace amsar da doctor din ya bashi, nan hankalin aadil ya tashi domin yasan yana dab da rasa dan uwan nasa gashi su biyu kacal iyayensu suka haifa, haka aka dibi jinin nasa leda biyu aka tafi domin karawa jawad, ba komai ne yafi daga masa hankali ba illa cewar da akayi kila jawad zai kamu da ciwon shanyewar barin jiki, dakin da jawad din yake ya koma ya samu Ummi
"Ummi wai duk mai ya haddasa masa wannan lalurar?"
"Wlhi aadil nima ban sani ba saboda jawad yanzu ya sauya hali dama can kasan shi ba mai yawan magana bane baya son hayaniya tun kuna yara kafishi magana shi sai ya wuni baiyi magana da kowa ba to yanzun kuma abinda ya tsira sai ya wuni a daki bai fito ba, nidai kawai ina zaune sai ga watchman wai nazo ga jawad can yafadi yanata aman jini, yanzu gashi doctor yace ciwon zuciya da hawan jini ne ke damunsa, ban san abunda yake damunsa ba har ya kamu da wannan lalurar" ta karasa maganar cikin kuka tareda rungume dan nata aadil
"Kidaina kuka Ummi insha Allahu zai samu lafiya, Ummi gara ke kinada wani dan kuma kina da yan uwa nikuwa fa?
Iya jawad ne dan uwana banida wani dan uwan sai shi idan na rasashi shikenan narasa wani bangare na rayuwata" aadil ya fada yana kuka hawaye suna bin kumatunsa
"To yanzu meye amfanin wannan kukan, haba aadil kamar ba namiji ba?" Dad ya fada yana kallonsu duk kuwa da cewar shima dauriya kawai yake yi.
Sai wurin karfe 9 na dare sannan aadil yaje gida yayi wanka anan yake sanar da Salima abunda yake faruwa, komawa asibitin yayi, daga Ummi har dad duk tausayinsa suke ji saboda sun san akwai soyayya mai tsanani tsakaninsa da dan uwansa, ko abinci ya kasa ci.
Kwanansu biyar acikin asibitin sannan jawad ya fara bude idonsa amma baya gane komai ga wata kumbura da fuskarsa tayi sai kuma ya fara tari mai wahala nan jini ya fara fita daga bakinsa da sauri aadil ya karasa gaban gadon ya rike hannunsa "sannu jawad"
Ko jinsa jawad bayayi, nan Ummi ta fara kuka sai janyeta dad yayi ya fitar da ita daga dakin, doctor ne ya shigo ya fara wasu rubuce rubuce ajikin fayil sannan ya yiwa jawad wata allura, nan yaja hannun aadil yana cewa yafi dacewa da adauki jawad akaishi kasar chairo zai fi samun lafiya fiyeda nan.
Wajensu Ummi aadil ya koma yayi musu bayani yace yanzu zaije yayi musu cuku cukun visa su hudun
"A'a aadil ban da kai, kaga yau kai saura 5 daurin aurenka, kayi mana mu uku kawai dani da mahaifiyar ka dashi jawad din"
"To dad" ya fada ba dan yaso ba, kallon Salima yayi amma baiyi magana ba ya juya ya fita.
Cikin kankanin lokaci aka samu visa nan suka tattara duk wani abu da zasu bukata aadil ya kaisu airport suka nufi kasar chairo, daga nan kumo ya wuce gidansu pherty.
Lokacin da ta fito ta ganshi sai taji gabanta ya fadi "yayana baka da lafiya ne?
Naga ka rame?"
"Pherty na jawad ne bashida lafiya, yanzun nan ma aka tafi chairo dashi, aman jini yake tayi"
"Allah yabashi lafiya" ta fada kamar zata yi kuka.
"Amin, Abba yana nan?"
"Eh" tafada a hankali
"To muje naganshi"
Rakiya tayi masa wurin abban ta fita ta basu wuri, ya dade awurin Abba sannan ya fito, ita da A'isha da Sadiya da hawy suka fito wurinsa
"Yaya aadil ango" suka fada su duka
Dan murmushi yayi
"Bakuda bukatar komai ko?"
"Muna son kudi wanda za ayiwa amarya gyaran jiki da kunshi" inji Sadiya da hawy
"Nawane?"
"20 thousand"
"To bari na bakubaku 50 thousand saboda ina son pherty na tayi kyau"
Motarsa yaje ya dauko kudin ya basu yayi musu sallama ya tafi ba tareda sun sake wata magana da pherty ba.
Kallonsa tayi ya dan rame kadan kamar wani marar lafiya
"Kaine marar imani marar tausayi jawad, kaine kake shirin kisan kai sai kuma Allah ya juya maka al'amarinka da mummunan kudurinka kanka, na dade da fada maka bana sonka yanzu na tsaneka, ni bakai nake so ba yayanka nake so kuma shi zan aura, da shi zan rayu"
Tsugunnawa yayi ya dafe kirjinsa, kanta ta dauke amma koda ta jiyo sai taga jini yana fita daga bakinsa, da sauri ta kalleshi amma ba tayi magana ba, da kyar ya mike bakinsa duk jini ya kalleta
"Nagode pherty, tabbas kinyi min sakayya kuma nagani sannan nagode, zan tafi da sonki kuma zan mutu dashi, ina muku fatan alkairi keda mijinki masoyinki sannan Allah ya baku zuri'a dayyaba" yana kaiwa nan ya juya yana dingisawa idonsa cikeda kwalla bakinsa duk jini ya shiga motarsa, sai da yayi kamar minti biyar yana zaune yana kuka sannan ya iya fara tuka motar yana tafe yana aman jini yana kuka, ita kanta phertyn ta dade a tsaye kafin ta shiga gida tana zuwa daki kuma ta zauna ta fara kuka wanda ita kanta bata san ko na menene ba, matsowa kawayen nata suka yi suka fara tambayarta meya faru amma bata iya basu amsa ba.
******
Allah ne kadai yakai jawad gida lfy domin yayi mutukar galabaita wani irin harbawa zuciyarsa take yi masa kamar zata faso kirjinsa ta fito waje gashi aman jinin da yake sai karuwa yake, yana shiga gida yayi packing ya fito yana dafe da kirjinsa, tafiya kadan kuma ya fara wani irin tari mai sarke kirji nan ya fara aman jini sosai, ahaka ya mike jiri yana daukarsa ya nufi side dinsa, sharafff ya fadi akasa sumamme daidai lokacin maigadi ya nufo wurinsa yana ganinsa kwance cikin jini ya nufi part din Ummi da gudu "hajiya, hajiya fito jawad ba lafiya" haka mai gadin ya fada daidai lokacin da ya shiga falon ummin, zuruf ta mike
"Yana ina?"
"Yana waje"
Dagudu Ummi ta fita ta nufi tsakar gidan, tana zuwa ta ganshi kwance bakinsa duk jini gashi ko alamun numfashi babu a tattare dashi, salati ta fara daidai lokacin motar dad dinsu ta shigo gidan, da sauri ya fito yana tambayar meke faruwa ganin jawad acikin wannan hali yasa yabawa driver da maigadi umarni su saka jawad a mota, dagudu Ummi taje ta dauko mayafinta ta shiga motar suka nufi asibiti.
Wani private hospital suka kaishi, nan likitoci suka nufi wani daki dashi, kuka Ummi kawai takeyi dad yana bata hakuri.
Kimanin awanni uku doctors din suka shafe suna kokarin ceto ran jawad amma abun yaci tura har lokacin bai farfado ba sai daf da sallar magrib sannan ya fara motsi nan kuma yafara tari yana aman jini, dakin Ummi ta fada ganin halin da yake ciki yasata sake fashewa da kuka.
Wani babban doctor ne ya shigo hannunsa rikeda fayil ja, "ba kuka za kuyi ba, addu'a za kuyi masa, agaskiya abun nasa yayi worst, yana dauke da ciwon hawan jini, jininsa ya hau sosai irin hawan da ba aso, sannan kuma a halin yanzu yana fama da ciwon zuciya"
Wani kuka Ummi ta fasa mai ban tausayi tana fadin "jawad wacce damuwa kasa aranka haka?
Haba jawad?
Tashi dad yayi yabi bayan likitan zuwa office dinsa bayan sun zauna ne likitan ya fara yi masa bayani
"Am Alhaji yaron nan naka yana cikin wani hali gaskiya, yanzu babbar matsalar itace idan yatashi farkawa kila zai tashi da ciwon shanyewar rabin jiki saboda irin wannan faduwar dama itace ke haddasa wannan matsalar, amma za muyi iya bakin kokarinmu sai dai idan hakan bai samu ba sai a fitar dashi kasar waje"
Wani gumine yaketa tsattsafowa dad din baice komai ba ya tashi ya fita ya koma dakin da jawad yake.
Kwanansu uku a asibitin amma jawad ko motsi bai yi ba yana nan kwance kamar gawa, aranar aadil yazo garin koda yaje gidan bai samu kowa ba sai maigadin ne yayi masa bayani, wayar dad ya fara kira ya tambayeshi sunan asibitin yana fada masa yakarawa motarsa wuta ya isa asibitin, har a lokacin jawad bai motsa kai idan ka ganshi ba zaka taba tsammanin zai kara awa daya a raye ba saboda gaba dayansa acikin wasu karafa yake gashi ansaka masa abun numfashi wato oxygen tube, gefe kuma ana yi masa karin ruwa, Ummi na zaune fuskarta ta gama kumburewa saboda kuka, tayi jawur abunku da farar mace,
Ahankali ya karasa kusa da Ummi, "sannu Ummi, ya mai jiki?"
Cikin hawaye Ummi ta juyo tana ganin aadil sai ta sake fashewa da kuka mai ban tausayi
Riketa aadil yaje yayi nan shima ya fara hawayen, doctor dinne ya bude kofa ya shigo ya kallesu "kuyi hakuri kudaina kukan nan domin patient dinku baya son hayaniya asali ma isolating din masu irin lalurar su ake yi asauran hospitals nan dinma saboda kune shiyasa muka barku kuke tare dashi" kallon dad yayi
"Alhaji muna da bukatar jini domin akara masa"
Mikewa aadil yayi fuskarsa cikeda kwalla yace "muje a dibi nawa a kara masa"
Fita sukayi da doctor din suka nufi lab anan aadil din yake tambayarsa me yake damun dan uwan nasa, hawan jini da ciwon zuciya itace amsar da doctor din ya bashi, nan hankalin aadil ya tashi domin yasan yana dab da rasa dan uwan nasa gashi su biyu kacal iyayensu suka haifa, haka aka dibi jinin nasa leda biyu aka tafi domin karawa jawad, ba komai ne yafi daga masa hankali ba illa cewar da akayi kila jawad zai kamu da ciwon shanyewar barin jiki, dakin da jawad din yake ya koma ya samu Ummi
"Ummi wai duk mai ya haddasa masa wannan lalurar?"
"Wlhi aadil nima ban sani ba saboda jawad yanzu ya sauya hali dama can kasan shi ba mai yawan magana bane baya son hayaniya tun kuna yara kafishi magana shi sai ya wuni baiyi magana da kowa ba to yanzun kuma abinda ya tsira sai ya wuni a daki bai fito ba, nidai kawai ina zaune sai ga watchman wai nazo ga jawad can yafadi yanata aman jini, yanzu gashi doctor yace ciwon zuciya da hawan jini ne ke damunsa, ban san abunda yake damunsa ba har ya kamu da wannan lalurar" ta karasa maganar cikin kuka tareda rungume dan nata aadil
"Kidaina kuka Ummi insha Allahu zai samu lafiya, Ummi gara ke kinada wani dan kuma kina da yan uwa nikuwa fa?
Iya jawad ne dan uwana banida wani dan uwan sai shi idan na rasashi shikenan narasa wani bangare na rayuwata" aadil ya fada yana kuka hawaye suna bin kumatunsa
"To yanzu meye amfanin wannan kukan, haba aadil kamar ba namiji ba?" Dad ya fada yana kallonsu duk kuwa da cewar shima dauriya kawai yake yi.
Sai wurin karfe 9 na dare sannan aadil yaje gida yayi wanka anan yake sanar da Salima abunda yake faruwa, komawa asibitin yayi, daga Ummi har dad duk tausayinsa suke ji saboda sun san akwai soyayya mai tsanani tsakaninsa da dan uwansa, ko abinci ya kasa ci.
Kwanansu biyar acikin asibitin sannan jawad ya fara bude idonsa amma baya gane komai ga wata kumbura da fuskarsa tayi sai kuma ya fara tari mai wahala nan jini ya fara fita daga bakinsa da sauri aadil ya karasa gaban gadon ya rike hannunsa "sannu jawad"
Ko jinsa jawad bayayi, nan Ummi ta fara kuka sai janyeta dad yayi ya fitar da ita daga dakin, doctor ne ya shigo ya fara wasu rubuce rubuce ajikin fayil sannan ya yiwa jawad wata allura, nan yaja hannun aadil yana cewa yafi dacewa da adauki jawad akaishi kasar chairo zai fi samun lafiya fiyeda nan.
Wajensu Ummi aadil ya koma yayi musu bayani yace yanzu zaije yayi musu cuku cukun visa su hudun
"A'a aadil ban da kai, kaga yau kai saura 5 daurin aurenka, kayi mana mu uku kawai dani da mahaifiyar ka dashi jawad din"
"To dad" ya fada ba dan yaso ba, kallon Salima yayi amma baiyi magana ba ya juya ya fita.
Cikin kankanin lokaci aka samu visa nan suka tattara duk wani abu da zasu bukata aadil ya kaisu airport suka nufi kasar chairo, daga nan kumo ya wuce gidansu pherty.
Lokacin da ta fito ta ganshi sai taji gabanta ya fadi "yayana baka da lafiya ne?
Naga ka rame?"
"Pherty na jawad ne bashida lafiya, yanzun nan ma aka tafi chairo dashi, aman jini yake tayi"
"Allah yabashi lafiya" ta fada kamar zata yi kuka.
"Amin, Abba yana nan?"
"Eh" tafada a hankali
"To muje naganshi"
Rakiya tayi masa wurin abban ta fita ta basu wuri, ya dade awurin Abba sannan ya fito, ita da A'isha da Sadiya da hawy suka fito wurinsa
"Yaya aadil ango" suka fada su duka
Dan murmushi yayi
"Bakuda bukatar komai ko?"
"Muna son kudi wanda za ayiwa amarya gyaran jiki da kunshi" inji Sadiya da hawy
"Nawane?"
"20 thousand"
"To bari na bakubaku 50 thousand saboda ina son pherty na tayi kyau"
Motarsa yaje ya dauko kudin ya basu yayi musu sallama ya tafi ba tareda sun sake wata magana da pherty ba.